Join Our WhatsApp Group

MADADI Complete Hausa Novel Document by MADADI


MADADI

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 50353



MADADI

Reading Time: 4 Hours

Added On: 18, Oct 2023

Author: Binta Umar Abbale ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : *MANAZARTA WRITES ASSO

Author Phone : 07084653262

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 274.31 kb

File Type: txt

Views: 1089+

Download: 608+

Last download: 2 hours ago

Description/Story: *🗯️MADADI!!💍*
_(Ba Haram Bane!!)_

*NA*
*BINTA UMAR ABBALE🍒*
~~~~~~~
*MANAZARTA WRITES ASSO*📚🖊️
_'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_
~~~~~~~
~~~~~~~

*'Kir'kirarren labari ne kuma ba'ayi dan aci zarafin wani ko wata ba. Wanda yaga yayi dai-dai da yanayi na labarinsa to a rashin sani ne*
~~~~
*Ban yarda a sauya min salon labari ta kowace siga ba, wanda ya sanja min labari na ta wata hanya daban to ban yafe ba*
~~~~~~

*NASIHA*
```A wasu lokotan sauyi na rayuwa yakan zowa mutum. misali da farko kana cikin 'kunci sai Allah ya saukar maka da farin ciki wanda zai sa ka manta ba'kin cikin ka na baya. Idan kaga haka ya kasance da kai/ki to tabbas ka/ki ji'banta dukkanin al'amuranka ga Allah. Na biyu kuma kana cikin farin ciki katsaham! Ubangiji sai ya saukar maka da ibtila'i na rayuwa gabad'aya al'amuran ka su dagule! To idan irin haka ta kasance da kai sai ka nutsu kayi tunanin shin wane laifi kayi wanda Allah ya saukar maka da ibtila'in rayuwa, kada ka/ki ce bari kaje gurin malaman duba su duba maka ko wani ne yayi maka asiri daga ka/kin aikata hakan shikkenan ta'bewa da lalacewa ta tattara a kanka ko a kanki, idan ka/ki fad'a ko wane irin bala'i na duniya Ubangiji kad'ai zaka/zaki fuskanta da matsalarka lokaci guda zai magance maka/miki, Allah ba'a had'ashi da abokin tarayya! Idan ka kuskura ka had'a Ubangiji da wani to zaka/zaki dawwama cikin 'kunci da lalacewa har 'karshen rayuwar ka/ki.```


