Join Our WhatsApp Group

KURUCIYAR MINAL Part 1 Complete Hausa Novel Document by KURUCIYAR MINAL Part 1


KURUCIYAR MINAL Part 1

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 75960



KURUCIYAR MINAL Part 1

Reading Time: 6 Hours

Added On: 08, Feb 2024

Author: Miss Unthiclobanty ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 416.65 kb

File Type: txt

Views: 422+

Download: 307+

Last download: 3 days ago

Description/Story: 🏆KURUCIYAR MINAL🏆

1 - CHAPTER 1-10
🏆🏆KURUCIYAR MINAL🏆🏆

🌹by miss untichlobanty🌹

*🍀CHAPTER 1🍀*

Amina ce zaune a kan wani lotsatstsen katifanta Kamar an taka bredi,basai nayi magana akan gadonta ba . Gefe wani kwano ne with a remained smelly stinky tuwo miyan kuka Wanda da alama tunna jiyane bata fitar da kwanon ba.

kuka take rizga Kamar ranta zai fita
innace ta shigo dakin domin ganin Lafiya yau yar lelenta shiru bata fito ta kama aiki ba? Turus tayi tana ganin ikon maleeku

Wani Abu na yar lele sai ita idan Ba haka Ba ya za'ayi mutum shi daya ya zauna yana kuka babu dalili.

innarce ta rafka uban salati Kamar an kama malam da karuwa tace me zangani haka aminatu Lapiya ? wa yatabo min tuwalle? me ya saki kuka?

Sai alokacin Amina ta dago ta soma magana cikin shessheka Kamar haka inna Dan Allah ki yafe min,ki roki kanwata deejeh ma tayafemin,awararta Dana karba tayi hakuri,dukan da nake mata ma na daina,kuma...kuma bazan kara zubar mata da abinci Ba kuma Wlh bazan sake kwace mata rakenta Ba Nayi alkawari har naira 50 din tama zan biyata 😭 duk rashin mutincin danakeyi Allah na dena Wlh na dena ta kara fashewa da kuka.

Galala inna tayi tana kallonta Wai yau aminatuwa ke Neman yafiya harda kiran deejeh kanwarta, lallai za'ayi ruwa da kankara
Inna tace toh yar lelen inna yi shiru kisanar dani ya akayi?me ya faru?
Minal tace inna aradu mafarki Nayi Wai cutar laser fever ta kamani Wai na mutuuu!
Inna tace kinga irinta ai mutum ace sai shegiyar kazanta yaushe Rabon da Kiyi wanka Yanzu?
Kina ganin kin kyautawa kanki kenan ?
Kuka ta fashe dashi tace kwana biyar ne kacal fa.

Inna tace ko kunyar fada bakyaji? wannan Ba laser Ba har ebola ma zata kamaki ai.
Kuka ta kara fashewa dashi tana shure-shure tace haba inna dama Ba sona kike Ba ?
Kuma ai dukda bana wanka ina canja pant fah.😭

Inna tace ni rufe wannan bakin naki karki taramun makwabta gashi duk kin cikani da warin baki.
Tashi dallah kije ki wanke baki Kiyi wanka.
Kurma ihu tayi tahau shure-shure da burbuwa.

Nan inna ta lallabata tace mata ai mafarki Ba Gaskiya bane.... haka dai ta hakura nan inna tace taje tayi wanka taci abinci Dan yau zata rubutar jarabawar karshe a makaranta daga shi next term zasuyi WAEC haka dai ta hakura ta shirya.

Ta fito zata tafi tace inna kin Tina wannan 100 Dana taba aramiki?
inna tace yaushe? tace lokacin nan sanda muka fara jarabawa
inna tace na Tina tace ki Dan banishi,inna tace haba yar inna nawa na baki atsakanin wannan lokacin?

Tuwalle tace ehheeeen wato dama badan Allah kika bani Ba inna ?!cabdi wallahi Nide sai kin bani kudin nan.

