Join Our WhatsApp Group

YAR AIKIN KARUWAI Book 2 Complete Hausa Novel Document by YAR AIKIN KARUWAI Book 2


YAR AIKIN KARUWAI Book 2

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 158967



YAR AIKIN KARUWAI Book 2

Reading Time: 13 Hours

Added On: 27, Oct 2023

Author: Asma Baffa ,

Ebook Compiler : ZAINAB BUTALAWA

Author Group : Unknown group

Author Phone : O8061929616

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 792.66 kb

File Type: txt

Views: 2805+

Download: 2632+

Last download: 5 hours ago

Description/Story: [8/9, 10:59 PM] +234 806 192 9616: 🌼'YAR AIKIN KARUWAI 2🌼
(MATAFIYA)



GARGADI GA MASU AUDIO WANNAN LITTAFIN NA RIGADA NA SIYAR DA SHI GA MASU SATA SU MAIDA SHI AUDIO BAN YARDA BA BAN AMINCE BA

COPY BY ZAINAB BUTALAWA


Official

By
AsmaBaffa


SADAUKARWA GA
ZAINAB USMAN



Ina masu bukatar unique kitchen utensils . fabrics adult and children's wears shoe's and bag's.
Da masu bukatar ahada musu lefe ko masu bukatar iya luggage's din kawai duk inkazo
R&U EXCLUSIVE KITCHEN AND MORE.
Zaku samu duk abinda kuke bukata ko a awanne state kake zaa kawo

Masu bukata ga number. 0703 455 9202

https://chat.whatsapp.com/LAizQA6PofSLoFhQ7XeaQx



Page din nan da
AIDA MAMAN TASNIM
Zai bude, nata ne 'yar Albarka.


Gaisuwa ga
AUTARESS tawa






Lokacin da Suka tsaya a mota an wuce gamborin gala dake Maiduguri anyi nisa an nutsa ana ta wuce kauyuka masu hatsari, Rufaida ce ta Fara dirgowa daga cikin mota wacce da ganin Kalar motar tayoyin kadai kasan suna bin Sahara gata Samanta a bude yake Kamar akori kura amma katuwa ce motar idan ana ruwa sai dai a lulluba musu tempol,ga Rana ana kwalawa,tace Kaka dirgo kaima Kar zafi ya kashe min kai mu dai ko Makkah ko kafar katako,Makkah ko a buhun kunama sai munje Inshaallah ba gudu ba ja da baya,mutanen motar ne Suka firfito Dan guzirinsu na ruwa da na ci suka Fara Dan gurgura,Kaka yana gefe Rana ta ishi tsoho yace Jikalle dakko mana ruwan muma mu jika makoshinmu,baki Rufaida ta zumburo tace tun yanzu sai ka shanye mana guzurin ba a san ranar tashin motar nan ba fa,Wani matashi Wanda bai da aiki sai kallon Rufaida Kamar maye yace ke da Allah ki bawa bawan Allah ruwa ya Sha ke wacce irin azzaluma ce ne,Cele tace kaci darajar a hanya muke cikin Niyyar shiga Makkah nake bazan ce komai ba,Ido matashin ya zaro yace yau naji fitsararriya rashin kunya Zaki min,Kaka ne yace in Banda shishiginka Ina ruwanka da ita,matashin yace haka ma zaka ce na barku ta kasheka yace naji dan ubanka jikata ce fa matsiyacin yaro.
Ana haka Kawai mota ta tashi Rufaida ta kwarara ihun murna tayi tsalle tare da fadawa motar tace Kaka Miko hannunka,tsoho ya taka da kyar tana taimaka Masa ya shiga shima Suka zauna sannan ta dakko ruwa ta bawa Kaka ya Sha sosai ta mayar Bayan ta Sha itama,Chin chin da Tayo da meet pie na guzuri suna tafiya ita da Kaka suna ci tana kallon mutane dai in ka cika kallonta ma Sai tai maka gwalo Wai su kayan dadi suke ci,suna gama ci ta ebo dabino Suka ci sabo dabino Yana rike cikin matafiyi ko yaya kaci sinadarinsa Yana rike mutum na wani dogon lokaci,suna tafiya sai da dare yayi sosai Suka karasa wani kauyen suna murna za a huta amma Agent din ciki wacce tana gaban mota da wasu maza biyu Suma suna gaban mota Suka ce ba a tsayawa a wannan kauyen hatsari ne da shi kuyi Addua ma mu wuce lafiya,Rufaida aka jawo carbi ana hailala da istingifari tana cewa Allah ka tsallakar damu Allah Makkah ko a buhun barkono ne ka kaimu.

