Join Our WhatsApp Group

BUSA A MUTU Book 7 Complete Hausa Novel Document by BUSA A MUTU Book 7


BUSA A MUTU Book 7

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 17063



BUSA A MUTU Book 7

Reading Time: 1 Hours

Added On: 29, Feb 2024

Author: Abdulaziz Sani Madakin Gini ,

Ebook Compiler : Al'amin ahmed Misau, Shuraihu Usman

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Adventure novels

File Size: 90.58 kb

File Type: txt

Views: 613+

Download: 295+

Last download: 2 days ago

Description/Story: BUSA A MUTU 💕
Littafi Na Bakwai (7)🩸
Part A💎
Na Abdulaziz Sani M Gini 🤴
Typing by AA Misau ke Magana
✍️⭐⭐⭐
(ALKAWARIN MU NA NAN DANI DAKU IN KUN LATSA MANA LIKES & COMMENTS KUNA ZUCIYATA 🎧🎤🎷🤓🤓🤓)
Labari Ya Isowa Shagala Cewa...
DA JARUMI IMRAN DA JARUMI MURAISU DA
SU MAHAIFIYARSA HUSNAILA SUKA SHAFE SAMA DA
SA'A UKU SUNA FAFATA YAKI, AMMA DAYANSU BAI
SAMI NASARAR KODA KWARAZANAR JIKIN DAYA BA.
Al'amarin da ya fusata kOwanncnsu ke nan. Da kansu
suka ja da baya, suka yi cirko-cirko suna haki da kallon
juna.
Kawai sai jarumi Imran ya mai da takobinsa cikin
kufe yai jifa da ita, sannan ya dubi Muraisu da Husnaila ya
ce, "Tun da dai iya yakinmu ya zo daya me zai hana mu
jarraba amfani da tsagwaron karfin dantsen mu amma bisa
sharadi guda,"
Cikin alamun fishi da mamnaki jarumi Muraisu ya ce,
"Wanne irin sharadi ke nan kake nufi?"
Jarumi Imran ya ce, "Sharadin shi ne, idan na sami
sarar kaiku kas za ku janye dukkan nufinku ku kar6i
addinina. Idan kuma ku ka sami nasara a kaina zan kyaleku
ku ci gaba da yin abinda kuka sa a gabanku. Na yi haka ne
domin na kawo karshen gardamar da ke tsakaninmu".
Koda jin wannan batu sai jarumi Muraisu da
mahaifiyarsa Husnaila suka dubi junansu sannan suka
koma gefe daya domin su yi shawara.
Muraisu ya dubi Husnaila ya ce, "Ya ke Ummina
yanzu ke a ganinki mene ne abinda ya kamata mu yi?"
Koda jin wannan tambaya sai Husnaila ta sunkui da
janta kas tana tunanı har 1zuwa tsaWon 'yan
dakiku, daga can sai ta dago kai ta dubi Muraisu cikin
alamun tsananin damuwa ta ce, "Ya kai dana, ka yi sani
cewa da dadewa tun ina yarinya Karama na taba ji daga
bakin mahaifina cewar ma'abota addinin Musulunci suna
da matukar sa'a da nasara bisa duk abinda suka sa a
gabansu.
Tabbas Biri ya yi kama da Mutum, tunda gashi mun
gani a zahiri, ta yadda mu biyu muka kasa samun nasara
akan wannan bakon jarumi duk da mun hada KARFI DA
KARFE ni da kai.
Ni ina ganin cewar zamanmu a cikin wannan daji na
Kirzufa yanzu ya kare, domin na fuskanci cewa sihirin da
ke cikinsa ya daina aiki tunda gashi KAHONKA na BUSA
A MUTU ya daina BUSUWA.
Kuma ga dukkan alamu wannan jarumi da ya z0 sai
ya fita daga cikin dajin nan lafiya kuma a raye, ka ga ke
sihirin dajin ya karye tunda a ka'ida duk mahalukin da
ya shigo bai isa ya fita a raye ba.
Yanzu idan har muna son wannan KAHO na BUSA
A MUTU ya sake BUSUWA, dole ne mu nemo wannan
Gashin SIHIRI wanda dan uwana Sarki Imras ya Boye
domin bisa binciken da na yi, na gano cevwa da wannan
gashi ne kadai zamu iya dawo da karfin sihirin kahon
