Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

MAIRO Complete Hausa Novel Document by MAIRO


MAIRO

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 54573



MAIRO

Reading Time: 4 Hours

Added On: 23, Jun 2024

Author: Khadeeja Candy ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 292.56 kb

File Type: txt

Views: 1383+

Download: 1666+

Last download: 4 days ago

Description/Story: *♡...  MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*1*

"Na rantse da Allah yau sai an biyani ni babu ruwana"
rik'e take da kunkuru tana marmaɗen ido da murguɗa baki jikinta sai rawa yake wai ita ga matsifaffeya.
yaron dake gabanta ya risina har k'asa yana bata hak'uri
"dan Allah Mairo ki yafe min wlh ba zan kara ba ni naga kinje wani gurin ne shiyasa na cika miki ban san ba kyaso ba"
sai a lokacin ta kalleshi cikin matsifa tace "saka nayi cewa nayi na cika min kai mai hegen salo yau ko saika busar dashi ko na maka hegen duka"

wata dattijuwa take wanki gefen kogin ta kalleta tace "ke Mairo wai miyasa baki jin magana ne yanzu miye laifin yaron nan dan ya cika miki tulu?"
harara ta watsa mata ta murguda mata baki "ke kuma tsohuwa ina ruwanki dake nake yi ne da zaki samun baki ko sashi nayi da zai cika min tulu wannan ai rainine"
"ke fa baki da kirki Mairo daga magan zaki wani taso min kamar wata warinki"
"mtsssss yau daman kin san ba warinki nake ba kika samin baki a magana dan neman tsokana"

daidai nan Almu ya iso da jakinsa da jalkunan ɗinba ruwa.
yana kallon Mairo yasan matsifa ce take ganin yadda take marmaɗen ido tana rawar jiki
murmushi kawai yayi ya gaida dattijuwar

"inna ina kwana?"

"lafiya kalau Almu an tashi lafiya?"

"Alhamdulillah inna"

kallon mairo yayi "ke lafiyarki kike wannan harare2?"

banza ta masa ta cigaba da karkada jiki.
inna ta taɓe baki

"ai haka take indai rashin kunya ne ta iya ga yar banzar matsifa"

juyowa mairo tayi kanta "wai ke ina ruwanki dani kinga ban hega saggarki ba ki fita tawa bana son shinshigi"

da marmaɗe2 ta ksrasa maganar tana murguda mata baki.
      mari Almu ya kai mata ya fizgota ya jefar
"ke wai miyasa rashin kunya yayi miki yawa kamar inna zaki tsaya kina faɗawa irin wannan maganar sa'arki ce?"
wani ihu mairo ta saki ta shiga murk'ususu cikin kasa tana jan gashin kanta
"wayyo na shiga uku ya kashe ni wayyo Allah ya kare ni wayyo gwaggo"

tsoro Almu yaji ganin yadda take ihu duk'awa yayi ya rikota "tashi mu gani?"
wani mugun cizo ta kai masa a hannu saida ya saki kara ya saketa da sauri.
inna ta rike baki "oh ni hajjo wannan wace irin masifaffiyar yarinya ce haka?"
Almu dai shiru yayi yana murzar hannun dan ba karamin cizo tayi masa ba,
ya dade a haka kamin ya nufi kogin ya shiga cika jalkunansa.
       ihunta ta cigaba dayi tana murje2 daga Almu har inna babu wadda ya sake bi ta kanta.
Almu na daf da cika kayansa halilu ya iso gurin yana ganin mairo yayi saurin ta data "ke lafiya miya faru?"
langaɓe masa tayi ta cigaba da kukan
nan ya kalli inna da Almu ya shiga tambayar su ba'asi "wai miya sameta ne haka?"
inna tace "babu kawai rashin kunya tayi min Almu ya ɗan zungureta shikenan fa ta faɗi ta shiga koke2"
cikin kuka Mairo ta ɗago "wlh karya suke itace ta fasa kuka tace masa na zageta shi kuma ya ɗaga ni sama ya jefar na kare"
tana kaiwa nan ta saki wata kara kamar wadda aka sokawa wuka.
rik'e baki inna tayi jin irin karyar da Mairo ta zagga
Halilu ya kalli Almu "haba Almu ya zaka mata haka kamar wata warinka ko namiji"
Almu yayi murmushi "haba dai Halilu sai kace bakasan halin Mairo ba wlh karya take"
Halilu yace  "wai minene mafarin wannan masifa?"
inna tace "ɗiban ruwa tazo fa saita eje tulun ta tafi yawonta shine haruna ya dauka ya cika mata shine data dawo tace sai ya biyata shine ya zubar da ruwan daya zuba kuma duk da haka tace wai saiya busar tulun yadda yake shine ya shiga bata hak'uri taki hak'ura wai ita saita dake sai natibmata magana shine fa ta shiga fada min magagganu har Almu saida tayi masa rashin kunyar"
Halilu yace "daman shine kawai take yiwa wannan kuka?"
"shine kawai babu wani abun da akayi mata"
cewar inna.
kai halilu ya kaɗa ya Nufi ecen dogon yaro ya k'allo ya juyo gurin mairo cikin zafin nama ya watsa mata ita,
mairo najin saukar bulala ta tashi da gudu ta nufi gida tana uhu.