*SADAUKARWA GARE KU*
'Yan Uwa Rabin Jiki♥️

*SADDIQA UMAR ABBALE*
*HALIMATU UMAR ABBALE*
*NAJA'ATU UMAR ABBALE*
~~~~~~~~~~~~~


*1*
"Innalillahi wa'ina ilaihi rajiun."! Abinda Baba Talatu tafad'a kenan ta kalli Saddiqa dake gefe a tsaye tana hawaye tace" Yi sauri ki d'ebo ruwa suma tayi." Saddiqa ta futa daga d'akin da sauri, karo suka ci da Baba Malam da Babban d'ansa Alhaji Magaji." Baba Malam yace." wato dai har yanzu Kuka kuke yi ko da alama dai kuna so ku hana Halima ta kwanta lafiya a kabarin ta." Tana girgiza kai had'e da 'kokarin mayar da hawayen idonta tace"Baba Malam mun daina kuka Yaya Naja'atu ce tafad'i ta suma shine Baba Talatu tace na d'ebo ruwa." Da sauri Baba Malam da Alhaji Magaji suka shiga d'akin. ita kuma ta futa da saurin gaske, ruwa ta d'ebo cikin kofi ta shigo d'akin dashi.
Baba Malam dake tsugune kusa da Naja'atu yana mata addua ya kar'bi ruwa ya shiga yayyafa mata a fuska, Baba Talatu hawaye kawai take sharewa tana girgixa kanta.
Baba malam sai da ya yayyafa mata ruwan sau uku sannan ta saki wata ajiyar zuciya mai kar'fi! idanunta ta shiga kiftawa, sai ta mi'ke zaune da sauri ta shiga rarraba idanunta a kansu.
Baba Talatu ta ri'ke hannunta tana fad'in "Naja'atu kiyi hakuri kada ki jazawa kanki lalura." Ihu! ta zumduma! tasa hannu ta toshe kunnuwanta jikinta na wata iriyar kyarma! tace"Baba Talatu kunnuwa ba zasu iya d'aukar wannan maganar taki ba! a ina aka ta'ba haka *Uba ya Auri 'Yarsa* ashe dama dake da Baba malam dashi kansa Abban nawa dukkanin ku maguzawa ne ku baku san addin........Kafin ta 'karasa Alhaji Magaji ya kwad'a mata mari! yace."Ke ki nutsu ki shiga hankalin ki bama son shirme da shashanci ki saurara ayi miki bayanin yanda al'amura suke."

A zabure! ta mi'ke tsaye! kamar wacce zata tada iska tace"Baba Magaji ni bazan fuskanci komai ba ba kuma zan nutsu ba, saboda ni ba kafura bace wallahi sai na kashe kaina idan kuka d'aura min aure da Ubana, wai baku ji sunansa bane Abban Naja'atu fa sunansa amma shine zaku daura mun aure dashi! to dukkaninku sai na kaiku *Hizbah!.* Ta'karashe maganar tana wani irin kuka mai cin rai.

Baba Malam ya goge guntin hawayen idonsa ya ri'ke hannunta da fad'in "Auta zauna ni da kaina zan warware miki abunda baki sani ba." Fuzge hannunta tayi tana 'kokarin tsallakeshi ta wuce! Alhaji Magaji yayi sauri tare mata hanya Yace."Naja bakya jin magana ko? To shikkenan idan baki kaimu *Hizbah* bakya 'kaunar Allah." Yafad'a babu wasa a tare dashi.
Hannunsa ta ri'ke jikinta sai mazari yake tace"Abba Magaji ka duba maganar nan da kyau fa! Kayi duba na tsanaki! ya za'ayi dan kawai Mamanmu ta mutu sai suce zasu d'aura min aure da Ubana wace irin rayuwa ce wannan."!!! Tafada cikin wani irin sauti!! Shima a fusace! Yace."Wai ke waye ya fad'a miki Alhaji Abbas Ubanki ne."!? Shuru tayi tana binsa da wani irin kallo! bakinta sai rawa yake yi. da kyar ta iya bud'e bakinta tayi magana....."Baba Magaji bangane maganar ka ba."! murya na rawa tayi maganar, Baba Malam ya zaunar da ita kusa dashi hannunsa cikin nata ya rike sosai yana kallonta, tausayi take bashi sosai, tabbas yasan dole ne ta shiga rud'ani da tashin hankali sakamakon bayyanuwar abinda yake rufe tsayin shekaru goma sha shida! da suka wuce. Wanda ta d'auka a matsayin mahaifinta dashi ake maganar d'aurin aure a tsakaninsu, babu shakka duk wanda ko yaji wannan lamarin dole ya shiga halin d'imuwa da tashin hankali

