Join Our WhatsApp Group

BABBAN GORO Complete Hausa Novel Document by BABBAN GORO


BABBAN GORO

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 117003



BABBAN GORO

Reading Time: 9 Hours

Added On: 28, Oct 2023

Author: Khadeeja Candy ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Khadijacandy44@gmail.com

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 626.41 kb

File Type: txt

Views: 789+

Download: 529+

Last download: 7 hours ago

Description/Story: [9/13, 11:19 PM] Auntie Candy: BISMILLAHI RAHAMIN RAHIM

Wannan littafin sadaukarwa ne ga Aunty na Anty Maijidda musa


BABBAN GORO...!

NA

KHADEEJA CANDY


1___Tsaye yake gaban wani k'aton dressing mirror, sanye da black suit yana gyara necktie,
_Give me freedom give me fire give me reason take me higher see the champions take the field now you define us make us feel proud_
A hankali yake bin sautin wak'ar suna rerewa tare, wani _pear watch_ naga ya ɗauko yasa bayan ya feshe jikin shi da turare _the real man_ tsaye yayi yana kallon kanshi a mirror, nan nima na tsaya ina k'are mashi kallo.
Dogone kuma fari fes mai dogon hanci gashi da manyan ido a gefen bakinshi an manna mashi dimples.
Murmushi yayi ganin yadda suit ɗin ya zauna jikanshi yayi mashi kyau sosai kamar dan shi akayi shi, sai da ya ɗauki wani _blue oil_ ya shafa a kanshi sannan ya nufo wani ɓangaren na ɗakin,
Babu komai a gurin sai sai jerin talkama na gani na faɗa, wasu _half cover shoes_ ya ɗauko yasa,
Sai da ya sake duba kanshi a madubin sannan ya nufi part ɗin maihaifiyarshi.

*****

Da sallama ya shigo Safiya ta amsa mishi, zaunawa yayi yana faɗin
“Ina Momi.?”
“Tana ɗaki wanka take”
“ok”
Hannu ya kai ya ɗauki wani littafi dake saman Center table _The broken heart_

“Man ka karanta news kuwa.?”
Nasir ne ya shigo yana maganar rik'e da jarida a hannunshi, kai Saif ya girgiza
“A'a miya faru ne.?”
Jaridar ya mik'a mishi yana faɗin
“Wai wata yar minister ce tayi k'ok'arin kashe kanka”
“Wow a ina.?”
Saif ya tambaya bayan ya k'arɓi jaridar,
“A Nigeria”
Nasir ya bashi amsa
“Toh mi akayi mata.?”
Zaunawa yayi yana bashi amsa
“Nima abinda nake son sani kenan nida yan'jarida”
Sai da Saif ya ɗan karanta jarifar sannan yace
“Yar minister man fetur ce Dr. Salamatu Abubuwa Yola kuma ita kaɗai ta haifa”
Safiya ta rik'e baki
“Amman dai ta mutu ko?”
“A'a bata mutu ba tana dai cikin mawuyacin hali”
Saif ya faɗa still yana duba jaridar,
Safiya ta cige baki
“Amman wallahi naso ta mutu dan ina jin daɗi ne yayi mata yawa”
Murmushi Nasir yayi
“Haba dai kiji ance ita kaɗai mahaifiyarta ta haifa kiyi mata wannan fatan yanzu haka fa mahaifiyarta tana cikin kiɗima”
“Toh ai gani nake iskanci ne yayi mata yawa idan ba shi ba miye na kashe kai?”
Nasir yace
“Baki san dalilinta ba”
“A'a Ya Nasir babu wani dalili ina jin dai kawai ta gaji da duniyar ne ko kuma bata da hankali” Faɗar Safiya,
Tashi Saif yayi “Allah ya kyauta ni bari na lek'a part ɗin Dad idan Momi ta fito kice mata na fita”
Kai Safiya ta ɗaga mishi yasa hannunshi aljihu ya fice,

_LABARAN DUNIYA,_
_Mai Karantawa Fareeda Muhammad Yabo. Da Farko Ga Kanunsu Bom Ya Fashe A Wata Mashaya Dake Amerika, Isra'ila Ta Shiga Teburin Tattauna Da Falasdin, Wata Kotu A K'asar Masar Ta Yan Kewa Wasu Matasa Hukuncin Shekaru Goma Gidan Kaso , Shugaban K'asar Turkiyya Zai Kaiwa Takwaransa Na K'asar Faransa Ziyara, A Najeriya Kuma Wata Yar ' Minister Tayi Unkurun Hallaka Kanta.._