BUSAA MUTU da kuma sihirin wannan daji na
KIRZUFA.
Ka ga ke nan yanzu zamanmu anan cikin dajin
Kirzufa bashi da wani amfani, dole ne mu fice daga cikinsa
mu tafi neman GASHIN SIHIRIN.
Sabo da haka, yanzu dole ne mu janye yaki da
Wannan bakon jarumi tunda ba shi bane
abokin gabarmu ba, ko addininsa gaskiya ne ko karya ne ba
ta tashi mu ke yi ba.
Dole ne mu san hanyar da zamu bi yanzu mu gujewa
wannan bakon saurayi da abokan tafiyarsa".
Cikin alamun tsananin damuwa Muraisu ya dubi
mahaifiyarsa Husnaila ya ce, "To yanzu wacce dabara
zamu yi mu gujewa wannan bakon jarumi?"
Husnaila ta yi murmushi ta ce, "Kar ka damu, zo mu
je mu yi magana da shi".
Nan take Muraisu da Husnaila suka koma inda jarumi
Imran da su jaruma Suzaila ke tsaye suna saurarensu.
Da zuwansu sai Husnaila ta dubi Imran ta ce, "Ya kai
wannan GWARZON MAYAKI, ka yi sani cewa mu yanzu
amince zamu bayar da gaskiya ga addininka, amma
sai idan mun zauna tare da kai mun yi maka wadansu 'yan
jarrabobi da za su tabbatar mana da gaskiyarka da
addininka.
Yanzu za mu je mu debo 'yan kayayyakinmu mu biku
mu tafi mu bar dajin nan gaba daya har abada ba zamu
dawo ba.
Amma ka sani cewa Sarki Imras da Sarki Huraisu su
ne manyan abokan gabarmu wadanda in dai zamu hadu da
su babu abinda zai rabamu da su face KAIFIN TAKOBI!
Don haka, kada ka kaimu izuwa garuruwansu".
Koda jin wannan batu sai jarumi Imran ya dubi
Husnaila cikin alamun damuwa ya ce, "Ya ke wannan 'yar
Sarki, ki yi sani cewa koda zamu hadu da su Sarki Imras ba
Zan bari su cutar da ku ba, wannan alkawari ne tsakanina
da ku.
AA Misau ke Magana
Ku sani cewa ni ina s0 ne na yi sulhu a tsakaninku
domin an riga an yi kuskure tun a baya, tunda dai akwai
nasaba ta jini a tsakaninku, ya kamata a yafi juna".
Koda jin haka sai hawaye ya zubowa jarumi Muraisu
ya ce, "Ta ya ya kake tsammanin zan iya yafewa Sarki
Huraisu wanda ya kashe mahaifina, ya jefa mahaifiyata a
cikin rayuwar kunci da wahala, rayuwar daji inda babu
abinci da abin sha mai dadi, kuma babu makwanci mai
kyau, alhalin ada ta saba da rayuwa mai dadi?
Kamar yadda nima ba zan iya yafewa Sarki Huraisu
ba, haka ma mahaifiyata ba za ta iya yafewa Sarki Imras
ba, tunda ya so ya lalata rayuwarta ya hanata yin aure da
haihuwa, kuma gashi da shi aka hada kai aka kashe mijinta.
Ka yi sani cewa tun dazu mahailiyata ta yi bincike ta
gano cewa Sarki Imras da Sarki Huraisu sun yi gagarumin
shiri sun taho izuwa nan dajin Kirzufa bisa kan wani aljani
domin su hallakamu. Yanzu mene ne abin yi?"
Koda jin wannan tambaya sai jarumi Imran ya sunkui
da kansa Kas ya yi dan guntun tunani sannan ya dago kai
va ce, "Yanzu abinda za a yi, akwai wani Kauye wanda
muka ci su da yaki muka kafa addinina a cikinsa, zamu je
can mu zauna tare da ku a can. Amma ina son ka gaya mini
iva tsawon kwanakin da za ku yi ku gama jarrabani don
tabbatar da gaskiyata da adalcina".
Koda jin haka sai jarumi Huraisu da mahaifiyarsa
Husnaila suka dubi juna, sannan Husnaila ta ce, "Muna son
ka barnu kwana ashirin da daya kawai."
Koda jin haka sai jarumi Imran ya gyada kai ya ce,