'Dakin ne yayi shuru na tsayin mintina uku kowa jikinsa yayi sanyi mussaman Naja'atu wacce take jin wata irin fargaba da fad'uwar gaba, tunda Abba Magaji yayi furucin cewar ba Abba Abbas ne mahaifinta ba take wata zabura tana rarraba idonta a kansu bakinta motsi kawai yake tana so tayi magana amma ta rasa me za tace! fashewa tayi da wani kukan tana kallon Baba Malam da kansa yake sunkuye sai zufa yake gogewa, tace"Baba malam kuna so nima na mutu ko? kuna so kamar yanda kuka rasa mamana nima ku rasa ni ko ? zuciyata daf take data daina aiki sakamakon bala'in da kuka jefata a ciki! Baba Magaji yace wai Abbana bashi ne Ubana to shikkenan sai ku fad'a min wanene ya haifeni."? Murya na rawa ta 'karasa maganar.
Baba Malam ya d'ago kansa a nutse yace."Naja'atu Nine Ubanki ni na haife ki Alhaji Abbas Uban ri'kon ki ne kuma miji ga 'yar uwarki Halimatu." wani irin kallo ta shiga yi masa tana girgixa kanta sai hawaye ya wanke mata fuska! murya a sanyaye tace"Baba malam ya akayi haka? ya kuka yi mun wasa da hankalina? ni ban yarda kaine mahaifina ba, Abba Abbas shine Ubana shi na sani tunda na taso shine yaci dani yasha dani ya tufartar dani ya tsaya a kaina nayi karatu kuma shi nake so ya aurar dani ga mijin dana za'bawa kaina."! Ta'karasa maganar cikin yarda da abinda take fad'a.
Abba Magaji ya fusata! sosai ya bud'e baki zaiyi magana Baba malam ya d'aga masa hannu yace."Kada kayi mata tsawa ko ka hantare ta, dole ne dama haka ta kasance da ita damu bakid'aya, ha'kika mutuwa itace ta janyo mana wannan tashin hankalin dan da Halimatu na raye to babu shakka Naja'atu zata cigaba da zama a matsayin 'yar data haifa alhalin kuma 'kanwa take a gareta, Yanzu zamu bari ta nutsu tukkuna zuwa dare sai mu sake wani zaman domin mu sanar da ita abinda ya faru a baya wanda bata sani ba." Abba Magaji ya sauke ajiyar zuciya a nutse yace."Shikeenan Allah ya za'ba abinda yafi alkairi." Baba Malam ya amsa da amin kana ya mi'ke suka futa a tare.

Suna futa, Naja'atu ta kalli Baba Talatu tace"Baba dan Allah dan annabi kada ki bari al'amarin nan ya tabbata, ke macace ce mai hankali da sanin ya kamata kuma kina zuwa isilamiyya kin san dai haramun ne Uba ya auri 'yar sa ko."? A zauce! take maganar.

Baba Talatu tace"Naja'atu Alhaji Abbas ba Ubanki bane an fad'a miki Mijin Yayar ki ne Halimatu Allah ya ji'kanta, Alhaji Abbas kinga wacce ya haifa nan ita da 'yan uwanta su Mussadiq.'' Ta nuna mata Saddiqa dake zaune a kusa da ita.

Wani irin kallo ta shiga binsu dashi tana girgiza kanta, ta rasa a'ina zata ajiye wannan babban al'amari a cikin zuciyarta, *Abbah Abbas* ba shine ya haife ta ba *Baba malam* ya haife ta? anya kuwa da gaske suke wannan maganar ko dai kawai suna so bukatarsu ta biya ne gurin ganin sun d'aura mata aure da *Ubanta* tabbas dole ne ta nemawa kanta mafita dan ita kam bata yarda da wannan maganar da suke ba.
Tana kallon Baba Talatu da Saddiqa suka suka futa daga d'akin, ta shiga girgiza kanta tana masifar mamakin a'lamarin, kwanciya tayi kan tabarmar dake shimfid'e a dakin ta shiga tunano rayuwar ta ta baya tare da mutanan data dauka a matsayin iyayenta.




*GA MASU BUKATAR KARANTA BOOK DIN ZASU TURA #400 SINGLE, VIP GROUP #600 GA ACCONT D'IN DA ZA'A TURA KUDIN.......0542382124.....BINTA UMAR GTBANK.....IDAN KATIN WAYA ZAKI TURA KIYI MIN MAGANA TA WHASAP DA WANNAN NUMBAR......07084653262.....IDAN KIN SAN BA BIYAN KUDIN LITTAFIN NAN ZAKI YI BA DON ALLAH KADA KI KIRA WAYA TA KO KIYI MIN WATA MAGANA TA WHASAP*

*MUTANAN MU NA NIJAR IDAN KUNA SO KU BIYA KUDIN LITTAFIN ZAKU TURA DALA DARI TA WANNAN NUMBARS.........90899076_88137740 KATIN AIRTAL KO ORANGE.*
[10/15, 1:05 PM] Gagarabadau👺: a

*🗯️MADADI!!!💍*
_(Ba Haram Bane!!!)_

*NA*
*BINTA UMAR ABBALE🍒*
~~~~~~~~
*MANAZARTA WRITES ASSOCIATION📚🖊️*
_'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi._
~~~~~~~~
~~~~~~~~


