Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

GIDAN MATI Complete Hausa Novel Document by GIDAN MATI


GIDAN MATI

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 13030



GIDAN MATI

Reading Time: 1 Hours

Added On: 08, Sep 2023

Author: Bongel Fulani ,Rufaida Omar ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 69.2 kb

File Type: txt

Views: 1425+

Download: 488+

Last download: 11 hours ago

Description/Story: GIDAN MATI
©BINGEL MITA & RUFAIDA OMAR
Hausaebooks
Shuraih Usman
http://shuraih.waphall.com


Buguzum-buguzum ta sanyo kai cikin gidan
tana wak'a.
"Ahayye iye nana..."
D'if ta dakata gami da sakin baki adalilin
abinda ta hango a tsakar gidannasu.
Maigidansu Mati a k'ofar d'akin kishiyarta
Abulle zaune su na hira da dariya. Ganinta
ya sanya Mati yin tsuru da idanu yayin da
ita kuwa Abulle ta washe baki, cike da
dabara ta fiddo takardar naman da ta 6oye
a bayanta ta warware ta d'auki tsoka d'ayan
da ya rage ta jefa a baki ta na tauna gami
da fad'in.
"Maigida kana burgeni, kana kawomin irin
wanda na ke so."
Mati ya watsamata kallon muguwar mace,
shaf a tunaninsa dagaske ta yarr da takardar
tsiren, ashe makirar abinda ta shiryamasa
kenan. Ya numfasa gami da share zufa ya na
duban Nene batare da ya ce uffan ba.
Nene wacce zuciyarta ta gama kaiwa bango
ta fisge mayafin kanta ta had'iye miyan da
ya taru a bakinta tsabar na ranta ya biya ta
ci d'amara ta hau tafa hannu.
"Allah na godemaKa da ka nunamin abinda
ke faruwa a bayan idona! Ashe daman cuta
ta ake yi ana dawowa idan bana nan? To yau
dubunku ta cika Mati, yau sai an bambance
tsakanin aya da tsak'uwa!"
Jin haka ya sanya Mati mik'ewa ya hau
fad'an k'arfin hali da borin kunya.
"Ke ya isa! Yimin shiru dak'ik'iya kawai! Kin
shigo gida ba sallama ba komai sai wak'en
banza sannan ba ki tsaya kin ji dalilin
dawowata ba yanzu kishi zai kaiki ya baro
ki!"
Kafin Nene ta samu bakin magana, Abulle
ta saki wata dariya irin ta wadanda duniya
ta yiwa dadi.
"Kai namiji, namiji akace buhun k'aya.
Sannunka munafuki, inace mun fi awanni
biyu tare? Duk dai abinda za'ayi sai dai a yi
don ba na tsoron kowace mai yanayin
kul6a, miji ne mun yi aurenmu na soyayya
muna zaune lafiya yana kawomin kayan
mak'ulashe koda kuwa ba kwana na ba, sai a
mutu!"
Da jin haka Nene ta zabura ta yi kanta ta na
faman surfa ruwan ashariya.
"Yau sai na nakasa ki tsohuwar bazawara
mai bin maza, saidai wannan tsohon gurgun
ya k'ara haifar wata."
Ai sai su ka shiga kokawa, Nene ta daddage
ta ba ta kyakkyawan cizo a mamanta wanda
ya ke fata ce kawai. Wani ihu Abulle ta saki
gami da fad'in.
"Kan uban can!" Ta cafki jan gashin kan
Nene mai kama da gemun ɗan Bunsuru ta
hau ja da k'arfi, ta kuwa shiga ihu har
zaninta na fad'uwa sai ga ta zirr babu ko
d'an bante. Mati ya tafi da gudu ya d'auki
zanin ya na kokarin suturceta ganin
magulmatan makwaftansu wato Gidan Delu
da Gidan Shafa har sun soma lek'e ta
Katanga.
"Menene haka? Ke Abulle don iyayenki
sakarta!"
Wani turi da Abulle ta yiwa Nene sai kuwa
ta jefata jikin Mati su ka yi kyakkyawan
