Join Our WhatsApp Group

DAN ADAM Complete Hausa Novel Document by DAN ADAM


DAN ADAM

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 161602



DAN ADAM

Reading Time: 13 Hours

Added On: 07, Sep 2023

Author: Rufaida Omar ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 878.92 kb

File Type: txt

Views: 1562+

Download: 1466+

Last download: 3 hours ago

Description/Story:    
Copied By
HAYATU BABA ZUBAIRU
(admin
Novels villa
Duniyan novels
Hayat hausa novels
Hausa novels and fashion
And
Cool novel, makeup and cooking)

WHATSAPP NO:
+2347039625239
                D'AN ADAM

       @Rufaida Omar

Sadaukarwa....ga....

        
Jiki na rawa take kwankwasa k'ofar d'akin da k'arfi tana fad'in.
  "Habiba! Ke Habiba!"
"Na'am." Ta furta cikin magagin bacci kafin ta mik'e ta bud'e d'akin. Ganin aminiyarta Saude ne ya sanyata wartsakewa babu shiri. Ta waro ido. "Lafiya dai Saude?"
  Saude ta rage murya.
"Ina fa lafiya? Ga waccan shegiyar tana nak'uda. Ai idan ta haihu na kad'e."
  Habiba ta dafa kafadarta.
"Karki damu, ai idan har ni ce unguwar zoma ba zata haife d'anta da rai ba. Itama muje sai ta bar duniya."
  Wani sanyi ya mamaye zuciyarta. Habiba ta dauko kayan amfani ta yi gaba Saude na biye da ita. Lokacin karfe shida na safe.
  Acan suka iske Malam Balarabe yanata faman zirga-zirga a tsakar gidan. Shigowarsu ne ya sanyashi nufarsu da saurinsa.
   "Yauwa, Habiba don Allah taimaka mata."
  "Ka kwantar da hankalinka Malam Balarabe, in sha Allahu lafiya kalau zata sauka. Ka sama mana itatuwa dai na dora ruwan zafi.
  Daga haka ta shiga ciki, Saude na gefe tana matsar kwallar munafunci ita a lallai tausayin abokiyar zamanta takeyi. Da ire-iren kissar da take cin galabar Malam Balarabe kenan. Da sauri shi kuma Malam ya fice.
    Saude dake tsaye sai jin kukan jariri tayi. Gabanta ya bada ras ras! A gigice ta fad'a d'akin. Bakinta na rawa ta tambaya. "Ta..ta.." Ina maganar gaba daya ta mak'ale a saman le66anta. 
Habiba ta dubeta tayi mata alama da tayi shiru. Dole ta rufe bakinta ba don ta so ba. 
  Habiba ta kammala yanke cibi ta mik'awa Saude d'iyar. Saude cikin kukan bakin ciki marar sauti ta kar6eta tana ji kamar ta shak'eta ta mutu.  
  Ga mamakin Saude, Habiba filo ta dauko ta danne fuskarta da shi, tun Hasiya na shure-shure har tayi lakwas. Saida ta tabbatar da cewar ta cika sannan ta yi jifa da filon ta mik'e tana sharce gumi. 
   Saude jikinta babu inda baya rawa.
"Ta mutu." Ta fad'a a gigice. 
Habiba ta gyada mata kai sannan ta dubeta.