***   ***   ***

da ihu ta isa gida tana murxa gurin da Halilu ya buga mata bulalar.
da sauri gwaggo ta tare ta "lafiya Mairo miya sameki?"
rumgumeta tayi "wayyo gwaggo zasu kasheni gwaggo basa sona sun min taro suna ta duka na"
gwaggo ta dagota "su waye Mairo faɗa min uban wa ya taba ki cikin garin nan?"
cikin kuka ta shiga yima gwaggo k'arya data saba "tsohuwar gidansu hajara ce tace wa Almu wai na zageta shine shi kuma ya daga ni sama ya jefar gwaggo ya k'arya ni na bani mutuwa zanyi"
da sauri gwaggo ta zaunar da ita ta shiga duba ta tana matsifa "wannan wace irin k 'etace haka wlh duk suka karyaki sai munyi shari'ah dasu mugayen mutane azzalumai"
gwaggo na taɓa mata k'afa ta saki wani mahaukacin ihu "wayyo na shiga uku gwaggo nan gurin Halilu ya buga min ecce"
gwaggo tayo waje da ido "ecce kuma yaushe mi kika masa?"
"ban masa komai ba daga zuwansa suka fada masa k'arya shine ya dauko k'aton ecce ya buga min gwaggo basu sona na shiga uku"
tashi gwaggo tayi ta shiga ɗaki ta ɗauko mayafinta ta nufi kofa.

  
        '''
NOTE'''
*_Assalamu Alaikum ina bawa fans ɗina hak'uri bisa ga rashin ganin cigaban novel ɗina mai suna LAMARIN DUNIYA na k'are novel ɗin gaba ɗaya kamin na fara posting sai phone ɗina ya samu matsala kuma wadda nayi publishing a blog ɗina blog ɗin ya samu matsa. ta dalilin matsalar da phone ɗina ya samu amman ana kan gyara blog ɗin da zarar an kare zanyi muku C & P Insha Allah ko kuma na baku blog address ku karanta bayan haka dan Allah ina rokon duk mai novels ɗina ko wane iri ya turo min ta wannan number_*
+2348036126660
*_taku har kullum Khadeeja Candy_*

© *Khadeeja Candy*
[11/5, 9:37 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*2*

gwaggo na k'ok'arin fita halilu na k'ok'arin  shigowa sukaci karo nan taci kwalarsa ta k'asara shigowa dashi tana masifa "ashe baka da hankali halilu dan kana magu zaka sa ecce ka bugawa Mairo bancin bugun da Almu yayi mata wai mi ta tare maka ne?"
kai ya girgiza "haba gwaggo wai miyasa duk tazo tayi miki k'arya saiki yarda ya za'aiyi na buga mata ecce fisabilillahi?"
"ai halinka na sani ba sonta kake ba zaka iya mata komai"
kallon mairo yayi da tayi shiru tana kallonsu kamar wata munafuka yace "ke dukanki nayi?"
kai ta daga ta turo baki tana matsar kwallah.
"eh gurin da Almu ya karyani ka buga min ecce"
gwaggo ta kara ciyo kwalarsa "mugu yanzu abunda kake ya kamata kenan a gaban idonka ka bari Almu yayi mata wannan illar wai miyasa baka son yarinyar nan ne halilu?"
"ohhh gwaggo haba haba wane irin illa Almu zaiyi mata rashin kunya fa tayiwa tsohuwar mutane shine ya dan zingureta fa"
gwaggo tace "tho ina ruwansa ya zingureta haihuwarta yayi kuma karya kake karyata yayi"
"haba gwaggo yarinyar da aka karya zata iya kawo kanta gida har ta iya faɗa miki an karya ta ai saidai a kawo miki ita"
saki kwalarsa gwaggo tayi ta nufi Mairo ta shiga duba k'afar.
aiko nan mairo ta k'ara marairaicewa tana "wayyoh k'afata" gwaggo ta duba bata ga alamun kariya a k'afarta ba ko alamun jimuwa babu barre karaya ta data gwaggo tayi tsaye "tashi kiyi tafiya na gani"
nan ta lak'e kafar "wayyo bazan iya takata ba gwaggo ta riga ta karye"
cikin dabara halilu ya cire takalminsa ya jefa mata iya karfinsa aiko da gudu ta faɗa ɗaki tana ihu.
matsowa yayi kusa da gwaggo ya ɗauki takamin yana faɗin "yanzu wadda aka karya zata iya wannan gudun?"

shiru gwaggo tayi halilu yace "gwaggo wata rana saita saki kunya matukar duk abunda tazo ta faɗa miki kina yarda dashi tho ko zaki ɓata da kowa"
tsaki gwaggo taja "mtsss tho sai mi dan na ɓata da kowa akanta so kake na zuba ido ina kallon ana cin amanarta? ko kai ka taɓa ta saina taɓa ka bare wani can"
halilu bai kara cewa komai ba banda kan da ya girgiza ya fice ya barta tana masifarta.
saida Mairo taji fitarsa sannan ta fito tana kukan munafurci.
nan gwaggo tayi cikinta ta masifa "Allah mairo in kina zuwa kina min karya saina ɓata miki rai kuma na ɓata dake na fita harkarki"
    kwantowa tayi jikinta tana kukan shgwaɓa "tho ai ba karya nake ba Almu ya dakeni kuma Halilu ya zaggamin bulala"
tureta gwaggo tayi "amman ai cemin kikayi shiya buga miki ecce Almu kuma ya karyaki"
turo baki tayi
"eh karya nake amman dai sun dakeni dukansu"
"tho miyasa kika min karya kuma halilu yace ai tsohuwa kikayiwa rashin kunya"
"tho gwaggo ai itace ta samin baki a magana kuma tace min masifaffiya"
"amman ai kinsan
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download MAIRO

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album