"Shi ke nan, kamar yadda kuka yi shawara kai da
mahaifiyarka nima akwai bukatar na je na yi
shawara da Lushaira, saboda ta zama tamkar 'yar uwata ta
jini yanzu tunda ta karbi addinina".
Gama fadin hakan ke da wuya sai jarumi Imran ya
juya ya koma inda su Husnaila ke tsaye , wato in da ya
shata musu layi ya ce kada su kuskura su ketara.
Da zuwansa sai ya dubi Lushaira ya ce, "Ya ke 'yar
uwata matso kusa da ni donin mu yi shawara a matsayinki
na 'yar uwata musulma".
Koda jin wannan batu sai jaruma Suzaila taji ta kamu
da tsananin kishi, ta jìi kamar ta hana Lushaira zuwa wajen
Imran, amma sai ta kanne.
Ba tare da 6ata wani lokaci ba Lushaira ta tako
Kafafunta ta gota wannan layi wanda jarumi Imran ya shata
musu, ta z0 daf da shi ta tsaya yadda har suna iya jin
numfashin juna.
Al'amarin da ya kara tunzura Suzaila ke nan, jikinta
ya kama tsuma. Ita kanta sai taji tana mamakin kanta, na
vadda take jin tsananin kishi akan mutumin da bai san ma
tana sOnsa ba.
Nan take Imran ya kwashe labarin duk abinda suka
tattauna shi da su jarumi Muraisu ya zaiyanewa Lushaira.
Kuma ya nemi shawararta bisa abinda take ganin zai
fishshesu".
Koda jin haka sai Lushaira tayi dan shiru tana nazari.
Daga can sai ta fago kai ta dubi Imran ta ce, "Ka amince
da wannan sharadi da suka zo da shi.
Amma fa dole ne mu zuba ido sOsai akansu domin
alkawarin duk mutunin da bai addinin Musulunci ba,
alkawari ne mara tabbas.
Ka sani cewa wadannan mutanc za su iya yaudararmu
su gudu su karya alkawarin da ke tsakaninmu.
Abu na biyu kuma, dole ne mu kula da alakarsu da su
jaruma Suzaila da tamu ni da dan uwana Husnalu, saboda
za su iya huce haushinsu akanmu.
Ma'ana za su iya kokarin hallaka Suzaila a matsayinta
na 'yar Sarki Huraisu ko kuma su yi yunkurin hallakamu ni
da Husnalu a matsayinmu na 'ya'yan Sarki Imras, domin su
đauki fansa."
Sa'adda jarumi Imran yaji wannan batu sai ya jinjina
kai ya ce, "Kada ki damu za mnu sa ido sosai akansu ni dai
kawai fatana shi ne Allah Ya sa su gane gaskiya kuma su
karbcta.
Koda gama fadin hakan sai ya koma wajen su jarumi
Muraisu ya ce, "Na gama shawara da 'yar uwata kuma na
amincc da sharadin da ku ka zo mini da su. Don haka sai
ku je ku dcbo kayanku ku zo mu tafi".
Cikin farin ciki jarumi Muraisu da Husnaila suka juya
da sauri suka nausa izuwa cikin dajin Kirzufa.
A kan hanyarsu ne Muraisu ya dubi Husnaila cikin
alanun tsananin damuwa ya cc, "Haba ya ke Ummina ya
ya ke da muka gama magana akan cewa guduwa zammu yi
amma kuma yanzu kı ka sauya magana kika ce zama za mu
yi tare da su? Ta ya ya ke nan za mu sami nasarar ganin
bay an wadannan abokan gaba namu idan jarumi Imran ya
sami nasarar yin sulhu tsakaninmu da su?"
Koda jin wannan tambaya sai Husnaila te yi
murmushi ta ce, "Ya kai dana kai yaro ne har yanzu baka
san cewa yaki dan zamba banc.
Tunani na yi na ga cewa idan ma muka gudun ba za
mu cimma nasara ba bisa bukatarmu. Idan kana son ka ga
bayan makiyinka dole ne ka kusanceshi ka san sirrinsa
tukunna, ta haka ne za ka sami lagonsa ka kawar da shi
cikin ruwan sanyi.
Tunda dai zamu zauna tare da su Husnaila a Kauyen
