Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

KURMAN BAKI Complete Hausa Novel Document by KURMAN BAKI


KURMAN BAKI

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 23474



KURMAN BAKI

Reading Time: 1 Hours

Added On: 20, Jan 2025

Author: Safiyya Abdullahi Huguma ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : zafafa biyar

Author Phone : 08038258489

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 129.62 kb

File Type: txt

Views: 218+

Download: 130+

Last download: 1 day ago

Description/Story: https://chat.whatsapp.com/LP1fwEwAkejETakHaD59VO


*_Bismillahir rahmanir rahim_*

*_KURMAN BAK'I_*

*H U G U M A*

PAGE 01


_Akwai saqonni masu tarin yawa a ciki,saidai kuma KURMAN BAQI ne me wuyar fassaruwa,ga duk me nisan zangon hankali da tunani zai tsinkayi hakan,DAN JAGORA NE ga mata,musamman masu KISHIYA,kuma hannunka me sanda ne ga masu sana'a data shafi labarin dake cikin littafin_

*NOTE:qirqirarren labari ne wanda ya dace da matsalolin da mata ke fuskanta a yanzu,komai dake ciki qirqirarre ne,idan ya dace da zahirin rayuwar wata to arashi aka samu*


Zaune take zaman farar stool din dake ajjiye gaban dressing table din dakin. K'afarta daya kan daya tana kuma karkadasu da wani irin sauri. Kallo daya tak zaka yiwa fuskarta ka fahimci akwai zallar bacin rai mai mugun yawa shinfide a saman fuskarta,bacin ran da ko shakka babu yana yiwa zuciyarta wani irin fusga da kud'a me ciwo.

Hatta da launin idanunta zuwa fuskarta sun sauya,abinda zai alamta maka kuka tasha bana wasa ba,da alamu kuma ba wani lokaci me tsaho ta dauka da gama kukan ba.

Har cikin zuciyarta takejin wani irin masifa da tashin hankali suna sadakarta. Qoqari take tayi ta taushi zuciyarta amma kuma kamar hakan yana neman gagararta.

Ita din tana cikin jerin sahun matan da basu iya cinye fushi da bacin rai ba tare da zukatansu sun furta ko sun furzar da shi ga dukka wanda yayi silar afkwarsu a wannan yanayin ba.

"Idan ba damuwa don Allah zan dan fita yau din,amma bazan wuce awanni biyu ba zan dawo in sha Allah" Sautin muryar dake tashi sama sama ya ratso ta cikin windows dinta,ya kuma keta labulayenta ya isa ga kunnuwanta.

Isar sautin muryar kadai ga kunnuwanta amma sai taji kamar an sakar mata guduma cikin tsakiyar zuciyarta. Tana da muradin jin amsar da wanda akayi maganar dominsa zai bayar,wannan ya sanyata miqewa zumbur ta kuma kai ga labulen ta yaye a zafafe.

Fes take iya hango mutum biyun wanda ke magana cikin wata irin nutsuwa a tsakaninsu. Tsayayyen namiji ne wanda ke tafe da tsaho da kuma qibarsa gaba daya,wanda hakan ya bashi wani irin kyakkyawan murjajjen jiki da ya qara masa kyau da cikar zatin da kai tsaye ya isa ya amsa sunan NAMIJI. Duk kuwa da cewa shi din ba wani mugun kyakkyawa bane,amma sam sam bai hada koda hanya da kalmar MUNI BA. Baqi ne da bahaushe kan kira da wankan tarwada,wanda yayi wani irin kyau me cike da nutsuwa cikin wani lallausan yadi ruwan sararin samaniya a jikinsa. Ganinka na farko da shi zaka tabbatar da cewa shi din gwanine wajen iya murza hula da sanya sutura ta zauna a jikinsa,hakanan telansa ya qware qwarai da gaske gurin baiwa dinki haqqinsa,dukka wadannan abubuwa suna da cikin abubuwan da suka hadu suka qarawa SALEEM kwarjini da cikae kamala da kuma siffa.

Matar dake a gefansa kuwa duka duka shekarunta ba zasu haura ashirin da takwas ba,idan tayi nisa da yawa ashirin da Tara zuwa talatin. Ita dinma baqa ce kamarsa,saidai nata baqin har yafi nashi gogewa,chocolate color ce sosai,mai matsakaicin tsaho,ba gajeriya bace,saidai kuma bata kai tsahonsa ba sam sam. Tana da manyan idanu masu matsaikatan girma,hakanan hancinta yana da tsaho da tudu. Komai nata matsakaici ne,itama tana da wani kyau na daban,wanda baiyi yawa ba.

