Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

MUTUWARE GIDAN GAWA Complete Hausa Novel Document by MUTUWARE GIDAN GAWA


MUTUWARE GIDAN GAWA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 22669



MUTUWARE GIDAN GAWA

Reading Time: 1 Hours

Added On: 05, Sep 2024

Author: Mrs Sadauki ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : FCWA

Author Phone : +22795045822

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 112.58 kb

File Type: txt

Views: 673+

Download: 553+

Last download: less than 1 second ago

Description/Story: [31/10 à 11:05] MRS SADAUKI 💫: *MUTUWARE ...*🧟‍♀️
GIDAN GAWA🧞‍♀️🌬️

Love
and
Horror story

```MRS SADAUKI💫✍🏻```

Dedicted to Ameera Adam


FCWA ☀️

_________________________


Ƙirƙiraren labari ne,ban yi shi don cin mutumci kowa ba.Duk wanda ya zo daidai da rayuwarsa to akasi aka samu.


1


#ƘASAR COTE D'IVOIRE
#Babbar asibitin Abengourou

A tsorace nake ƙara tushe kunnuwana ko zan samu sa'ar toshe ma'adanar sautina da ke zuƙo min wata murya mai cike da tashin hankali.Sai dai yaudarar kaina nake,domin kuwa toshe kunnen da na yi hakan bai canza zane ba .Na kai hannu da niyyar ɗaukar pilow ko shi Allah zai sa na dace,hasken ɗakin ne ya ɗauke ɗif wanda ya yi sanadiyar tsayawar na'urar da ke kore zafi.
Ƙaiƙayi na fara ji yayin da sauro da zafi suka ce salama alaikum,shegiyar muryar nan mai shegen naci sai ƙara ƙaimi take wurin roƙon abin da ban san mi take so ba “ku cece ni ! Ku cece ni don Allah babu kowa ne?”
Na ja tsuki bisanin na lalubo wayata na kunna fitila,duk abokan aikina baccinsu kawai suke a gajiye.Na miƙe tare da nufar ƙofa,na murɗa handle na fito ,ga mamakina ko ina na asibitin akwai hasken wuta sai ɗakinmu da kuma wani ɗakin da ke can gabashi wanda akwai ƴar tazara tsakani.
Haka kawai na ji zuciyata na tunzura ni kan na je na duba tako ɗaya ,biyu,ina daɗa matsawa ina kuma daɗa jin sautin muryar nan mai neman taimako har na isa bakin ƙofar daidai nan hasken ɗakin ya dawo.Na kutsa kai,sai na tarar da nurse biyu da wani Dr a tsaye kan wata matashiyar budurwa ,gefe kuma wata jemamiyar tsohuwa ce zaune ta na kaɗa ƙafa.
Duk kallonsu ya dawo kaina,ni ma su nake kallo ɗin.
“Ayodele mi kike yi a nan? Babu aiki ne ɓangaren ku?” Dr ya tambaye ni,na buɗa baki da niyyar yin magana na tsinkayo wata murya kuma na ce min “Ayodele please ki taimaka min ban mutu ba!”
Inda sautin ya fito na duba,sai yanzu na lura da idon budurwar rufe suke ruf kamar mai yin bacci.Da mamaki nake tambayar kaina ‘dama mai bacci ya na iya yin magana?’
“Ta rasu ne! Ƙoƙarin cire duk abubuwan da ke jikinta ne muke amma sun ƙi fita” Dr ya katse min tunani.
“Amma yanzun nan fa ta min magana akan na taimaketa ba ta mutu ba” na faɗa .
Duk kallon mamaki suka bi ni da shi,hakan yasa na ci gaba da cewa “tun ɗazu fa ita ta hana ni bacci kururuwar ta ce ta tashe ni”
“Ayodeleee?” Dr ya kira ni da wani sauti,bisanin ya tambayi nurse ɗin “ku tun ɗazu da muke nan kun ji kururuwar ne?” duk kai suka girgiza alamun a'a.
Sai ya maido kallonsa gare ni “to kin ji ta yiyu kunnuwanki ne ba su jiye miki daidai ba”
“Mi sunanta?” ita ce tambayar da na yi,“Emeka” ɗaya daga cikin nurse ɗin ta ban amsa.
A hankali na fara taka ƙafata sai dai kafin na isa ga Emekar tsohuwar nan ta taso tare da tsaya wa a gabana “ina za ki je? Mi za ki yi?” ta jero min tambayoyi haɗi da jifata da wani mugun kallo mai ratsa ɓargo da tsoka don sam bai da daɗi.
Dakyar na fizgo numfashi tare da jarumtar kallonta cikin tsakiyar ido ,kawai sai na ga mugun razani a nata idon tare kuma da saurin ja ta bani wuri ba tare da na san dalilin yin haka ba.
Kai ga Emeka na yi tsaye bisanin na kai hannu kan fuskarta na ce “Emeka ?”
“Ayodele ta fa mutu,ya kike yi wa matatta magana kamar zautatta?” Dr ya tari numfashina.Ba tare da na dube shi ba na ce “ba ta mutu ba Dr ! Doguwar suma aka sa ta”
“Wa ya sa ta doguwar suma? Nan fa asibiti ce kuma mun san aikinmu ”
“Dr ita wacce ta saka ta suman ta san kan ta! Ina iyayenta suke?” na tambaya.