Suna tafiya a garin suka iske gawarwakin mutane birjik a gefen Hanya an karkashe su gasu nan,Cele ta tsorata da ganin gawar mutane birjik bata taba gani ba,suka ci gaba da tafiya har dare yayi sannan Suka zo wani kauyen da shi kuma ana yawan ruwa ba a tsayawa a wajen ruwa sai ya shanye motar gaba Daya su kansu mutanen wajen a saman dutse suke Kan tsauni,ana sauri za a bar wajen ruwa ya kece me karfi gashi ba batun ma a rufa musu tempol Dole sakkowa sukayi da yawansu sosai sabo da shake suke dam a cikin motar wasu sun iya daukan guzirinsu wasu basu iya dauka ba,ga wata Mata harda danta karami a baya dan wata uku,Agent dince ta karbar Mata yaro sannan ta sakko daga motar Suka hau gudu suna gudun tsira,Kakan Cele ya Fadi ya tashi Cele ta daukar musu guzirinsu ta Goya jakar a baya,suna gudu Kaka ya sake faduwa ta dawo ta dagashi ta taimaka Masa Suka ci gaba da gudu Allah yasa Cele Riga da wando ta saka amma rigar iya gwiwa, sai da Suka Yi tafiya me uban Nisa sannan Suka samu saman tsaunin da zasu fake,sai lokacin aka tuna da wata tsohuwa tukuf,aka dinga tambaya Ina Baba Ina Baba,Cele tace ai kuwa an barta a mota,sai da ruwa ya tsagaita Agent da driver da maza Uku Suka koma wajen motar tasu wadda ruwa ya shanyeta gaba daya,Baba suka hango Allah yasa iya kanta ne ruwan bai shanye ba,Suka Yi dabara aka dakkota.

Suna dawowa inda su Cele suke aka hau jinyar Baba Kamar zata mutu ana so ruwa ya tsotse na Hanya su samu su iya fitar da motarsu daga cikin tabo,sai da Suka kwana biyu a saman tsaunin duk sun fita a hayayycinsu ga ruwa ga sanyi sai da suka samu ruwan ya dauke sannan mazan suka dinga canja kaya dama jakan kayansu duk ta Leda ce wacce ruwa bazai Shiga ba,Sauran matan Suka dan fake daga Bayan tsauni Suka canja Kaya Suka shanya kayan jikinsu,Cele tana zagawa zata canja Kaya maza wasu samari suka dinga leka ta,tana daga Riga Suka yi Ido hudu da wani matashi Mustapha nan take tace uwarka ka kalla Mustapha shege me idon ungulu Mustapha ya koma inda yake da sauri,Agent ta hau zaginsu tana dura musu ashar sannan Cele ta samu ta canja wasu riga da wando t-shirt fara da jean blue duk a gwanjo ta siyo abinta sabo da tunanin tafiya irin wannan sai da Riga da wando,cikin Yan matan wata Wasila tace kin huta wallahi Rufaida da nasan haka tafiyar take Nima duk kana nan Kaya zan kwaso,Cele tace ai ni Nan da Kika ganni akwai maths Ina da tunani da lissafi kayansu duk ya Fara bushewa sabo da rana ta kwalle,a ranar Kuma Baba tsohuwa da ake jinyarta Allah ya karbi rayuwarta suna sauri sai mutanen yankin Suka samu a ciki akwai musulmai sosai Suka Basu Gawar Baba suyi Mata sutura su binne ta,suka koma motar tasu kafin ta tashi sai da Suka yini tun safe suke abu Daya sai kusan dare sannan ta iya tashi,bayan ma ta tashi fitar da ita daga tabon sai da Suka hadu aka turata sosai sannan Suka tafi,Cele sai ihun murna take Makka ko da kafar katako ne,tace Alherin Allah ya Kai Miki Saudiyya wuuuuuu tayi tsalle ta dane bayan mota ta kamo Kaka Wanda yaji wuya cewa yake mu koma gida nidai na fasa zuwa Jikalle,Cele ta bata rai tace wlh sai dai muyi shahada a Hanya amma ba gudu ba ja da baya iya wuya sai munje Inshaallah sai munyi kudi,Abdul yace Inshaallah ai Ina zuwa shayi Zan ta Sha muryata ta washe sai kiji yalla yalla...suna dariya Awwalu yace sai kaji Muna ciniki muna Kam Kam,2riyal laa laaa kamsa riyal,suna tafiya kowa ya zaro kayan cinsa Yana ci har suna sake kwana Suka yini Sallah ce kawai ke tsaida su a wasu kauyukan.

