Join Our WhatsApp Group

AUREN SHEHU BOOK 2 Complete Hausa Novel Document by AUREN SHEHU BOOK 2


AUREN SHEHU BOOK 2

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 57938



AUREN SHEHU BOOK 2

Reading Time: 4 Hours

Added On: 21, Mar 2024

Author: Khadija Sidi ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 279.08 kb

File Type: txt

Views: 227+

Download: 220+

Last download: 3 days ago

Description/Story: Auren Shehu 2

Afuwan akan rashin cika alkwari, aiki ya min yawa, a yi min hakuri.



Nan Kawu Iliya ya bar Usman da Bello ba tare da yayi kokarin rarrashin su ba, yana cike da tsabagen takaicin dauke kafa da Usman yayi daga Rugar Shehu. Sun kai kusan minti talatin gaban kabarin Mahaifiyar su, Usman gani yake tamkar ita din ce zaune kusa da shi. Sai da sauran matasan Ruga su ka zo su ka ja shi suna mai bashi baki sannan ya hakura ya ta so su ka nufi cikin Rugar Shehu.

Tuni labarin dawowar Usman ya zaga lungu da sako na Rugar Shehu, har ya ga kai kunnan Baffa Mudi, hankalin sa tashe ya zo ganin shin da gaske Usman din ne dan kuwa bai taba tsammanin zai sake taka kafar sa a Rugar Shehu ba bayan kurciyar da ya masa, babban tashin hankalin sa be wuce kar Usman ya ce zai kwaci sarautar Rugar Shehu ba dan shi kan sa ya san jama'ar Rugar sun gaji da mulki irin na sa.

A dandalin shadi ya tarar da jama'a sun taru makil maza da mata, Yara da manya, mata da maza, masu kida na yi, haka masu tafi, tsuffin cikin su kuwa kuka biyu su ke, kukan dawowar Usman da kuma kukan rashin Iyar sa. Cike da tsana da faduwar gaba Baffa ya tsaya gefe ya na duban duk abubuwan da ke wakana, ganin yanda Usman ya ƙara girma ya zama cikakken matashi ma'abocin karfi da kwarjini, ga matasa zagaye da shi, sai koda shi su ke, su na masa kirari da fulatanci, fadi su ke

"Dan Shehu jikan Shehu, karen bana mai maganin zoman ba na, Shehu ya tafi, Shehu ya dawo!"

Ya sanya Baffa Mudi barin wajen a fusace, cikin ran sa ya na saka yanda zai dauki mataki akan dawowar Usman. Shi kuwa Usman gangan jikin sa ne kawai a wajan, zuciyar wacce ke cike da bakin cikin rashin Iyarsa tuni ta yi nisa wajan saka yanda za ta hukunta wacce ta ke da alhakin rashin ganawar sa da iyar sa na har abada, Amma ya kudiri niyar fara raba Rugar Shehu da ummul abasin dalilin da Iyar sa ta tilas ta masa barin Rugar a karan farko, wato Baffa Mudi.

Duk yanda ya so ya kadaice shi kadai yayi makokin Iyar sa abin gagarar, mutane ke ta kai kawo cikin sashen su domin masa maraba da kuma ta'aziya. Haka kuma kishiyoyin Iyasar sa Yagwalgwal da Duduwa su ka sako shi gaba da mitar barin Rugar Shehu da ya yi. Ba shi ya sami kan shi ba sai bayan ishi'i, ya na shirin shiga bukkan sa sai ga yan uwar Mahaifiyar sa sun zo. Yayar ta wacce ake kira da Huwaila, sai kuma kanwar ta mai suna Iyalle, da kuma matar shi Kawu Iliya Hansai.

Sune su ka sa Usman gaba da fadan barin gida da yayi shekara da shekaru babu ko waige, har Iyar sa ta fadi ta mutu. Usman ya kasa musu bayanin umarnin Iyar ta sa ne ya sanya shi barin Rugar dan kuwa har lokacin be yi niyar tonawa Baffa Mudi asiri ba. Jin su na rokan sa da ya kaunaci Allah ya karbi mulkin Rugar Shehu, a cewar Huwaila wasiyar da Iyar sa ta bar ma sa kenan, ya sa shi tambayar ko da wani abun da be sani ba ne?