  "Eh na cika burinki. Yanzu Malam na dawowa mu nuna mutuwa tayi bayan ta haife d'iyarta. Ko kusa kada ki nuna wata alama ta rashin gaskiya Habiba. Ita kuma wannan k'aramar alhaki ce, ni nasan yanda zamuyi da ita nan gaba kadan."
   Saude ta amince da batun aminiyarta. 
"Shikenan."
  Ai kuwa sunajin sallamar Malam suka hau salati da koke-koke.
Malam baisan sadda ya yarr da itatuwan da ya riko ba. Jiki na rawa a gigice ya fada dakin yana tambayar ko lafiya.
  Ya dubi Saude hannunta rike da jaririya tana ta canyara ihun kuka kafin ya kai dubansa ga Habiba. Bai yi wata-wata ba ya yi kan Hasiya yana kiranta a rud'e.
"Hasiya! Hasiya!!"
  Ina! Ya fahimci abinda ake nufi, Hasiya ta rasu. Ya hau salati yana zubda  ruwan hawaye. Baice uffan garesu ba ya fita zuwa tsakar gida ya zauna.
                     *    *     *
   Haka yana ji yana gani aka wanke Hasiya aka kaita gidanta na gaskiya batare da 'yan uwanta sun sani ba saboda nisan dake tsakanin garuruwansu. 
    Malam Balarabe ya shiga tashin hankali matsananci, ya rame yayi bak'i kamar ba farin mutum ba. Ga duk wanda ya ganshi dole ya tausaya mishi musamman abokansa wadanda suka riga sukasan irin kaunar da yake yiwa matarsa Hasiya don kuwa baya 6oyemusu irin yanda take kyautata mishi a rayuwa ta hanyar yin biyayya ga dukkanin umarninsa. 
     Sai ranar bakwai sannan babban yayan Hasiya da kuma mahaifiyarta da sauran yayyunta uku mata suka iso. Sun koka kwarai da rashin yar uwarsu. Saidai babu yanda suka iya, su mutane ne wadanda sukasan ya kamata, sam basu zargi komai ba. Toh me zasu zarga? Bayan sun san irin kaunar da Saude ke nunawa Hasiya a gabansu tamkar ba kishiyarta ba. Wannan ne yasa koda Saude tace zata rik'e yarinya, babu wanda baiyi na'am ba. Haka suka tattara suka koma garinsu batare da shakkar komai ba.
                        *   *   *
  Wahala, tsangwama da kyara, babu irin wacce d'iyar Hasiya, wacce ta ci sunan mahaifiyarta Hasiya suke kiranta da Ummi, bata gani ba wajen Saude. Saidai a gaban idon Malam Balarabe, babu abinda Saude bata yiwa Ummi na nuna kulawa da kauna. Yarinya ce mai hakuri, haka take hakura da komai ta shanyeshi, anan ma Mahaifiyarta ta dauko.
  Saida ta kai shekaru goma sha uku a duniya sannan Saude ta samu ciki. Zo kaga murna wajen Saude da mijinta. Sai ya zamana bayan Saude ta haifi diyarta Mariya. Ta chanja kwarai a gidan. Ta hanyar asiri da tsafi, ta siye zuciyar Malam Balarabe ya zamana ko kallon Ummi baya kaunar yi. Komai ya samo, daga Saude sai Mariya. A wannan lokacin ne, Habiba ta zo da shawarar tura Ummi aikatau. Ba musu ba jayayya, Malam Balarabe ya amince da a turata ko bangon duniya ne. Duk acewarsa, bashi da matsala ko wata damuwa...!
     DAN ADAM
@Rufaida Omar
  (02)