Wise tana girkinta a kitchen Papa ya shigo a hankali ya dade Yana kallonta Yana zuba uban murmushi,yanzu sai Fushi take yi da shi bata kulashi ta maza yayi ya rungumeta ta baya,Wise Ido ta lumshe yau sati tana gaba da mijinta an dade ba a hadu ba a hankali cikin kunne Papa ya Shiga furta Mata haba my Game changer,My play maker, Heroes in my book, uhm haba my best goal assistance Allah yaci gaba da tsare min ke,Nayi kuskure ki yafe min ki taya ni da rokon Allah ya yafe min,da me zanji da halin da nake ciki ko da fushin da kike Yi dani,I love you my wife,kalaman Papa sun sanyaya zuciyar Wise ba kadan ba sunyi tasiri a zuciyarta a hankali ta juyo a jikinsa suna facing juna tace na hakura nima me laifi ce na maka karya na shigo rayuwarka badan Allah ba karshe na fada sonka,na taba karuw....shiiiii...Papa ya furta yace bana bukatar Jin komai na San komai Kuma na gano Baku da kudin da kika Zo yaudara ta da shi daga baya na hakura na aureki a haka, bana fata naji zancen kin taba karuwanci a duniya magana ta wuce Allah ya yafe mana,Wise tace na gode lokacin da idonta ya ciko da kwalla,Yana Murmushi yace mene abin kwalla kuma,Wise a kirjin Papa ta kwanta tana nadamar karuwancin da tayi a rayuwa,yace Kinga gama Mana abincin tukun yunwa nake ji rabon da naci abinci ya tsirga min tun kafin Maman Sabreen ta ballo ruwa,Gama girkin muci sai kizo kici gaba da min Shagwabar taki,lokacin da Wise ta danji kunya kenan tun shigarta bariki har mamakin kanta tayi Wai taji kunya,Papa yana fita ta kirani na daga lokacin Ina gyarawa Nawwar kayansa na sawa tace Miracle albishirinki nace goro tace yau naji kunya abin mamaki papan Sabreen yayi magana wai naji kunya,Dariya ta bani nace to congratulations,ta kashe wayar ta Kira Star dake jikin Malam a kwance suna murza juna taji Malam Abulkhair yana wani nishi,Star tace karatu yake Dora min ke Zan kira...ta kashe wayar,Wise ta bi Wayar da kallo tace shegu bari na Kira Seraline Saliha ce ita ta Kira Sera bugu Daya ta daga tana cewa Hero plate din fa daka wanke bai fita ba haka ake wanke wanken,Sabeer Yana dariya yace kin sani Shiga kitchen ni ba aikina ba,ni fa eating you shine aikina,Seraline tana dariya tace Allah ya shiryeka,Wise wayarta ta kashe tace to bari na Kama dattijona nima na hutawa kaina da Yan Iska,Iyamami an warke ras ashe an dawo da ita gida,ita bata rabo da zaga bangaren yaranta sai kace yar iska tana ji da Yamma part din Wise uban kida na tashi a speaker amma ta wani dangala kafa ta tafi wajen Wai zataje wajen danta Yusufa zasuyi magana.
Tana shiga ta iske Papa a zaune yana cin abinci Wise sai uwar rawa take tika Kamar ba gobe ta juyawa Papa mazaunai Yana kala Yana washe baki yana nishadi,Iyamami ta Shiga ko sallamarta ba a ji sai da Papa ya lura ransa ya baci wai ita Kawai sai dai ta shigowa mutum Palo ba knocking,kidan ya kashe Wise bata lura da Iyamami ba ma ta koma ta zauna a cinyar papa,sai da yace Iyamami fa,ba tare da ta tashi a cinyarsa ba ta juya ta kalleta ita kanta Wise tana Jin haushin abinda tsohuwar take mata,kin tashi tayi ta kwanta a jikin Papa sannan tace Ina yini Iyamami,tsohuwar Hannu ta shiga tafawa tace ke mayyar maza dama ance cikakkiyar karuwa ce gashi Kuwa idona Yana ta gani,yanzu idan ba tambadewa ba Kamar Papa babban mutum Wanda ya haifeki ki zauna kina uban murguza Masa tuwon duwawu a gabansa kina karkada su wato harda tura Masa ya gani ke ga tabbatacciya, yanzu idan a Zamanin mu ne yaushe za ayiwa Yusufa wannan iskancin ai sai kunya da kunya amma Kai Yusufa laifinka ne Kaine ka bata Fuska ta rainaka wannan raini ne,da yarka kamar Sabreen ko kunya baka ji,Kuma ta ganni na shigo tayi zamanta ma a cinyarka daram wato na gani da kyau Kuma a haka ta gaisheni ba rusunawa ba komai wato na haifar Mata yaro a banza ko Kai Kuma sai wani gyada Kai kake yi Kamar na jinjirin jaki.