Inna tace sarkin jaraba, kin fita naci Kamar me, ta since bakin zaninta ta miko mata wata kodaddiyar Dari biyu tace ingo kuma kikawo mini canji domin shi kadaine gareni. Inna ta fadi dukda ko tasan da wuya ta kawo chanjin.
Yamutsa fuska minal tayi kamin ta karba tare da Cewa dande ina bukatar kudin ne da yasin bazan karba tsohuwar kudinnan Ba.

Nan ta rungumi inna Kamar da gaske sannan ta fita tare da Cewa sai na dawo sannan ta biya ta gidan su kawarta zaliha domin tafiya makaranta.

Koda aka tashi Tara(break) tsallaka katangan makaranta tayi taje tasiyo gurasa a kasuwa na duka kudin tayi sadaka dashi wa almajirai akan Allah ya kara rufawa iyayenta asiri

(dukda Cewa Amina akwai tsiwa da rashin mutunci ga Wanda ya nema amma akwaita da tausayin iyayenta sosai domin kazantarta Nada nasaba da haka acewarta Idan sabulu da turarenta basu Kare Ba ai iyayenta bazasu kashe kudi wajen siyan wani Ba shiyasa sau biyu take wanka a sati su inna har sun gaji da mata magana)

Amina Yusuf yarinya ce er shekara 18-19 farace sosai ga hanci shima daidai misali 8 figure ce ga tsayi daida gwargwado idonta ko sexy eyes ne gashin kanta kuwa ba'a magana.

Babanta wato malam Yusuf Wanda akafi sani da baban kowa carpenter ne bashida karfi amma yanada rufin asiri sannan duk anguwar ana ganin girmansa sosai manya da yara.

Asalin sa fulanin taraba ne wadda yarasa kowa NASA sanadiyyar gobara tun yana shekara 18 haka yarike Kansa har yakai 25 ananne ya dawo kano da zama inda ya hadu da falmata wanda ake kira da inna wacce take kanuriyar barno ce gyaran miki da turaren wuta take a kanon har sukayi aure dagabaya suka Koma Kaduna da zama Inda suke can cikin malali ahaka har inna ta haifi danta na fari wato Abubakar Wanda yanzu yake project a ABU amma shi yake rike kansa domin ya ragewa iyayenshi nauyi sannan yakanyi musu aike idan ya samu hali tunda Ba zaman banza yake Ba.

Daganan inna bata kuma haihuwa Ba sai bayan shekara takwas Inda ta Haifi Amina wacce take yarr jagwal ce ga neman magana,ga tsiwa, saide matsoraciya ce na masifa amma ta rike addininta dukda ko Ba ganewa ake Ba.

Sai daga baya inna ta Haifi khadijah wacce take auta kuma shekaranta 12.

Wannan kenan

Kubiyoni domin jin cigaban kuruciyar minal

26th April 2019

Love you all

Mzz untichlobanty💕
[1/11, 1:06 AM] Mzz_Untichlobanty💞:
*🏆🏆KURUCIYAR MINAL🏆🏆*

🌹by miss untichlobanty🌹

*🍀CHAPTER 2🍀*

*BAYAN WANI LOKACI DA RUBUTA JARABAWAR MINAL*

*Morning*

Minal rike da sakamakonta a Hannu miftahu (kanin hannatu zamu ganta a gaba #chapter 8 ) yace manya manyan Yan boko har an karbo sakamakon kenan da fatan wannan karan ma ba'a dauko ajinba. Cukumosa minal tayi ta naushi bakinsa tace aiko Ba Komai ni nane makarantar wasu a yawon banza za'a kare. Daidai lokacin sani (yayan bilkisu itama zamu gantaa gaba #chapter 8) ya wankawa minal mari juyowa tayi tace buhun bala'i bai ankareba yaga an nunashi wa sama an nana da kasa suka minal tamai jina-jina sannan tasa yara sukabuleshi da kasa.