"Wai kina ina ne? Baki kammala shirya tsummokaran naki ba?"
  Ummi dake d'aki tana kuka, ta tsinci muryar Baba Saude wacce ta sanyata rud'ewa babu shiri. Cikin rawar murya ta amsa a tsorace.
  "Na gama Baba, ganinan."
Daga haka ta mik'e da saurinta ta dauki ledarta ta fito har lokacin kuka takeyi sosai.
   Baba Saude na zaune tare da Habiba sai wata mata wacce ita ke dillancin mata zuwa gidajen aikatau, a gefe kuwa, Mariya ce ke faman cin masara hankalinta kwance, ta yi filo da cinyar uwarta.
   Wata harara Baba Saude ta watsawa Ummi.
  "Shegen bakin hali, kukan me kikeyi na kinibibi toh? Gwara ki share hawayenki ma, don babu abinda zai hana yau ki bar gidan nan."
   Ummi ta durkushe a gefe tana share hawaye yayinda wasu ke k'ara kwaranyowa har da majina tana gogewa da hijabinta.
   Baba Saude ta juya ga dillaliya.
"Ina jinki Yaha, yanzu dai duk wata zaki dunga aiko da albashin nata?"
  Wacce aka kira da Yaha ya gyara zaman mayafinta lokacin da ta mike tsaye.
  "Karki damu, duk wani abin arziki da ta samu ma, naki ne Saude. Komai zan tattaro na kawomaki. Kedai ki kwantar da hankalinki kamar kin kashe d'an maigari."
  Sukayi dariya sannan Yahanasu ta dubi Ummi tana yamutse fuska.
  "Wannan dogon gashin idan bakiyi wasa ba sai na yankeshi kafin mu k'arasa, yarinya sai shegen munafunci. Zaki maidashi cikin hijabin ko kuwa?"
   Jiki na rawa Ummi ta ja jelar kitson kalbar da ta jagwalgwala a kanta ta maidashi cikin hijabi. Don kuwa bata isa ta je gidan kitso ba har ya saka ran samun mai kyau. Ta mike ta bi bayan Yaha wacce tuni tayi sallama da su ta bata umarnin ta taso. 
   Suna ficewa Habiba da Saude suka tafa suna shewar jin dadi.
  "Ina sonki wallahi aminiya, bani da tamkar ki." Cewar Saude wacce ke jin ranta yayi wani mugun sanyi. 
  Habiba ta gwaguyi masarar hannunta tana wani rausaya kai.
  "Ni ce fa, sai ma idan kudi sun soma shigomaki a hannu zakisan cewa ba k'aramin gata nayi miki ba. Ai ba'a saurin illata d'iya mace haka, ita tamkar jari ce, ko zata bi duniya in dai zata nemo ta kawomaki to kada ki damu kanki, ke dai ki more rayuwarki ta jikinta. Amma fa 'yar kishiya nake nufi."
    Sukayi shewa da dariyar farin ciki. Koda Malam Balarabe ya iso suka sanar mishi cewar Ummi ta tafi, ko a jikinsa, karshe ma watsar da zancen yayi ya bi Mariya da tsarabar 'yar tsanar da ya siyomata.
                      *   *   *
    Tun Ummi na kuka a motar kasuwa, har ta gaji tayi shiru tana kallon hanya kafin bacci kuma mai nauyi yayi awon gaba da ita. 
Cikin baccin kuma ta ji Yaha na tashinta.
  "Ke! Ke!" Firgigit ta farka tana dubanta. "Na'am." Ta amsa a tsorace don kuwa kusan zuwa yanzu Ummi ta saba da hakan, da wuya tayi bacci a tasheta batare da ta firgita ba. Don sau da yawa ruwan sanyi ake kwara mata ko kuma a sanya k'afa a haureta, wani sa'in kuwa da bulala ake tashinta. Yaha ta watsa mata mugun kallo.
  "Sai ki sauko tunda motar bata ubanki bace ko? Shashashar yarinya."
  Ummi ta lura su kadai ya rage a motar, cikin rawar jiki ta bi bayan Yaha suka fito. Sai lokacin ta lura cewar cikin wani babban gari suke lura da yawan mutanen da ta ga suna faman zirga-zirga. Haka tayi ta bin bayan Yaha har suka fito daga tashar zuwa bakin titi. Saida gabanta ya fad'i ganin ababen hawa da yawa saman kwalta. Ta tsorata sosao da yawan mutanen da ke zirga-zirga awajen. A kauyensu na Ringim babu motoci har haka. Yaha ta tsayar da d'an sahu. Nan Ummi ta ji tace ya kaisu Gadon K'aya. 
  A hanya Ummi tayi ta rarraba ido tana duban tituna. Abin bai gama bata mamaki ba, saida ta ga sun hau wani dogon kwalta ta sama. 
  Ta kankame ledar kayanta, basuyi aune ba sai ji sukayi ta fashe da kuka.
  "Wayyo Allah zan mutu!" Ta fad'a iyakar k'arfinta. D'an sahun harda kokarin juyowa.
  "Lafiya?!" Yaha ta rankwashi kanta.
"Ka bar 'yar iskar yarinya mana, "yar kauye. Ta ji ta a titin 'yan birni zata kawomin iskanci. Yanzun nan zan bubbugeki idan baki rufemin wannan  karamin bakin naki ba mai kama da na tsutsa."
    Dariya d'an sahun ya kwashe da shi. Ita kuwa Ummi da sauri ta rufe bakinta, tana kuka a ciki-ciki har suka sauka idanunta a runtse yayinda jikinta ke kad'awa. 
   D'an sahun kuwa har da labarin tsohuwar da tayi makamancin hakan ya shiga bawa Yaha. Kasancewar Yahar itama ba baya ba wajen surutu, nan ta biyemishi suna tayi tana 6a6aka dariya. Ummi dai tana jinsu, alokacin ta bar kukan. 
   Sunyi kusan rabin awa suna tafiya sannan suka iso unguwar da ta ji Yaha tayi kira da Gadon K'aya. Haka ta ji Yaha nayita zuba mishi kwatance har suka iso wani gida d'an flat da shi. Ta biyashi kudinsa sannan ta dubi Ummi. "Sauka muje."
  Ba musu Ummi ta sauka da saurinta. Yaha tayi gaba ta bi bayanta tana wulk'a idanu tana duban layin. Yaha ta shiga kwankwasa k'ofar tana sallama. Can ta tsinci muryar maigadin na cewa. 
"Ana zuwa."
     