Alhaji Bashir Bature ne kishingiɗe cikin makeken ɗakinshi da aka k'awata da kayan alatu yana sauraren radio dake gefen shi yana aiki,
Salamar da Saif yayi ne yasa shi ɗago kai tare da amsawa
“Wa' alaikassalam”
Guri ya samu kusa dashi ya zauna
“Barkada Safiya Dad”
Hannu Dad ya kai ya kashe radio sannan ya amsa mishi
“Barka dai Ka tashi lafiya.?”
“Lafiya kalau Alhamdulillahi”
Tashi Dad yayi zaune ya kalli Saifa yace “Ya maganar Matarka?”
Kawarda Fuska yayi yana ɗan sosa kai,
Dad yace “Saifullahi Hak'uri fa ake da mata, duk wani mai iyali da kake gani hak'uri yake muma da ba muyi hak'urin ba da bamu kai yanzu ba nan gaba kaɗan fa Uba zaka zama idan babu hak'uri yaya kenan? Kaga itama kanta tayi nadama tunda har kaga iyayenta sunyi magana”
Wani guntu numfashi yaja “Dad ni Wallahi halinta ne bana so kuma nayi nayi da ita tak'i ta chanja”
“Ka daiyi hak'uri ka dawo da ita muga abinda Allah zaiyi”
“Shi kenan Dad zan maida ta In Sha Allah”
“Toh Allah yayi maka albarka ya baku hak'urin zama da juna”
“Amin Dad thank you”
Tea cup ɗin dake gabanshi ya ɗauka ya kurɓa sannan ya sake kallon Saif
“Saifullahi”
A natse na amsa
“Na'am Dad”
“Ina son yanzu idan ka fita kaje gidan Dr. Salamatu Abubakar Yola ka bincika min lafiyar yarta dan faɗa min tayi unk'urin hallaka kanta kuma yanzu ma naji a labarai”
“Ok Dad zanje yanzu dana fita amman Dad an faɗi dalilin yin hakan da tayi?”
Gyaran murya Dad yayi
“Har yanzu ni dai banji wani dalili ba ina dai son kaje ka bincika”
“Yanzu ma dana fita daga nan can zanje”
“Yayi Kyau karfa ka manta da zancen Matar ka”
Tashi yayi yana murmushi “Toh Dad bazan manta ba” Sai da yayi mishi Sallama sannan ya fice.
[9/13, 11:19 PM] Auntie Candy: BABBAN GORO...!

NA

KHADEEJA CANDY


Episode___2

Saif na fita parking space ya nufa, yana shiga motarshi yayi mata key yayi horn aka buɗe mashi gate,
Hanyar da zata kai shi gidan Dr. Salamatu ya bita yana gudu kamar zai tashi sama daman haka al'adarshi take gudu a mota,
Yana isa yayi horn maigadi na lekowa yaga Saif jiki na rawa ya bude mashi yana ɗaga mashi hannu,
Yana yin parking ya fito ya cikin gidan, duk inda yabi gaishe shi ake cikin girmamawa da rawar jiki,
tun kamin ya k'arasa parlor wata tsohuwa ta tareshi bayan sun gaisa tace
“Hajiya fa bata nan tana asibiti dan gidan ba lafiya”
“Eh naji ai shi ne abunda ya kawo ni wace asibitin aka kai ta?”
“Kings Hospital aka kaita”
Bai tsaya jiran ta k'ara cewa wani abun ba ya ya juya tunda yaji abinda yake son ji.
Cikin minti biyar ya isa asibitin yana yin parking ya nufi Emergency,
Reception ya tafi aka faɗa mishi ɗakin da suke, a hankali yake tafiya har ya isa gurin.
Tsaye ya tararda Dr. Salamatu, wasu mata na tsaye kusa da ita duk kansu sun rakfa uban tagumi especially ita sai ruwan hawaye take,
Da sanyin jiki ya k'arasa kusa dasu
“Dr. Salamatu”
Da sauri ta kalleshi kamin tayi magana ya rigata
“Mr President yace nazo na duba jikin yarki ko tayi rai?”
Cikin muryar kuka tace
“Eh sunce tana da rai sai dai ban tabbatar da lafiyarta ba dan tun jiya basu barni na shiga ba yanzu ma suna ciki suna duba ta”
“Okey”
Kawai yace ya juya da nufin tafiya hakan nan kuma sai ya samu kanshi da kasa tafiyar, juyowa yayi ya zauna a kujerar dake gurin yana kallon kofar ɗakin,