da zamu je har tsawon sati uku, ka yi kokari ka sace
zuciyarta ta fada cikin tarkon sonka ta kowacce hanya.
Kana da kyau, kuma ka ga jarumi na gaske,
wadannan abubuwa biyu da kake da su yana matukar jan
hankalin 'ya mace
Sai ka yi amfani da wannan dama ka dinga dukan
cikin Husnaila har ta sanar da kai inda mahaifinta ya boye
kwalbar da ya sanya wannan GASHIN SIHIRI.
Da zarar ka sami nasarar hakan sai mu sulale mu
gudu mu bar Kauyen da zamu je domin tafiya neman
gashin sihiri. Da zarar mun mallaki wannan gashi zamu iya
hallaka Sarki Huraisu da Sarki mras cikin sauki tamkar
cire silin gashi a cikin tandun mai.
Nan dai suka garzaya cikin sauri suka dcbo
kayayyakinsu a cikin kogon dutsen da suke kwana.
Muraisu ya dauko kahonsa na BUSA A MUTU ya
ratayashi a bayansa.
Koda suka fito daga cikin kogon dutsen rike da 'yan
kayayyakinsu sai suka ga gaba dayan dabbobin dajin sun
taru a waje daya sun kura musu idanu sun yi zugum-
Zugum.
Kai da gani ka san cewa dabbobin suna cikin
tsananin bakin ciki da alhini na rabuwa saboda sun
fuskanci cewar ranar rabuwa ce ta z0 alhalin
AA Misau ke Magana
an yi sabo da juna tsawon shekara da shekaru.
Nan take zuciyar Muraisu da Husnaila ta karaya, har
idanunsu suka ciko da kwallah suka kama zubar da
hawaye.
Wasu daga cikin dabbobin sai suka taho wajensu
suna kwanciya a jikınsu suma suna rungumesu suna shafar
jikinsu.
Kawai sai Muraisu ya fashe da kuka yana cewa , "Ku
Yi hakuri ya ku abokan zama zarmu rabu yanzu, amma zan
dawo gareku nan ba da dadewa ba."
Nan dai Muraisu da Husnaila suka yiwa dabbobin
dajin bankwana suna kuka suka juya suka koma inda su
jarumi Imran suke.
Nan dai suka dunguma gaba dayansu suka fice daga
cikin dajin Kirzufa suka durfafi hanyar da za ta kaisu
wannan Kauye wanda suka yi niyyar zuwa domin a zauna
tsawon sati uku kamar yadda aka yi alkawari.
fitarsu:
dajin.
daga cikin dajin ke da wuya
kamar da tsawon rabin sa'a sai ga
su Sarki Imras sun sauka a bakin dajin
Saukaisu ke da wuya sai suka sauko daga kan aljanin,
Sannan Sarki huraisu ya dauk0 madubin tsafinsa ya
shafeshi da hannun hagu.
Koda
takarkare
ya gama ganin abinda yake son gani sai ya
Takarkare ya kwarara uban ihu cikin tsananin bakin ciki,
har kwallar takaici ta ciko masa idanu.
Cikin firgici Sarki Imras ya dubeshi ya ce "Ya kai
abokina me ka yani ne a cikin wannan bincike naka? Shin
ba za mu iya shiga cikin wannan daji bane?"
Sarki Huraisu yai ajiyar zuciya ya ce "Ai wannan
bakon jarumi ma'abocin addinin Musulunci ya ruguza
mana shirinmu gaba daya.
A yanzu haka ya daukc jarumi Muraisu da 'yar uwata
Husnaila ya tafi da su izuwa can wanı Kauye inda za Su
7auna tsawon kwana ashirin da uku.
Babban tashin hankalina shi ne wannan ne kadai
lokacin da za mu iya amfani da shi mu ga bayan Muraisu
da mahaifiyarsa amma idan muka bari har suka karbi
wannan sabon addini, to fa ba zamu iya ganin karshensu
ba.
Ni yanzu ma kaina ya daure, ban san ma abinda zamu
yi ba. Idan muka ce zamu bi bayansu a yanzu ba zamu iya
yin komai ba don jarumi Imran ba zai bari mu taba su ba".