"Ina zuwa kenan?" Ya tambayeta yana duban fuskarta da murmushi ya subuce mata

"Gidan aunty khadija mana" kai ya jinjina yana murmushi

"A dawo lafiya Allah ya tsare" ya fada yana same fadada murmushinsa. Qaramar dariya ce ta qwace mata

"Da sauri haka?,saboda kaji gidan aunty deeja ne?" Ido ya fiddo yana sakin wani murmushin

"Ta yaya zan hanaki zuwa nan?,ai nasan ta samu ne" ya fadi qasa qasa. Siririyar dariyar da ta ajjiyeta musamman saboda shi ta saki,cikin salon nuna jin kunya tace

"Ni bance ba,amma dai sirri ne"

"I know,bance sai naji ba nima,Karki jima please" ya fada cikin tausasawa yana takawa zuwa muhallin ajiyar mota na gidan dake dauke da motoci gida uku kamar yadda iya adadin abinda zai iya dauka din kenan

"Nasan ba ka son yin dare a waje daddynsu,ba zan kuma saba ba in sha Allah" dakatawa yayi da tafiyar ya waiwayo yana dubanta. Wani murmushi ne saman fuskarsa wanda ya sani bai isa ya hanashi fita daga fuskar tasa ba. Tattausan murmushin itama ta saki sannan tadan rausaya kanta cikin alamun jin nauyin kallon da yake matan. Tamkar an saya hannu an finciko zuciyarta daga qirjinta haka ZAINAB taji. Taji na zata iya qara koda second daya a tsaye tana kallon wannan abun ba. Sai ta saki labulen da sauri ta kuma juya da sassarfa tana rufar qofa zuciyarta na sake soyewa da wani irin zafi da radadi.

Ya za'a yi mutumin da tun daren jiya ta rasa ganin walwala koda qanqani saman fuskarsa?,hatta da abincin darensa ma bai samu ci ba,ya kuma gaya mata baijin dadi ne a haka suka kwana amma shine yake rausaya da idanu da wani irin shu'umin kallo irin haka?. Bayan ko yau da safe a tsaitsaye ya shirya,ko fuskantarta suyi magana ya kasa yi,sai baya da ya juya mata,ya gama shirinsa a gaggauce ya fice?. Ta dauka ya jima da barin gidan ma,ashe yana tare da wannan makirar baqar matar tasa.

"Allah ya bada sa'a,ya tsare mana kai,ya baka ikon nemo halak ka ciyar damu da ita,a dawo lafiya" idanunsa ya lumshe kadan,addu'arta tana masa tasiri har tsakiyar zuciyarsa. Wanann addu'ar na cikin jerin abubuwan dake faranta zuciyarsa duk safiya,ta kuma yi masa rakiya har zuwa shagonsa na kasuwa.

Da fara'ar shimfide akan fuskarsa ya bude idanunsa yana motsa labbansa. Sai idanun nasa suka sauka akan zainab wadda ke tsaye tana numfarfashi nata idanun itama a kansa. Janye dubansa yayi daga kanta ya mayar ga RUQAYYA yana cewa

"Ameen ameen,na gode qwarai,Allah yayi albarka"

"Ameen" ta amsa masa tana shafa tafukan hannuwanta dukka biyun saman fuskarta,sannan tayi taku biyu taja baya daga kusa da zainab din,ba tare data dubeta ba saboda sanin cewa ko meye zata gani saman fuska da idanunta ba alkhairi bane,sai ta saka kai cikin gidan tana zarcewa sashenta.

"Har ka warke kenan?" Zainab ta jefa masa tambayar kai tsaye tana ci gaba da dubansa, tambayar da tazo da salo ma titsiye da kuma son qure mutum

"Dama ai ba ciwo nakeyi ba,nace dai miki bana jin dadi ne kawai,kuma kowa yana tsintar kansa a irin wannan yanayin"Ya fada yana janye dubansa daga kanta,baqinciki na lasar zuciyarsa. Ita sam kwata kwata ma kamar bata kishin kanta?,bata taba damuwa da ta sauya wasu abubuwa ba ko don ruqayya. Ruqayya din bata taba zamar mata abar kwatance ba,tafi bawa abu guda daya muhimmanci,sannan wannan abu dayan tafi bashi himma kima da darajar data zarce ace an bashi din.

"Kaji dai tsoron Allah kada ranar qiyama ka tashi da shanyayyen barin jiki wallahi.....koda yake ba laifinka bane,kaci ka sha,duk da shima asirin ai yana tadda hali ne" ta fada a zafafe sannan ta juya abinta tana komawa cikin gidan da sauri saurinta.

Bai dakata da kallonta ba har ta bacewa ganinsa,ya sauke numfashi mai nauyi ya zura key yana qoqarin bude motarsa yana girgiza kai hadi da jan wani qaramin tsaki. Ba abinda ke yawo a idanunsa sai rigar baccin jikinta wadda duk dalli dallin maiqo ne a jikinta,abinka da abu silk jirwaye da maiqo bashi da wuyar nunawa a tattare dashi. Iya tsaiwarta a wajen,qamshin jikin ruqayya ya baje ya koma inda ya fito,ba komai a wajen sai wani yanayi dake nuni da lokaci yayi da gangar jikin mutum ta fara buqatuwa zuwa ga wanka,wankan da yayi imanin koda za'a yishi to saifa idan ya dawo ko kuma yana dab da dawowa idan an tafka sa'a a ranar.

Zuciyarsa cike da qiyasce qiyasce da juya al'amuran zainab ya tashi motarsa sannan ya sulale ya fice a gidan yana son daidaita nutsuwarsa kota halin qaqa.

A nutse ta tura qofar parlor din nata da bata gama rufewa ba saboda tana sauri ta cimmasa ta gaya masa zata fita din a yau.
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download KURMAN BAKI

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album