*Evening*

A guje yara suka rugo Suna oyoyo baban kowa oyoyo baban mu! dama ya saba Dan haka yasa kullum baya rabuwa da tsaraba, hanjin ligidi mai yawa acikin bakin laida ya ciro ya basu suka karba Suna godiya kamin suka raba, wata yarinyace tace baba yau wani tatsuniya zaka mana yace tatsuniyar gizo bakin barawo zan muku.
Lado ne ya shinfida masa buhu Kamar yadda suka saba sannan Suma yaran suka zazzauna nan dattijonnan ya soma musu ta tsuniya......

🌹.............

Wasu samarine zaune Suna busa sigari wayan dayansu ta soma kara daukowa yayi yaga karfe alarm dinsa na large hudu ne take ya kashe sigarinsa yace kai yau fa alarm NASA mana aradu lokacin dawowan tsohonnan yayi,dariya suka fashe dashi wani yace Ba mamaki ya tsaya yiwa yara tatsuniyane. Sukace Ba shakka amma fa tsohonnan yana yiwa mutane cikas ka duba abinda yar b*ra ub*an yarnan tasa tayi dazu.
Daidai lokacin baban kowa ya karyo kwana,a take suka karkade jikinsu tare da wulla alewa a baki Dan kar yaji warin sigarin tasu.

Nufosa suka farayi Kamar abin arziki shima da murmushinsa yaje nufosu domin yaune karo nafarko dabai kamasu Suna busa sigari Ba.

Saide kash suna motsowa kusa dashi ya jiyota aiko take annurin fuskarsa ta dauke sukace babanmu sannu da zuwa Suna masu durkusawa

bata rai yayi yace Duba su Kamar da haske Kamar mutanen arziki, Wai Ku fi sabillilahi bazakuyi wa kanku fada ba, Kamar da gaske nadau kunyi hankali Ashe da sauran Rina a kaba,

Bakusan cewa wannan shaye shayen naku yana janyowa iyayenku Bacin sunaba?ko kunaso duniya tazagesu ne?girgiza kai sukayi sukace ayi hakuri baban mu Insha Allah zamu daina.

murmushi takaici yayi domin Indai wannan alkawarinne to an karyasa tun kafin adaukesa yace Allah ya bada ikon dainawan,kuna batawa kanku rayuwa ko bakusan Cewa duk abinda mutum yayi yana kuruciyar shi zai bishi har girma ba ko kunaso idan kun hayayyafa acewa yaranku kun taba busa wiwi ?girgiza kai sukayi yace Idan yaranku suka sha Ku ya zakuji hada baki sukayi wajen Cewa bazamuji dadi ba yace Idan Baku sani bama Ku sani wannan shaye shayen yana haifar da tabin hankalin,lalacewar koda da zuciya kuma tsaf zai kashe mutum. Ku a haka zaku hadu da Allah? Kuma kuna tunanin Idan an tafi a haka ba matsala?Ba Arabic Ba bokon?Allah ya Shirya....

Tafiyarsa ya cigaba dayi yana mai fada akan yadda matasa ke bata rayuwarsu.

Majalisar su malam yakubu zai wuce sukace salamu alaikum baban kowa barka da war haka murmushi ya soma musu sannan ya mika musu hannu sukayi musabaha.
Malam isa mai wankin hula ne yace ya naganka haka ne ? baban kowa yace kaide bari yaran yanzu basu rabuwa da kayan bakin ciki yanzu na.....

Malam saminu ne yazo yana girgiza kai alamun alajabi jikinsa a sanyaye ya zauna
Baban kowa yace haba malam saminu ya haka zakazo ka zauna bako sallama? inkai kayi haka 'yan'yan mu kuma yaya zasuyi ?