2 hours later...
Likitoci uku suka fito daga cikin ɗakin, da sauri Dr. Salamatu ta nufe su tare da matan har Saif, ɗaga daga cikin likitocin ne ya tsaya yana yi mata bayani kamin ya bata izinin shiga,
Da sauri Dr. Salamatu ta nufi ďakin su kuma matan dake tare da ita suka samu guri suka zauna.

*******

Zaune take sanye da k'ananan kaya idanunta sunyi wani fari fatar k'aramin bakinta ta bushe sai faman sauke ajiyar zuciya take,
Babu abinda take ji sai tsanar kanta,
A hankali ta kai hannunta a baki ta shiga cizon akaifarta, jin an taɓa kofa yasa ta juyo tana kallon kofar,
Dr. Salamatu ce ta shigo rungume da hannayenta fuskantar shakaf da hawaye, cijin sayyayiyar murya ta kalleta tace
“Minal My child...”
Juyarda fuska Minal tayi “Dan Allah Mummy ki fita i don’t want to see you anymore”
Sauke hannayenta tayi ta nufota tana faɗin “Minal ina son ki-”
Hannu ta ɗaga mata tun kamin ta k'araso kuda da ita
“No Mummy i don't want to understand i hate you karki zo kusa dani”
Cikin tsawa take maganar tana k'ok'arin saukowa saman gadon,
Da sauri tayi baya tana matsar kukan dake son fito mata,
Dai-dai lokacin Saif ya shigo ɗakin yanayin yadda yaga Dr. Salamatu yasan ba lafiya ba, sai da ya kalli Minal sannan ya sake kallonta yace
“Yaya jikin nata?”
Ba tare data kalleshi ba ta bashi amsa,
“Better”
Kai ya gyaɗa ya ɗan kalli Minal da itama shi take kallo....
Cikin tsoro Dr. Salamatu tace “Minal zaki sha tea.?”
Tsawa ta katsa mata kamar mai faɗa da yarta “Bana so bana son ganin ki ever again miyasa kika kawo ni asibiti miyasa? miyasa kika ceci raina baki barni na mutu ba?”
Cikin kuka da sanyin murya Dr. Salamatu tace “Because I'm your mother bazan iya kyale ki ki mutu ba”
Kai Minal ta girgiza tana hawaye
“No you are not my mother ke ba uwata bace stay a way from me”
“I'm your mother Minal no matter what I'm still your own mother nice na haife ki Minal”
Dr. Salamatu ce take maganar tana nuna kanta hawaye na mata zuba,
Tunda Minal ta soma maganar ya lumshe ido yana ɗan cizon baki, sosai yake jin kalaman sunyi mashi girma,
Ya tsinar fuska Minal ta shigayi tana haɗiye yawu da karfi kamar mai shan maɗaci, ta tsire baki ta kalli Dr. Salamatu tace “Ke ba uwata bace ke... -”
Tasss Saif ya wanke mata fuska da mari tun kamin ta k'arasa maganar da sauri ta dafe kunci tana kallonshi,
Baki Dr.Salamatu ta rik'e tana kallon Saif da k'arfin hali irin nashi.
[9/13, 11:19 PM] Auntie Candy: BABBAN GORO...!