Nan su ka bude ciki su ka bayyana masa mulkin zalinci da Baffa Mudi ya ke aikata mu su, tare da sana'ar da babban dan sa Tanko ya shiga na garkuwa da mutanen birni ana biyan shi kudi kafin ya sake su, Kuma duka ya na yi ne da sanin Baffa Mudi. Matukar ba so ya ke a maishe da duk matasan garin yan garkuwa da mutane ba, har gwamnati ta gane ta turo a ayi kan mai uwa da wabi toh lalle yayi wani abu.

Cikin bakin ciki da jimami su ka tafi su ka bar Usman, ba su dade da fita ba sai ga dattawan Rugar Sheshu su ma sun iso gare shi da irin bukatar da dangin Mahaifiyar shi su ka zo da shi, cewar su dan babu yanda za su yi ne da tuni sun bawa Muhammadu Bello sarautar Rugar Shehu, ya duba girman Allah ya fanshe su daga wannan ukuba da su ke ciki, Allah ne ya dube su ya dawo da shi.

Cike da girmamawa Usman ya sallame su tare da mu su alkawarin zai kwana da maganar cikin ran sa, in Sha Allah zai samar mu su mafita.

Sai da kafa ta dauke sannan Usman ya sami damar shiga dakin Mahaifiyar sa cikin faduwar gaba, gani ya ke kamar zai gan ta kwance bisa gadon karar ta. Har lokacin dakin cike ya ke da kayan ta kamar ta na raye. Duk yanda ya so daurewa kasawa yayi, Yana mai rungumar zanin Iyar ta sa hawaye ke fita daga idanun sa, haka ya zauna bakin gadon ta ya ci kukan sa ya koshi, be fita ba sai da ya daukarwa kan sa alkwari biyu, na farko shi ne tabbatar da cigaba da yancin Rugar Shehu ta hanyar karbar ta daga hannun Baffa Mudi kamar yanda Mahaifiyar sa ta bar masa wasiyya, na biyu kuma shi ne Zainab, ya yi alkawarin sai ta yi da na sanin zama silar rashin sake ganawa da mahaifiyar sa har abada, zai iya yafe komai amma ban da wannan.

Washegari tun kafin Usman ya je in da Baffa Mudi ya kafa fadansa dattawan Ruga su ka tada bukatar Baffa Mudi ya bawa mai mulki mulkin sa, dama ya kan yi ikirarin rashin Magajin Shehu ya sanya shi zama kan mulkin, toh Allah ya dawo da magajin Shehu.

Nan fa Baffa Mudi yayi kyememe ya ce be san zance ba, mulki ya rigada ya koma gidan sa, saboda haka be da wani magaji da ya wuce Tanko, in Sha Allah kuwa ko bayan ya mutu Tanko ne mai gadon Rugar Shehu. Nan fa aka hau kace na ce, masu goyan bayan Baffa Mudi na yi, haka kuma masu rantsewa sai ya sauka ba su fasa ba, ana cikin wannan yanayi ne Usman ya karaso.

Ganin sa gaban Baffa Mudi yayi mummunar faduwar, ga shi dai Usman din da ya sani ne, haka kuma tufar jikin sa ba ta sauya ba, rigar saki nan dai da kowa ke sakawa ne jikin sa, Amma wani irin cika ido da kwarjinin da Allah ya wa Usman sai ya zamewa Baffa Mudi tamkar Dodo, dan kuwa yanda ya ke shakkar Usman be ji shakkar Maihaifin Usman marigayiya Shehu ba. Usman be fasa gaishe shi cike da ladabi ba a matsayin sa na kanin mahaifin sa ba. Ba komai ne ya dagawa Baffa Mudi hankali ba sai jin furucin Usman na

"Baffa abubuwa da dama sun faru, wanda mun sani, ka sani, ka kuma san mun sani, wanda tonasu na nufin zubewar darajar ka a Rugar Shehu na har abada, haka ba ya cikin abin da na tanadar ma ka....."

"Zancen banza zancen hofi!"