Malam saminu ne ya cire hularsa ya ajiye kana yace wato wani abune yayi mugun jijjigani, Wai yar gidan malam ado salma akayiwa fyade saboda sakacin maihaifiyarta. fita tayi bayan magariba ba'a saniba uwar kuma da bata ganta Ba bata nemeta Ba sai da taga kusan goma ya wuce shine ta Sanar da malam adon. neman duniya an mata ba'a ganta Ba yau da asuba aka yadda ita koda aka kaita asubiti likitoci nata kokarinsu amma ina. yanxu yanzunnan rai yayi halinsa,Allah ya mata rasuwa!

Shiru wajen ya dauka kamin caaan malam sambo Wanda tun dazu baiyi magana ba yace Wai salma dai guda Dana sani yar shekara 6?itafa wannan salmar dai inji malam saminu
Salati suka rafka jikin kowa yayi mugun sanyi kamar an musu duka.
Allah sarki salma yarinya mai hankali da Shiga rai. Allah yaji kanta bari anjima sai mu hadu muje muyi masa ta'aziya nan dai suka Dan tad'a kamin malam Yusuf yayi gidansa.

Koda yake tafiya a hanya sai surfo masa gaisuwa ake ta ko'ina manya da yara. Atakaice de baban kowa mai jama'a ne.

Yana isowa kofar gidan sa, basheer mai shago yace baban kowa ina wuni,Lpy klau basheeru ya shagon?basheer yace Alhamdullah baban kowa yace masha dafatan dai yauma minal bata taba kowa Ba Dan yau da safe tace Mani Wai tun jiya akace suje su karbo sakamakonsu. Basheer yace Gaskiya baban kowa yau minal bata yi hayaniya da kowa Ba hasalima ko fitowanta bangani wadda nima abin ya bani mamaki da alamu dai kawattamu ta natsu(haka basheer din ke kiranta domin ya kasance abokin ya abubakar ne tun yarinta shiyasa ma yayiwa baban kowan karya Dan kar yasa wa ransa damuwa sosai)
Baban kowa yace to Masha Allah haka akeso ai ni bara in Shiga Daga ciki ko? Allah yayi albarka basheer yace amin.

Minal na zaune tana yanka kubewa taji sallamar mahaifinta hantar cikinta ne ya kada da gudu ta mike har tana tuntube a 360 ta fada daki,garin sauri ta barar da yakuwar da take yankawa innace ta haba er lele lafiyarki kuwa zaki barar mani da......

Bata ida maganar ba baban kowa ya shigo yana cewa inata sallamma Baku amsa ba Kamar ba kowa a gidan inna tace yi hakuri malam sannu da dawowa Wlh wannan yarinyarnance ta fada daki da gudu har tayi Mani bari banjika ba yi hakuri bara na kawo ma ruwa
Takalmin sa ya cire ya zauna a tabarmar dake shinfide a tsakar gidan yana Cewa halan wayanta aka kira take wannan gudu , inna dake shirin bude randa domin sachet watern su ya kare tace anya kuwa?hira fa muke daga jin sallamarka ta rusa da gudu Kamar taga aljani,baban kowa najin haka jikin sa yayi sanyi bayason irin faduwsrnan da yarda keyi a makaranta domin Hanson tayi karatu ta inganta rayuwarta

Yace takarbo sakamakon jarabawar tasu kuwa inna tace eh ta karbo dazu gasucan yana kan yana kan taaga(window),tashi yayi jiki babu kwari ya dauko ya Duba aiko Kamar yadda yace ne ankuma na 48 tazo acikin su 52 a Dan fusace yaje kofar dakin yace aminatu me kikeyi acikin dakin nan,minal tace Riga make canjawa yace inba so kike na Shiga Ba maza ki fito tace baba aradu Babu Riga ajikina wanka make shirin yi yace Kamar da haske rabon da Kiyi wanka keda kanji Ba tare da dance Kiyi Ba yanzu shekaru 6 kenan amma shikenan ni bara in dubo sakona waje.