NA

KHADEEJA CANDY


Episode___3

Cikin wani irin ɓacin rai Minal ta zaburo masa
“Who do you fucking think you are da zaka saka kazamin hannunka ka mare ni?”
Saif kamar jira yayi cikinta da matsifa
“Quiet silly little stupid girl taya zaki rik'a fadawa Mahaifiyarki waɗannnan kalaman bakisan darajar iyaye ba ko or maybe baki da hankali”
Da karfi tace
“Nayi ni ba mahaukaciya bace nayi saboda ina da damar yin haka get the hell out of here here”
Zai sake magana Dr. Salamatu ta rik'e mashi hannu
“Ka barta tayi duk abinda take so tana da damar yin duk abinda take so”
Cike da mamaki Saif ya kalleta
“Kinsan abinda kike faɗa kuwa yarki ce fa ke kika haifeta ba ita ta haife ki ba ko dai kin manta ne?”
“Please Saif let her b thanks for the Concern”
Taɓe baki yayi ya janye hannunshi daga rik'on da tayi mishi ya juya ya fice,
Yana fita Dr. Salamatu ta nufo Minal tana bata hak'uri
“I am so sorry dear i.. -”
Hannun Minal ta ɗaga mata hakan yasa ta kasa k'arasa maganar...
“You too Mom please just go”
Yatsanta ta shiga murzawa “Please Minal ki fahimceni mana banyi hakan dan na cutar da rayuwar ki ba nima bada son raina hakan ya faru ba inason ki kwantar da hankalinki nayi miki bayanin komai”
Hannu Minal ta kai ta danna wata yar karamar ɗanja ja dake gefen gadonta, nan take ɗakin ya ɗauki k'ara cikin mintunan da basu fi 3 ba likitoci suka shigo tare da nurses,
Dafe kai Minal tayi tana kallonsu
“Dan Allah ku fitar dani daga nan bana son ganinta”
Da sauri wata daga cikin likitocin wadda nake zaton bahaushiya ce ta kalli Dr. Salamatu,
“Dan Allah Hajiya ki ɗan bata guri for now tana muna bukatar natsuwar ta”
Kai kawai Dr. Salamatu ta ɗaga ta juya ta fice tana hawaye,
Tana fitowa wata daga cikin matan dake tare da ita ta dafata tana tambayar lafiyar Minal,
Kasa magana tayi saboda kukan da ya ci karfinta, nan suka shiga tambayarta ko lafiya duk hankalinsu ya tashi,
sai da tayi mai isarta sannan ta share hawaye ta ta ɗauki Jakarta tana faɗin
“Babu komai Minal kuma taji sauki”
Tana kaiwa nan ta nufi hanyar fita su kuma suka rufa mata baya,

A k'ofar Emergency suka tararda Saif tsaye kamar mai jiran fitowarsu, Tsayawa Dr. Salamatu tayi dai-daishi sannan ta kalli matan dake tare da ita tace “Kuje gurin mota”
Ba musu suka nufi gurin motar
Sai da suka fice sannan ta kalli Saif zatayi magana ya rigata
“I'm sorry to ask you miyasa yarki ta tsaneki kuma tayi kokarin kashe kanta?”
Wani dogon numfashi taja tare haɗiye wasu yawu da karfi
“Kace wai Mr President na gode sosai da kulawarshi kuma kace taji sauki ina mika mashi gaisuwar ban girma”
Bata tsaya jiran abunda zai sake cewa ba tayi tafiyar ta
Ajiyar zuciya ya sauke ya ɗaga kafaɗunshi,
_Toh wai miye na damuwa da sanin dalilin koma minene ai can su suka sani nidai nayi abinda ya kawo ni_
A zuci yayi wannan maganar yasa hannayenshi aljihu ya fice.


MINAL....
Sai da suka tabbatar da hankalinta ya kwanta sannan suka fice suka bar mata wata nurse guda ɗaya, tana haɗa mata tea,
“Please brought borrow me your phone”
Ta tambaya tana matsar gurin da akayi mata karin ruwa,
Juyowa nurse ɗin tayi ta kalleta tana murmushi tace “OK but you should drink this tea first”
Ta k'arasa maganar tare da mika mata tea ɗin, ba musu ta karɓa ta kai baki, sai da ta shanye shi kaf sannan ta dire kofin tana shafe bakinta,
Hannu naga nurse ɗin tasa ciki aljihu ta ciro wayar ta mika mata, da sauri ta karɓa tana mata godiya "Thank you”
Murmushi Nurse ɗin tayi “Your welcome”
Sannan ta juya ta fice,
Wasu numbers Minal tasa guda goma sha ɗaya sannan ta danna calling.
Ringing tayi har ta katse ba'a ɗauka ba nan ta sake bugawa,
“Com-on pink the call pink the call”
Abinda take faɗa Kenan tana yarfar da hannu,
Sai da ta kusa katsewa sannan aka ɗauka cikin rawar murya ta soma magana
“Hello Deen ina asibiti yanzu haka”
Shiru tayi can kuma tace
“I need to see you Deen urgent”
Banji mi aka ce mata ba na dai ji tace
“Ok”
Ta kashe wayar,
Ido ta tsurawa tana shafa gashin kanta,

27 MINUTES LATER.......


Read / Download BABBAN GORO

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album