zubewa a k'asa abinka da siririn mutum. Da
sauri Nene ta mik'e ta suturta jikinta ta na
huci.
"Shegiya mai kalar mayu zan yi maganinki a
gidannan, za ki san kin shigo gidan Nene."
Wani banzan harara Abulle ta watsamata
sa'ilin da ta ke gyara zaman rigarta.
"Yanzu aka fara tashin hankula a gidannan
muddin ba za ki fita a harkata ba. Mace ba
ta ajiye komai ba sai ta ci ta yasar da k'aton
kashi a masai! Gwara ni, tunda ko ba komai
na yi 6ari an ga shaida!"
Nene ba ta jira komai ba ta nufi wajen
girkinsu ta rarumo ta6arya ta taho a guje,
ai Abulle na ganin haka ta fad'a d'akinta, ga
shi ta kasa d'aga labulen kaban k'ofar d'akin
hakanan kawai ta turo kyauren.
Nene ta tsaya ta na huci ganin Mati ya sha
gabanta.
"Shegiya kai, ashe ke 'yar iskar k'arya ce, yo
ki tsaya mana idan ban nakastaki ba anan."
"Haba Nene, ya isa hakanan, muje daga ciki
ki ji."
Fad'in Mati hankali a tashe don shi har ya
rasa ma yanda zaiyi ga makwafta 'yan gulma
na kallo.
"Haba ke kuwa Nene, ki yi hakuri mana."
Fad'in Delu kenan cike sa tsegumi.
Wani banzan kallo Nene ta watsamata, sai
lokacin ta lura da tarin magulmatan
makwaftansu da ke lek'e.
"Kai! Allah Ya tsaremu da munafukai,
mutane ba su ajiye komai ba banda
munafunci da gulma, dadin abin dai mijina
bai ta6a jibgata ba kuma bai ta6a haikewa
wata ba."
Delu wacce tasan ita miji ke jibga ta ja tsaki
ta ce.
"Oho dai! Duk acikin so ne." Daganan ta bar
lek'en tare da yanmatan yaranta uku. Ita
Shafa salin alin ta sauka ba ta ce uffan ba,
to ina bakin magana tunda tasan da gaske
mijinta kwarto ne na a kwantanta.
Dakyar dai Mati ya kashe rigimar tare da
alk'awarin zai kawomata na ta k'unshin
tsiren. Abinka da kwad'ayyiya kamar
Asma'u a gari, ba musu ta hak'ura.
*** *** ***
Abulle ta ta6e baki.
Mati bai ko kula ba ya ci gaba da
maganarsa.
"Sanin kanki ne dai Inna ba ta damu da
zuwa k'auyen nan ba tunda Baban su Ladiyo
ya d'and'ana mata zaman birni, yanzu kuma
musamman don ni za ta zo ayi zumunci.
Don Allah Abulle, ke ce k'arama, ke ce
kuma ba ta sani ba, ki taimaka ku zauna
lafiya har ta tafi. Sannan inda hali inason ayi
wani abu."
"Menene shi?"
Ta fad'i da sauri.
Ya yi shiru sai kuma ya numfasa ya sassauta
murya.
"K'aryar ciki."
Gaba daya ta zaro idanu ta na dubansa. Ta
murza bajajjajen hancinta.
"Yi min gwari-gwari dai."
Ya hau bayani.
"Inna ta sanarmin cewa muddin ta tarar
kema ba ki da ciki to lallai za'a samu
matsala don kuwa sai na sake ki na yi wani
auren. Ni kuma kinsan dai ina sonki ina son
zama da ke, don.."
"Tsaya tsaya Mati, shi ke nan wannan abu
mai sauk'i ne zan yi, sai dai menene ribar?
Wace kyautar bajintar za ka samu bayan
hakan don nasan halinka, ba ka aikin
banza."
Ya yi 'yar dariya ya shafi sumarsa.
"Kai kai Abu tawa ta kaina, kina da saurin
fahimta kam. To bari ki ji, akwai wata
tafkekiyar gona ta Inna da kuma gida da ta
ke bayar da haya ana biyanta balas duk
karshen wata, ba yanda ban yi ba akan ta
bani gonar ta k'i, to ta tabbatarmin za ta
bani har da k'arin gidan nan ya zama
mallakin jikanta."
Abulle ai sai ta hau tsallen murna da sakin