  Yaha ta rik'e k'ugu tana taunar cingam ta dubi Ummi. Ganin haka yasa Ummi kauda nata idanun cikin sauri. 
   "Don ubanki saura kiyi min halin kauyenci sai na shak'e ki kin mutu har lahira. Banason yawan kalle-kalle. Kiyi ladabi so..."
  Sauran maganar ya mak'ale a fatar bakinta ganin an soma k'ok'arin bud'e k'ofar.
   Maigadin ya d'an lek'o da kansa. Farin buzu ne. Ganin Yaha ya sanyashi sakin fuska. 
  "A'a mai yara, kaine?"
  Hakanan yake kiranta. Tayi dariya.
"Ni ce dai Baba. Hajiyar na ciki ko?"
  Ya bata hanya ta shigo yana amsa mata.
  "Eh yana nan. Ina ka samo d'an garinmu?"
   Ya fad'a yana duban Ummi wacce ta durkusa da rawar jiki ta gaisheshi. 
  Yaha ta dubeta tayi mata alamun ta mik'e.
   "Wannan ba 'yar garinku bace. 'Yar Maiduguri ce."
   "Anya? Yana kama da mu." Yaha dariya kawai ta d'anyi batace uffan ba.
   Daga haka sukayi ciki. 
Ummi na bin farfajiyar da kallo a sace don bataso Yaha ta kamata tana kallon bayan ta ja mata kunne. Babban gida ne sosai, an k'awatashi da shuke-shuke. Daga wajen ka rantse ba shi da wani kyau ko girma don kuwa ko fenti ba'ayi ba daga wajen. 
   Haka suka isa har bakin wata k'ofa. Yaha ta murd'a ta shiga. Suka cigaba da tafiya a doguwar barandar dake wajen har suka iso tsakar gidan. Acan bakin rariya, wata babbar mace dattijuwa ce ke zaune saman kujera irin ta tsakar gida tana wanke-wanke.   Ganin Yaha ta washe baki.
  "A'a, lale marhabin da Hajiya Yaha. Yau kuma zuwan rana ce?"
  Yaha ta numfasa fuskarta na nuna gajiya.
   "Bari kawai Ramma, duk a gajiye nake. Hajiyar na ciki mu k'arasa?"
   Ramma fuska a sake ta amsa tana duban Ummi wacce ke takure jikin bango. 
  "Eh tana ciki." Ummi da sauri ta gaisheta. Ramma ta amsa. Har suka kama hanya Ramma na binta da kallo, yarinyar da alamu zasu d'asa da Hajiya Madina, don kuwa da alama nutsastsiya ce
DAN ADAM