Oya show some love
By voting,
liking,
sharing
and
commenting

Tnxs for reading

26th April, 2019

Mzz untichlobanty💕
[1/11, 1:09 AM] Mzz_Untichlobanty💞:

*🏆🏆KURUCIYAR MINAL🏆🏆*

🌹by mzz_untichlobanty🌹

*🍀CHAPTER 3🍀*

Sanda ta kara kusan 5min sannan ta leko da kanta duk ta hada gumi saboda rashin gaskiya

Saukan rankwashin da tajine yasa ta sankare a wurin na wani sakanni.

Durkushewa tayi a wurin tana tutturo baki kamar zai taba kofa.
Baba ne yace rufi min baki kamin in kara miki,maza tashi.

Mikewa yayi tana zuzzunburewa tace haba baba ko Dan wannan rankwashin da kake samani kamar abinci Ba dole na KASA kokari Ba kana taba min CPU na bakasan Cewa itace masarrafin Dan Adam ba?

yace yimin shiru kamin in da'da maki wani yar kaniya kawai,me kwakwalwar kifi Allah dai ya bude maki wannan toshesshiyar kwakwalwar taki.

kuka ta fara yi tana buga kafa ni Gaskiya baba kwakwalwata ba a toshetake baaa😭 inna tace ni yimin shiru karki taramin makwabta ehe.

Murya ta kara baba yace bari kiga ikon Allah mikewa yayi ya dauko sanda.
yanda Kasan Anyi ruwan sama an dauke tsit ta shanye kukan da takeyi tana tsitstsilla idanu tare da sheshsheka baba yace banson jin sheshekar nan. Ki natsu bari inga tsiyar da kika shukowa mutane wannan karan.

Mutum bashida aiki sai fada ni Nayi mamaki ma yau kusan sati 2 ba'a kawo kararki Ba.
Turo baki tayi duk yasha mai sai yalki take tace yo ai dannayi mafarkin na mutu ne kuma ko yanxu ma Ba fasawa nayi Ba.

Kallonta baba yake har ta ida maganan ta already ya Ciro takalmi Dan haka ya lafta mata.

papers din ya fara dubawa yaga  subjects 2 ne takeda A amma saura Wai sai a slow saide rubutun nan war inka gani zaka dauka wata Dr ce tayishi sai ka karantawane kaji Kamar kayi kuka.

takaicin rashin kokari na diyartasa abar kaunarsa ne ya taso mai.

Kansa  kawai yake girgizawa saboda takaici bazai musaba Idan akace masa Dan primary five ma yafi yar tasa kokari.

Tsawa ya daka mata ke zonan !
Simi simi taje ya kalleta sannan yace yanxu ke ahakan zaki tafi makarantar gaba?ki Duba fa gododuwar banza da wofi. Murmushi tayi
inna tace Allah zanci mutuncinki ana miki fada kina dariya saboda kin daina mutane ko? Tace Toh Toh Toh ni inna me Nayi ? Dakuwa inna ta mata tace kaniyarki kikayi

tace to yi hakuri bazan kara Ba shikenan aiko?yauwa inata Dan Allah ki siyan awara?harara inna ta banks mata tace ba'a siya dinba
Baba dake jinsu  ya tattare takardun yana cewa ace mutum anmai repeat har sau biyu amma bai gyara ba nasan duk ajin keda zaliha kun fisu girma amma kanku Kamar kifi har gara ita akanke.
antara dakikai biyu a aji daya bakuda aiki sai ciye ciye kuma da kunada kokarinku tunda kuka fara Hulda da wannan fatiman shikenan lamuranku ya tabarbare.

tace toh Ba kai kake Bani kuddin Ba? Kuma ai fatimamma sun Koma kano.

Yace au haka zakice?

Inna tace kaga malam rabu da ita kar hawan jininka...


Read / Download KURUCIYAR MINAL Part 1

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album