Koda jin haka sai Sarki Imras yai ajiyar zuciya kuma
yai tunani na tsawon 'yan dakiku, sannan ya dubi Sarki
lHuraisu ya ce, "Ya kai abokina, ka kwantar da hankalinka
ka sani cewa hanyar kashc makahon Kare yawa gareta.
Yanzu abinda zamu yi shi ne mu koma can kasarka
nu zauna akwai dabarar da nake so mu yi".
Sarki Huraisu ya jinjina ya ce "Me zai hana ka gaya
mini dabarar da kake da ita yanzu?"
Sarki Imras ya ce, "Ai shirin zaune ya fi na tsaye".
Koda jin hakan sai Sarki Huraisu ya koma kan aljani
ya zauna, shima Sarki Huraisu sai yą hau, nan take aljani
ya bude fuka-fukansa ya tashi da su sama ya nufi hanyar da
za ta kaisu Birnin Hutaira.
Kallo daya za ka yiwa sarakan biyu ka fahimci cewar
suna cikin tsananin tashin hankali da bakin ciki.
su jarumi Imran kuwa,
lokacin da suka iso
Kauye sai
Wannan
mutanen Kauyen suka karbosu hannu biyu cikin tsananin
farin ciki, saboda basu taba tsammanin cewa za su sake
ganinsu ba.
Shugaban mutanen Kauyen ne ya zo da kansa ya
shigar da su har cikin farfajiyar gidansa aka kawo musu
abinci da abin sha suka kimtsa.
Bayan sun nutsu sai jarumi Imran ya dubi shugaban
Kauyen ya zaiyane masa abinda ya kawo su, sannan ya
tambayeshi ya ce, "Mencle ne abinda ya fi kawo muku arziki
a wannan Kauye?"
Da jin wannan ambayà sai shugaban Kauyen ya yi
murmushi ya ce, "Ya shugabana babu abinda yake kawo
mana kudi sama da cinikin fatocin dabbobi da kuma harkar
su (kamun kifi) saboda muna da wani babban kogi da ke
can karshen gari, har ta kai cewa baki daga hauren
kauyuka da birane sun fara zuwa suna siyayya.
Kwatsam! Sai wata matsala ta taso mana wacce ta
firgita bakin suka daina zuwa.
Matsalar dai guda biyu ce. Matsala ta farko ita ce;
Dajin da muke zuwa farauta yanzu ya gagaremu shiga
Saboda wadansu mugayen dabbobi uku_da suka wanzu a
cikinsa suka hana shiga,
Dabba ta farko, wani rikakken Zaki ne mai tsananin
Karfi, girma da sihirin da komai yawan mafarauta sai ya
tarwatsasu.
Sau bakwai ana yin taron manyan mafarauta masu
takama da kansu suna shiga cikin dajin domin su kashe
wannan Zaki amma dayansu baya dawowa a raye.
Mafarautar sun canfa fatar Zakin da cewa duk wanda
ya dinka sutura da ita ya sanya a jikinsa, to babu wata
dabba da za ta iya gumurzu da shi komai girman ta da
karfinta.
Dabba ta biyu kuwa, wata narkckiyar Macijiya ce da
ke yammacin dajin wacce makami baya tas iri a jikinta,
kuma tsawonta ya kai kamu dari uku da sittin, haka ma
Ko dutse ta kewaye komai girmansa idan ta matseshi
sai dai ka ga yana rugurgujewa.
Itama wannan Macijiya sau uku ana jarraba kasheta
amma abu ya gagara. Har gudunmawar Dakarun Yaki
muka nemo daga manyan birane uku amma duk a banza.
Dabba ta uku kuwa, wata Doddanniya ce wacce ke
zaunc a arewacin dajin.
Ita dai wannan Dodanniya tana da hannaye guda
goma sha biyu, shida a hagu, shida a dama. Hannayen na ta
suna da...


Read / Download BUSA A MUTU Book 7

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

1 Comments On BUSA A MUTU Book 7
avatar
walid

1 month ago

Reply

Is so sweet

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album