*SADAUKARWA GA DUK WANI A HALINA DAKE CIKIN WANNAN UNGUWA♥️*


*2*
*'Kofar Na'isa* Unguwa ce mai cike da d'umbun tarihi, duk wanda ya kwana ya tashi a cikin birnin kano ya san da zaman unguwar. 'kofar na isa unguwa ce ta malamai masana addini da kuma 'yan boko masu aiki da iliminsu, duk wanda yake mu'amula da d'an cikin unguwar zai gane cewar suna da wani irin quality wanda Allah yayi musu, saboda sun iya mu'amula da mutane sosai! akwai masu kudi a unguwar akwai marasa karfi a ciki, dai-dai gwargwado masu rufin asirin dake cikin unguwar suna taimakawa marasa shi mussaman da azimi suna hidima sosai da sosai da wuya kaji ance maka ga wata hatsaniya ta tashi a unguwar irin ta *Daba!* ko kuma *Sace-sace* dai-dai gwargwado suna bawa yaransu tarbiya had'e da ilimin addini dana boko!

Alhaji Sama'ila mai kwano wani attajirin mai kudi ne a cikin unguwar wanda yayi suna sosai dan idan kana neman gidansa daga bakin titi ka ambaci sunansa za'a nuna maka Alhaji Sama'ila mai kwano mutum ne mara ganin 'kyashi mai kaunar dan uwansa da ma'kotansa, Yana da 'yaya Uku kacal wanda matarsa Hajiya Abu ta haifa masa su, Biyu maza mace d'aya, amaryarsa mai suna Hajia Rabi bata ta'ba haihuwa ba tsayin shekarun da sukayi a tare! Yana zaune da ita haka dan shi mutum ne mai mi'ka al'amuransa ga Allah yasan tabbas Allah ne ke bada haihuwa kuma shine yake hanawa.
*Ramlatu* itace babba a cikin 'yayansa sai wanda yake bin ta, Abbas sai Alhasan shine na karshe! tunda su Abbas suka taso a cikin unguwar nan suka ga yanda mahaifinsu ke mu'amula arziki da makotansa sai suma suka fara kwantantawa, hakan yayi wa mahaifin nasu dadi sosai ya kuma 'kara nuna musu cewar hakan da sukeyi shine dai-dai dan cikin jinsin mutunan da Allah ya hallita a duniya babu wanda yafi wani a gurinsa sai wanda yafi bauta masa, kada su nuna sunfi karfin yin mu'amula da wanda suka fi rufin asiri, to babu shakka watarana Allah zai iya 'kwace damar dake hannunsu ya mi'kawa wanda suke ganin bai isa ba......Wannan dalilin ya sanya suka saki jikinsu da kowa suke mu'amula a cikin unguwar tamkar sauran mutane.

