Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

DAN ADAM Complete Hausa Novel Document by DAN ADAM


DAN ADAM

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 161602



DAN ADAM

Reading Time: 13 Hours

Added On: 08, Sep 2023

Author: Rufaida Omar ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 878.92 kb

File Type: txt

Views: 2651+

Download: 4192+

Last download: 3 days ago

Description/Story:    
Copied By
HAYATU BABA ZUBAIRU
(admin
Novels villa
Duniyan novels
Hayat hausa novels
Hausa novels and fashion
And
Cool novel, makeup and cooking)

WHATSAPP NO:
+2347039625239
                D'AN ADAM

       @Rufaida Omar

Sadaukarwa....ga....

        
Jiki na rawa take kwankwasa k'ofar d'akin da k'arfi tana fad'in.
  "Habiba! Ke Habiba!"
"Na'am." Ta furta cikin magagin bacci kafin ta mik'e ta bud'e d'akin. Ganin aminiyarta Saude ne ya sanyata wartsakewa babu shiri. Ta waro ido. "Lafiya dai Saude?"
  Saude ta rage murya.
"Ina fa lafiya? Ga waccan shegiyar tana nak'uda. Ai idan ta haihu na kad'e."
  Habiba ta dafa kafadarta.
"Karki damu, ai idan har ni ce unguwar zoma ba zata haife d'anta da rai ba. Itama muje sai ta bar duniya."
  Wani sanyi ya mamaye zuciyarta. Habiba ta dauko kayan amfani ta yi gaba Saude na biye da ita. Lokacin karfe shida na safe.
  Acan suka iske Malam Balarabe yanata faman zirga-zirga a tsakar gidan. Shigowarsu ne ya sanyashi nufarsu da saurinsa.
   "Yauwa, Habiba don Allah taimaka mata."
  "Ka kwantar da hankalinka Malam Balarabe, in sha Allahu lafiya kalau zata sauka. Ka sama mana itatuwa dai na dora ruwan zafi.
  Daga haka ta shiga ciki, Saude na gefe tana matsar kwallar munafunci ita a lallai tausayin abokiyar zamanta takeyi. Da ire-iren kissar da take cin galabar Malam Balarabe kenan. Da sauri shi kuma Malam ya fice.
    Saude dake tsaye sai jin kukan jariri tayi. Gabanta ya bada ras ras! A gigice ta fad'a d'akin. Bakinta na rawa ta tambaya. "Ta..ta.." Ina maganar gaba daya ta mak'ale a saman le66anta. 
Habiba ta dubeta tayi mata alama da tayi shiru. Dole ta rufe bakinta ba don ta so ba. 
  Habiba ta kammala yanke cibi ta mik'awa Saude d'iyar. Saude cikin kukan bakin ciki marar sauti ta kar6eta tana ji kamar ta shak'eta ta mutu.  
  Ga mamakin Saude, Habiba filo ta dauko ta danne fuskarta da shi, tun Hasiya na shure-shure har tayi lakwas. Saida ta tabbatar da cewar ta cika sannan ta yi jifa da filon ta mik'e tana sharce gumi. 
   Saude jikinta babu inda baya rawa.
"Ta mutu." Ta fad'a a gigice. 
Habiba ta gyada mata kai sannan ta dubeta.
  "Eh na cika burinki. Yanzu Malam na dawowa mu nuna mutuwa tayi bayan ta haife d'iyarta. Ko kusa kada ki nuna wata alama ta rashin gaskiya Habiba. Ita kuma wannan k'aramar alhaki ce, ni nasan yanda zamuyi da ita nan gaba kadan."
   Saude ta amince da batun aminiyarta. 
"Shikenan."
  Ai kuwa sunajin sallamar Malam suka hau salati da koke-koke.
Malam baisan sadda ya yarr da itatuwan da ya riko ba. Jiki na rawa a gigice ya fada dakin yana tambayar ko lafiya.
  Ya dubi Saude hannunta rike da jaririya tana ta canyara ihun kuka kafin ya kai dubansa ga Habiba. Bai yi wata-wata ba ya yi kan Hasiya yana kiranta a rud'e.
"Hasiya! Hasiya!!"
  Ina! Ya fahimci abinda ake nufi, Hasiya ta rasu. Ya hau salati yana zubda  ruwan hawaye. Baice uffan garesu ba ya fita zuwa tsakar gida ya zauna.
                     *    *     *
   Haka yana ji yana gani aka wanke Hasiya aka kaita gidanta na gaskiya batare da 'yan uwanta sun sani ba saboda nisan dake tsakanin garuruwansu. 
    Malam Balarabe ya shiga tashin hankali matsananci, ya rame yayi bak'i kamar ba farin mutum ba. Ga duk wanda ya ganshi dole ya tausaya mishi musamman abokansa wadanda suka riga sukasan irin kaunar da yake yiwa matarsa Hasiya don kuwa baya 6oyemusu irin yanda take kyautata mishi a rayuwa ta hanyar yin biyayya ga dukkanin umarninsa. 
     Sai ranar bakwai sannan babban yayan Hasiya da kuma mahaifiyarta da sauran yayyunta uku mata suka iso. Sun koka kwarai da rashin yar uwarsu. Saidai babu yanda suka iya, su mutane ne wadanda sukasan ya kamata, sam basu zargi komai ba. Toh me zasu zarga? Bayan sun san irin kaunar da Saude ke nunawa Hasiya a gabansu tamkar ba kishiyarta ba. Wannan ne yasa koda Saude tace zata rik'e yarinya, babu wanda baiyi na'am ba. Haka suka tattara suka koma garinsu batare da shakkar komai ba.
                        *   *   *
  Wahala, tsangwama da kyara, babu irin wacce d'iyar Hasiya, wacce ta ci sunan mahaifiyarta Hasiya suke kiranta da Ummi, bata gani ba wajen Saude. Saidai a gaban idon Malam Balarabe, babu abinda Saude bata yiwa Ummi na nuna kulawa da kauna. Yarinya ce mai hakuri, haka take hakura da komai ta shanyeshi, anan ma Mahaifiyarta ta dauko.
  Saida ta kai shekaru goma sha uku a duniya sannan Saude ta samu ciki. Zo kaga murna wajen Saude da mijinta. Sai ya zamana bayan Saude ta haifi diyarta Mariya. Ta chanja kwarai a gidan. Ta hanyar asiri da tsafi, ta siye zuciyar Malam Balarabe ya zamana ko kallon Ummi baya kaunar yi. Komai ya samo, daga Saude sai Mariya. A wannan lokacin ne, Habiba ta zo da shawarar tura Ummi aikatau. Ba musu ba jayayya, Malam Balarabe ya amince da a turata ko bangon duniya ne. Duk acewarsa, bashi da matsala ko wata damuwa...!
     DAN ADAM
@Rufaida Omar
  (02)