gud'a.
Mati ya hau rufemata baki a tsorace.
"Ke ki rufamin asiri kada waccan ta ji."
Tunanowa da Nene da ta yi ne yasa ta
saurin sai ta kanta.
FIKRA WRITERS ASSOCIATION
*GIDAN MATI*
©ƁINGEL FULANI & RUFAIDA OMAR
Daga waje kuwa Nene na jin haka sai ta yi
wuf ta fito daga maɓoyarta, can baya take
zagayawa ta hau kan ɗan dutse tana kasa
kunne a ƙaramar tagar ɗakin Abulle. ta na
yi tana leƙa bayanta ko wani zai taho
wucewa kasancewar daga nan ana hangen
waje a dalilin gajartar katangar.
. Ɗakinta ta shige da saurinta, jiki na
rawa ta hau sauke kwallayenta tana faɗin;
"Idan sammako ku kayo, ni asubanci na yi."
Ta fiddo wani maganin gargajiya wanda
tayi mugun tsanar warinsa, sannan ta mai
da kayan ta afka garin kusan rabi a baki. Kan
ka ce mene wannan cikinta ya murɗa ga
yunƙurin amai da ta soma. Ai a guje ta fito
ta isa gaban makwararar ruwa ta hau sheƙa
aman iyakar ƙarfinta tana nishi yanda ta
tabbatar za su tsinkaya...
"Ni fa kamar kakari nake ji." Cewar Mati
yana kallon Abule.
"Kai fa daɗi na da kai har yanzu baka
bambance kukan Jakinka dana Akuyar
Delu."
"To idan ma itan ce kinyi zaune salon tamin
ta'adin da ta saba?"
Ya faɗa yana mai mi'kewa tsaye, itama da
sauri ta mi'ke tana mai rufa masa baya.
Ita ɗin ma ta wajen jin tahowarsu ya
sata zubewa gefen kwatamin tana mai ri'ke
cikinta da faɗin "Wayyo! Mati..."
Da gudansa ya 'kara so wajen yana mai
janyeta gefe.
"Ikon Allah! Nene ashe ke ce. Sannu me
kika ci ne haka?"
"Ba komai tun safe nake jin tashin zuciya da
rashin jin daɗi."
Ta faɗa da ƙyar tana sauke numfashi.
"A'a irin wannan ciwon ai ba na shiru ba
ne Nene, karki manta da haka Sahura ta
mutu da irin shirun nan."
"To Mati ana ta kai wa yake ta larura?
Taimaka min zakai Abule ta dubomin 'Yar
Magaji, ji nake kamar ana daka yaji a
kirjina."
"Huu'umm!" Abule ta faɗa tana tafa hannu.
"Ai wallahi da aiken kishiya gwamma na
jibgi Uwar miji. Kai ni ban ma yarda da
wannan ciwon ba. Saboda Allah Mati baka ji
warin tazargaje ba?"
Ta faɗa tana mai ɗaɗɗaga hanci sama.
"Me kike nufi ne? Kinga Abule ban san
fitina, ya mutum na halin ciwo kina kawo
shashanci. Idan na isa dake to maza ki je ki
dubomin 'Yar Magaji."
. Mintuna kaɗan Abule ta dawo da 'Yar
Magaji biye da ita ta rataya wata tutturna
jaka me kama da ta wazirin Sarkin kutare.
Kallo ɗaya tama Nene maƙaryaciyar
zuciyarta ta kisa mata menene,
dan haka ta kalli Mati da murmushi.
"Malam ai ba wata larura ba ce mai girma,
ƙaruwa ce zaku samu, a taƙaice dai Nene
ciki gare ta har na tsawon wata biyu."
"Kan babban bala'in can! Alkur'an
wannan ƙarya ce."
Abule ta faɗi tana mai buga tsalle gefe,
kafin kuma ta yi ɓarin da Nene ke kwance.
"Ke Nene ki ji tsoron Allah, ina ce ba
shekaranjiyar nan muka gama rikici kan
tsumma na da kika yaga kikai kunzugu da
shi ba?"
"Wayyo Ni Abule! Yau na ga abinda yafi
'karfina, wai cikin ma har kinsan ya yi wata
biyu sai ka ce wacce kika haɗa iri da Mayu.
ke kam 'Yar Magaji
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download GIDAN MATI

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album