Baffa Mudi ya katse Usman cike da burin kunya, be gushe ba ya cigaba da fadin

" Kai Usman ni za ka zo ka nunawa bude idanu? Wai kai na birni idon ka ya bude ko? Nan ba kafa ka sa ka tsallake Rugar Shehun ba? Sai da ka ji labarin mun fara samin cigaba, shugaban kasa ya ce zai tallafawa fulani ta hanyar gina mana Ruga mai inganci, da asibitoci, da makarantu da kayan more rayuwa shi ne za ka wanko kafa ka dawo ko? Toh ko uban ka Tanko be isa ba....."

"Baffa Mudi!!!!"

Usman ya daka masa tsawar da sai da ya sha ruwan jikin sa, a fusace Usman ya ce

"Kada ka yarda ka bari na take dan guntun girman da na ke ba ka! Mulki! Taimakon shugaban kasa da koma menene baya gaba na, cigabar Rugar Shehu shi ne gaba na..."

Ya tashi tsaye ya na mai duban dattawa da Kuma yan gari da ganin Usman ya sa su karasawa fadar Shehu. Cikin bada umarni Usman ya ce

"Ni Usman magajin Shehu ina mai sanar mu ku cewa ba na zo ne dan karbi sarautar Rugar Shehu ba, na zo ne ganin Iya ta, wacce Allah yayi ba za mu gana ba, duk da haka ba zan iya kau da kai daga gare ku ba bayan shekaru da dama, haka kuma ba zan ce kada ku bi Baffa Mudi ba, Amma ku sani ba a sarki biyu, dan haka idan har kuna so na kasance Shugaba gare ku sai mun canza sheka, ina mai umartar duk wanda ya ga zai iya zama karkashin jagoranci na da ya hade na shi ya nashi, kwanku da kwarkwatar ku, lokacin da Rugar Shehu za ta bar falgore yayi, za mu tasarwa barin falgore rana ita yau"

"Saboda da kai ne wa? Ka juyawa Rugar ta ka baya shekara da shekaru rana a tsaka ka zo ka na wani kurari? Sai mu ga wanda zai bika ai!"

Cewar wani dattijo wanda ke zaune kusa da shi ya kara da

"rabu da shi ya maishe da mutane sakarkaru, mutumin da be damu da uwar sa ba ina zai damu da mu?"

Wani ya ara ya yafa.

"Mu na biye da kai Shehu Usman, kafar ka kafar mu har illa mashaAllah!"

Cewar matasa da wasu daga cikin dattawan wanda su ka yi na'am da batun Usman. Da wanan rudani fadar Rugar Shehu ta watse, in da na jikin Baffa Mudi ke goyan bayan Shehu Mudi, duk da dai hankalin fiye da rabin jama'ar Rugar ya fi karkata ga bin Shehu Usman.

****

Maiduguri kuwa shirye shiryen auran Halitta da Sudais ne ya kankama duk da daurin aure kawai za a yi su tare. A nan cikin wannan hidimar Hajja Kilish ta nemi bukatar a bawa maneman Zinaru da Kori damar fitowa, idan sun shirya a hada auren gaba daya. Hakan kuwa ake yi Allah ya sa aka dace wanda ke neman Zinaru a shirye ya ke, na Kori ne dai ya turo iyayen sa amma tare da bukatar a dan ba shi lokaci be gama shirin sa ba.

Ganin kiri kiri za a aurar da yan uwan na ta biyu ga mazaje na gani na fada ne ya hana Zainab sukuni. Haka ta saka su Anty Sauda gaba da kuka, ta dena cin abinci ta dena walwala cewar ta da ta zauna da auren Usman gwara ta rasa ran ta. Ammy kuwa ta ce ba ita kadai ta haifa ba, idan mutuwar ta ce alkhairi gare su toh Allah ya sa a tafi a sa'a.

Duniya ta yi mata zafi, cikin kwana uku kacal ta rame ta fara lalacewa. Ganin haka Anty Sauda ta yanke hukuncin daukar mataki, gidan Malam ta je, ta saka Ammy gaba tare da Zainab, ta ce lalle ta kira gidan Kano ta ce Usman ya zo Maiduguri ta na san ganin sa.

Ammy na girgiza kai ta ce

"Ah ah ba zan kira shi ba fa, toh na kira shi ma akan me? Na fa fada mu ku wallahi babu yawu na cikin lamarin auren Yakura, gwara ma ta hakura ta zauna da mijin ta...."