"Wai kina ina ne? Baki kammala shirya tsummokaran naki ba?"
  Ummi dake d'aki tana kuka, ta tsinci muryar Baba Saude wacce ta sanyata rud'ewa babu shiri. Cikin rawar murya ta amsa a tsorace.
  "Na gama Baba, ganinan."
Daga haka ta mik'e da saurinta ta dauki ledarta ta fito har lokacin kuka takeyi sosai.
   Baba Saude na zaune tare da Habiba sai wata mata wacce ita ke dillancin mata zuwa gidajen aikatau, a gefe kuwa, Mariya ce ke faman cin masara hankalinta kwance, ta yi filo da cinyar uwarta.
   Wata harara Baba Saude ta watsawa Ummi.
  "Shegen bakin hali, kukan me kikeyi na kinibibi toh? Gwara ki share hawayenki ma, don babu abinda zai hana yau ki bar gidan nan."
   Ummi ta durkushe a gefe tana share hawaye yayinda wasu ke k'ara kwaranyowa har da majina tana gogewa da hijabinta.
   Baba Saude ta juya ga dillaliya.
"Ina jinki Yaha, yanzu dai duk wata zaki dunga aiko da albashin nata?"
  Wacce aka kira da Yaha ya gyara zaman mayafinta lokacin da ta mike tsaye.
  "Karki damu, duk wani abin arziki da ta samu ma, naki ne Saude. Komai zan tattaro na kawomaki. Kedai ki kwantar da hankalinki kamar kin kashe d'an maigari."
  Sukayi dariya sannan Yahanasu ta dubi Ummi tana yamutse fuska.
  "Wannan dogon gashin idan bakiyi wasa ba sai na yankeshi kafin mu k'arasa, yarinya sai shegen munafunci. Zaki maidashi cikin hijabin ko kuwa?"
   Jiki na rawa Ummi ta ja jelar kitson kalbar da ta jagwalgwala a kanta ta maidashi cikin hijabi. Don kuwa bata isa ta je gidan kitso ba har ya saka ran samun mai kyau. Ta mike ta bi bayan Yaha wacce tuni tayi sallama da su ta bata umarnin ta taso. 
   Suna ficewa Habiba da Saude suka tafa suna shewar jin dadi.
  "Ina sonki wallahi aminiya, bani da tamkar ki." Cewar Saude wacce ke jin ranta yayi wani mugun sanyi. 
  Habiba ta gwaguyi masarar hannunta tana wani rausaya kai.
  "Ni ce fa, sai ma idan kudi sun soma shigomaki a hannu zakisan cewa ba k'aramin gata nayi miki ba. Ai ba'a saurin illata d'iya mace haka, ita tamkar jari ce, ko zata bi duniya in dai zata nemo ta kawomaki to kada ki damu kanki, ke dai ki more rayuwarki ta jikinta. Amma fa 'yar kishiya nake nufi."
    Sukayi shewa da dariyar farin ciki. Koda Malam Balarabe ya iso suka sanar mishi cewar Ummi ta tafi, ko a jikinsa, karshe ma watsar da zancen yayi ya bi Mariya da tsarabar 'yar tsanar da ya siyomata.
                      *   *   *
    Tun Ummi na kuka a motar kasuwa, har ta gaji tayi shiru tana kallon hanya kafin bacci kuma mai nauyi yayi awon gaba da ita. 
Cikin baccin kuma ta ji Yaha na tashinta.
  "Ke! Ke!" Firgigit ta farka tana dubanta. "Na'am." Ta amsa a tsorace don kuwa kusan zuwa yanzu Ummi ta saba da hakan, da wuya tayi bacci a tasheta batare da ta firgita ba. Don sau da yawa ruwan sanyi ake kwara mata ko kuma a sanya k'afa a haureta, wani sa'in kuwa da bulala ake tashinta. Yaha ta watsa mata mugun kallo.
  "Sai ki sauko tunda motar bata ubanki bace ko? Shashashar yarinya."
  Ummi ta lura su kadai ya rage a motar, cikin rawar jiki ta bi bayan Yaha suka fito. Sai lokacin ta lura cewar cikin wani babban gari suke lura da yawan mutanen da ta ga suna faman zirga-zirga. Haka tayi ta bin bayan Yaha har suka fito daga tashar zuwa bakin titi. Saida gabanta ya fad'i ganin ababen hawa da yawa saman kwalta. Ta tsorata sosao da yawan mutanen da ke zirga-zirga awajen.
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download DAN ADAM

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album