'Karamin gida ne madaidaici mai kofa gami da dakalin siminti a kofar gidan, gidan na kallon gate din gidan Alhaji Sama'ila hanya ce kawai ta raba tsakaninsu! Malam Baba shine mai wannan gidan, kamilin mutum nitsatstse mai kamala da dattako, malam baba mutum ne shi mai yawan ibadah da karatun al'kur'ani kusan duk azimin yana zaman tafsiri a kofar gidansa, inda Alhaji Sama'ila ke sawa ana fito da sadaka daga gidansa, akwai jituwa mai kyau a tsakaninsu dan sai nace halinsu ne yazo daya na gudun duniya shiyasa suke zaune lafiya da kowa, Alhaji Sama'ila ya dauki ragamar gidan Malam Baba a hannunsa ba wai dan shi malam din ya gaza ba Malam na futa sana'arsa kuma sa'i da lokaci al'amajiransa na kawo masa abun arziki gidansa babu yunwa ko kad'an! malam nada 'Yaya Uku wanda suka haifa tare da matarsa Baba Talatu Babban cikinsu shine Adamu wanda yaci sunan mahaifinsa sai suke kiransa da Magaji, Halimatu itace ta biyu sai kuma Naja'atu da tazo a karshe! Lokacin da suka haifeta har sun cire tsammani da sake haihuwa sai kuma Allah ya kawo cikinta, lokacin Halimatu na daf da kammala secondary skuul lokacin tana da shekara goma sha shida a duniya.

Tsakanin Abbas da Magaji akwai jituwa sosai suna abota mai kyau da tsabta komai nasu tare sukeyi karatu tare su d'inka kaya iri daya hula iri d'aya takalmi iri daya kai hatta da agogo iri daya suke daurawa! Sai kuma Allah yasa shekarunsu suka zo daya da juna yanzu haka suna matakin shekaru talatin da d'aya koda biyu Lokacin ne kuma iyayensu suka fara yi musu maganar aure dan sun riga sun mallaki hankalin kansu! kuma suna zuwa kasuwa suna harkokinsu, Alhaji Sama'ila yanzu ba ya fita kasuwa sosai su ya d'ora kan harkokinsa na yau da gobe! Alhaji Sama'ila nada shaguna sama da talatin a cikin kasuwar sabon gari kuma dukkanin rumfunan sa harkar siye da siyarwa akeyi a ciki, suna harkar kayan rufin gida da kofofi da ta gogi sannan kuma yana da gidajen bulo suna buga bulo da harhad'a intar lock da ties, mutane da yawa naci da sha a karkashin wannan bawan Allahn, to ganin 'Yayansa sun kai munzali ne yasa ya d'ora su kan harkokinsa na kasuwa kwata-kwata baya nuna bambanci tsakanin Abbas da Magaji Abinda zaiyi wa d'ansa Abbas shi yake wa Magaji, har jama'ar unguwa na surutu kan cewar ba haka kawai Baba Malam ya barshi ba wasu suna gani kamar yayi masa asiri ne domin ya mallake shi shida dukiyarsa, wannan cece kucen da mutane keyi bai dameshi ba, dan saboda yasan Malam baba ba zai ta'ba cutar dashi da zuriarsa ba.


Mama Ramlatu babbar Yaya gasu Abbas tayi aure a cikin unguwar dan gaba dasu kadan cikin unguwar Tudun wuzurci! wanda ta aura yana da rufin asiri dai-dai gwargwado amma tana da kishiya, Ramlatu wata irin mata ce mai izzah da ta'kama! bata da hali mai kyau! Tayi ta wulakanta kishiyarta kasancewar ta yar talaka gorin yau daban na gobe daban! a duk sanda Alhaji Sama'ila zaiyi mata aiken kud'i ko kuma tufafi sai ya had'a da kishiyarta kafin ta bawa kishiyarta sai ta gama yi mata gori sannan! Ita kuwa da yake mai hakuri ce sai dai kawai ta girgiza kai ta kyaleta, gabadaya Ramlatu bata dauko halin mahaifinta da 'yan uwanta ba.
Lokacin data haifi 'Danta na fari! sosai Mahaifinta ya gatantata daki guda aka cika mata da kayan barka, shi kuwa...


Read / Download MADADI

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album