“Daga ita sai Kakarta suka zo,kuma ga ta can ta fita” cewar nurse.
Na ɗago kaina sai na ga tuni tsohuwar nan ba ta nan,wato abin da na fahimta ita ce Kakar Emeka.



“Ayodele ki taimaka ki damƙa ni ga iyayena Kakata ba ta sona shi ne take son kashe ni,ta ɓoye ruhina cikin asusun ƙarfe ta lashi takobi ba za ta fiddo shi ba har abada” shiru na yi ina sauraren esprit ɗin Emeka da ke yi min magana ba tare da ni kaina na san shi ne ba.
“Dr yanzu ma ba ga shi ta na yin magana ba?”

“Mtsw! Ayodele fita! Fita na ce !” Dr ya yi min wata muguwar tsawa.
Tako ɗaya na yi na tsaya,cikin fushi ya kuma cewa “kenan ba za ki fita ɗin ba?”
Murya a raunane na ce “ba ka ga ta riƙe min hannu ba ne?”
Duk ido suka waro Dr har da ɗora hannu a kai ya ce “wai Ayodele haukata ni kike son yi? Ku kun ga ta riƙe ta?” ya tambayi nurse suka girgiza kai.

Da mamaki nake kallonsu bisanin na mayar da dubana ga Emeka wacce ta riƙe ni gam ta na girgiza kai idonta na shatatar da hawaye.
“Ke kaɗai ke jin abin da nake cewa da kuma ganin abin da nake don Allah kar ki biye su” cewar Emeka .
Cikin jin haushi Dr ya fizgo hannuna da niyyar fitar da ni da ƙarfin tsiya sai dai sam ya kasa sakamakon ɗayan hannun da ke riƙe da Emeka .
“Dr ni fa na fara jin tsoro! Ina ga fa gaskiya ne! Dubi yadda hannunta ke jone kamar a rinƙe shi ɗin kuma ....kuma gadon kamar ya na motsa wa” nurse ta faɗa.

Dr ya sake min hannu,ya ce “ba zan yi mamaki ba don Abeno cike take da ƴaƴan matsafa da Mayu....” bai rufe bakinsa ba Emeka ta fara shaƙuwa,da sauri duk suka nufeta tare da saita na'urar aiki a kanta.


Ni kuwa ganin numfashinta ya dawo kawai sai na sulale na koma can ɓangaren mu.Kasa bacci na yi sai zaune da na yi na rabka uban tagumi ina tunanin abin da ya faru.Gadon bayana ne ya fara yin ƙaiƙayi,tare kuma da wata irin tsira wa tamkar ana nitsa wasu abubuwa gefe da gefen kafaɗuna.
Dishi-dishi idona ya fara,ban san ya aka yi ba na tsinci kaina a wata duniya wacce na fi kyautata zaton ta mafarki ce.


Wani ƙaton gida mai ɗauke da ɗakuna kashi-kashi,ruhina ya sallama.Babu wanda ya amsa min haka ba wanda ya ɗago ya dube ni sai tsohuwa wacce tun farkon shigowata na ji yaran gidan na ambaton sunanta da “Yaba”

Mugun kallon nan mai cike da hassada,ƙyashi haɗi da baƙin ciki ta jefo min bisanin ta miƙe tsaye ta zo gare ni.“Mi kike so kuma yanzu?”
“Abin da kika ɓoye!” na bata amsa.
“Maganar ahali ce wannan bai shafe ki ba,kin dai yi naki ikon don haka ki....” ban bari ta dire ba na tari numfashinta da “ki bani cikin lumana ko kuma na ƙwata ta ƙarfin tsiya! Yin haka kuma babba asara ce gare ki domin duk abin da kika ɓoye zan fito da su ne”
Tsoro ne na gani shimfiɗe ƙarara a fuskar Yaba,bisanin ta yi gaba ni kuma na take mata baya har cikin ɗakinta na laka wanda aka yi ma rufin kara.
Ƙarƙashin gado ta duƙa ta fito da wani asusun ƙarfe tare da miƙo min shi,ban ɗauki lokaci ba wurin buɗe shi.Baƙin hayaƙi ya fito kamar fitar iska ya tashi sama,guntun ƙyallen atamfa na gani sai na ɗauke shi bisanin na aje asusun na fito.


Daidai nan kuma na farka daga baccina,na dafe gefen goshina da yake sara min bisanin na buɗe idona taram .Da sauri na tashi ganin Emeka a tsaye ta na min murmushi.
“Na gode sosai Ayodele,kin ceci rayuwata!” ta faɗa tare da ƙoƙarin karɓa wani abu daga hannuna da nake jin na jimƙe ba tare da na san mine ne ba sai da na kai dubana sai na ga ƙiren atamfar da na yi mafarki ne.
Emeka ta ci gaba da cewa “wannan zanen ankon bikina ce,Inna Yaba ta yi amfani da shi don kashe ni saboda kawai zan auri bare wanda ba cikin danginmu ba.Na gode!” ta na gama faɗar haka ta fice ta bar ni sake da baki ina tunanin kar dai ace mafarkin da na yi gaskiya ne? ??????






MRS SADAUKI ce🌬️
[31/10 à 11:05] MRS SADAUKI 💫: *MUTUWARE ...*🧟‍♀️
GIDAN GAWA🧞‍♀️🌬️

Love
and

Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download MUTUWARE GIDAN GAWA

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album