"Na gaji da yin wannan maganar da ke Aleesha! Taurin kai gare ki kamar mutanan farko! Toh tantabara! Tunda masoyin ki ya daura ke kuma ba ki rabawa ko? Toh bari ki ga mu yi mai gaba daya, ni nan zan kira shi kuma sakin yarinyar nan ne sai yayi!"

Ammy na mai zuba mata idanu Anty Sauda ta kira numbar wayar da Malam ya aje bangaran masu gadi, wayar na kara ba a dauka ba, ta na shirin katsewa aka daga tare da yin sallama.

"Sunana Hajiya Sauda daga gidan Malam nan Maiduguri, ina son magana da Usman Maigadin"

Cewar Hajiya Sauda cikin dakiya. Shiru ne ya biyo baya daga bisani ta aje wayar ta na mai fadin

"Toh madallah, ke Yakura ai sai ki kwanatar da hankalin ki, Almajiri dai ya hade kayan sa yayi gaba, abin da abokin aikin sa ya sheda min kenan!"

"Yanzu haka ya tafi be sake ni ba? Toh wallahi ko da wasa kar a kara danganta ni da shi! Kada a sake cewa ina da aure...."

"Idan kuma ba haka ba fa?"

Cewar Ammy cikin tsawa, ta na mai nuna ta da yatsa ta ce

"Sai me za ki yi? As far as I'm concern Yakura ke matar aure ce ko kin ki ko kin so!"
Kuka Yakura ta saka wanda hakan ya sanya Anty Sauda fadin

"Sai ki kashe ta ki huta, ko kuwa ki janyo ta gudu ta bi duniya ayi biyu babu. Ke dena kuka na ce dai kun kusa komawa makaranta?"

Cikin muryar kuka ta ce

"Registration ma mu ke, na fadawa Ammy ko kudin registration din ma ba ta ba ni ba"

"Kudin registration dai? Ai kuwa a dangin uwar ki ba matsiyaci! Ki zo gida na ki karba gobe zan baki kudin registration da ma na kashewa"

"Waya ta ma ta lalace Anty Sauda"

Cewar Zainab cike da shagwaba.

"Toh kar ki damu sai a siyi wata ai, ki duba duk wacce ki ke so I got your back. Haka kuma ki hade na ki ya na ki ki koma makaranta, idan ma kin so kar ki halarci daurin auren gidan nan babu lalle ba tilas!"

Jin abin nema ya samu Zainab ta share hawayen ta tare da yiwa Anty Sauda godiya dan kuwa sai a sannan ta dan ji sanyi cikin ran ta, ta fice ta bar Anty Sauda da Ammy su na musayar magana kan ta, har sai da ran Anty Sauda ya baci sosai, cikin fushi su ka yi sallama ta tafi.

***

Washagari da sassafe Zainab ta nufi gidan Anty Sauda, Nan ta yi karin kumallo. Anty Sauda ta ba ta kudi masu yawan gaske domin registration da na kashewa har da na siyan wayar sanan ta kai ta super market ta mata siyayya sosai irin wanda Dady ya ke mata duk sanda za ta koma makaranta. Hatta tiket din jirgi Anty Sauda ce ta siya, Ammy ta sa mata idanu kawai. Wayewar gari Anty Sauda ta zo ta tisa ta gaba, Hajja Kilishi na fadin ba za ta jira a yi auren yan uwan ta ba? Anty Sauda ta ce
"idan lokaci yayi ta dawo, ai ba wani abu ba ne"

Ta yiwa kowa sallama amma ban da Halitta wacce dama idan ba dole ba magana ba ta hada su. Anty Sauda ce ta kai ta Airport, sai da ta tabbatar jirgin su ya tashi sannan ta juya gida.

Haka ma da jirgin su ya sauka birnin Yola Anty Sauda ta kira ta shedawa, Sai Anty Sauda ce ta sheda ma Ammy diyar ta ta sauka lafiya, ta kuma koma makaranta. Ammy da har ranta ba ta jin dadin halin da Zainab ke ciki ba addua ta yi, Allah ya shirya mata ita, ya sa ta gama makarantar nan lafiya ko Allah ya sa ta dawo gida...


Read / Download AUREN SHEHU BOOK 2

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album