@Rufaida Omar
          04
     
"Sannu Ummi."
Muryar Amina ta katsemata tunani, ta dubeta, sukayi murmushi a tare.
  "Yauwa."
  Amina ta ninke abin sallar ta ajiye a gefe. Zama tayi a gefen katifa kusa da Ummi tana dubanta.
   "Daga wane gari kuke?"
"Ringim." Ta amsa a takaice. 
"Lallai, baku da nisa sosai."
Ummi zuwa yanzu ta dan saki jiki da Amina ganin irin yanda take janta a jiki.  Wannan yasa itama bata ji nauyin tambayarta ba.
  "Ke ba anan kusa kike ba?"
Ta gyada kai.
"Anan dai nayi rayuwata, amma mahaifina d'an Maradi ne can cikin jamhuriyar Nijar. Zama da neman abinci ne ya kawoshi Nijeriya sukayi aure da Innata, amma yanzu ya rasu, ya barmu mu hudu yaransa. Ni ce 'ya ta uku a cikinsu."

  Ummi ta d'an tallafi kumatunta.
"Kema aiki kike yiwa Hajiya?"
Amina ta murmusa.
"Ni ina yiwa Hajiya Mama aiki ne, kanwar Hajiyarnan ce, abinda yasa kika ganni a gidannan, sunyi tafiya ne da mijinta da yaransu, shine dalilin da yasa na dawo nan da zama kafin su dawo."
    Ummi ta jinjina kai cike da gamsuwa. A ranta ta ji babu dad'i, kenan itama wataran zata bar gidan ta barta? 
   "Ya dai Ummi? Kinyi shiru ina magana."
  Ummi a sanyaye ta girgiza kai.
"Bakomai."
  Jin haka yasa Amina yin murmushi.
"Shikenan, tashi muje mu tattara falo da kicin kafin Hajiya tayi magana, ki dunga lura da dukkan abinda nakeyi, nasan karshe ke zaki maye gurbina."
   Ummi bata ko damu ba, idan ana sabo da aikin wahala, ai yaci kuwa ace ta saba, ina take samun damar yin cikakken awa sadda tana gidan babanta batare da an had'ata da wani nannauyan aikin ba? Gashi anan har gatan da za'a gyara mata kai a bata wajen kwana tsaftatacce da abinci mai kyau ta samu. Ai babu abinda zata ce ga Ubangiji sai godiya.
   Haka ta bi bayanta zugui-zugui suka fita. A falon suka iske Adnan da kannensa su biyu, wadanda ta ji Ramma ta ambacesu da Ihsan, Hanifa da Fahad wanda shi ne auta a d'akin nasu. 
    Adnan hankalinsa kacokam yana kan wayar hannunsa yana faman latse-latse, yayinda Ihsan ta dukufa wajen koyawa kannenta aikin gida da aka basu a makaranta. Shekarun Ihsan goma sha uku a duniya zata shiga na hud'u, sa'ar Ummi ce. Hanifa kuwa, tana da shekaru goma sha biyu bata da tazara tsakaninta da Ihsan, Fahad ne mai shekaru takwas a duniya. Daga kansa kuma, Hajiya Madina bata k'ara haihuwa ba. 
   Yaranta gaba daya su takwas ne cif, mata uku ne kafin zuwan Adnan duniya, Rahila, Na'ima, Aisha, gaba dayansu ukun suna gidajen aure.
      Shigowarsu falon...


Read / Download DAN ADAM

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album