Wise tace Iyamami kiyi hakuri mu ai zamaninmu daban da naku Kuma Banga shigowarki ba irin waje na Yara ai ba a shiga da ka haka sakaka idan da tsirara muke fa ai Kinga bai Dace kiga inda danki yake Shige da fice ba ko ni bazan ji Dadi ba ki kallar min Antainarsa ba sabo da kin Gama kallon rabonki lokacin da Kika haife shi har ya balaga yanzu hurumina ce ni kadai ya kamata na gani,Iyamami salati ta saki kamar me Aljanu tace karya kike karuwa baki Isa ki mallake min Dana ba Kuma sai an sakeki,Papa yace Dan Allah Iyamami ki ja girmanki bazan ji dadi ana fada Miki magana ba ba tsari Kuma ke Kika jawo,Kuka Iyamami ta saki tace shike nan ku kashe ni ku huta wayyo jama'a kuzo mace tafi uwa wayyo Allah laaaaaaa mace tafi uwa Yusufa ka nemi Albarka,nayi tur da Allah wadai da wannan auren,bazai Albarka ba ta juya tana bazai Albarka sai ka saketa,Wise ta kalli Papa Wanda ya zuba tagumi yace shike Nan Iyamami ta kwashewa auren nan Albarka Ina tsoro Kar masifa ta kunno Mana,Wise tayi Murmushi tace Inshaallah zaiyi Albarka ni Wise na sa Masa albarka,bari naje na lallashe ta,yanzu a Fushi take ko kaje ma sake kwashewa auren Albarka zata yi Kawai muyi Mata Addua Allah ya ganar da ita idan ta huce sai muje tare mu bata hakuri ai uwa ce tafi gaban wasa,daganan Suka fara tsotsar juna suna murza juna har zuwa bedroom Suka fada saman bed, Papa Yana Mata rada suna dariya kasa kasa.

Nawwar yana kwance a jikina saman bed Ina zaune a tsakiyar bed dinmu jingine nake da jikin gadon Mami ta Kira shi ya kashe tare da kiranta back,yace Mamita ta kaina yau sati biyu da Iddar ki Ina murna Mami,karka dameni cewa nayi zanyi aure a nan kace no to ya kake so nayi balarabe ne dan Yemen Ina sonsa gaskiya,Nawwar yace Mami kede kice kyau ya rude ki Kawai gaskiya Ina taya Baffa kishi wani zai aure Masa mata,wallahi Mami larabawan nan karfin sha'awa gare su Basu San hakuri ba Kar ya kashe min Mami,zanci ubanka Nawwar ni sa'arka ce kafa dameni Ina ruwanka,dariya yayi yace Mami Ina jiye Miki wlh tam Ina nan zaki min waya kice an sakeki larabawan Yemen ko Kuwait ba sauki,Tsaki Mami ta ja tare da kashe wayarta ta Kira Yan uwanta ta sanar musu ta samu mijin aure Mahmood Suka Mata fatan alheria.
Ni Kuwa Ina Jin Nawwar suna magana da Mami ya gama bance kala ba waya nake dannawa Muna chat da Star akan magungunan gyara Oven Ina dariya ni kadai sabo da iskancin Star ya isheni,tace wai maganin da na baki ki gwada sunansa Memory ba irin kidan da Nawwar bazai Kama ba,tace yau akwai kida Nawwar ba bacci,makwafta ma Sai sunji kidan da Nawwar ke ji,voice na Mata nace baki ga bakina ba Dan karami can ma wajen haka yake ance da ganina kin San da lafiyata,Voice ta min itama tace zo kiga Malam na goge Masa hadda wlh karatu ma ya daina yanzu Sam sai karatun Antaina,Nace Nawwar yace ku dawo makaranta wlh gobe kullum sai...


Read / Download YAR AIKIN KARUWAI Book 2

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

2 Comments On YAR AIKIN KARUWAI Book 2
avatar
zainab-ibrahim-8

2 months ago

Reply

Thank

avatar
ghh

1 month ago

Reply

Replying to zainab-ibrahim-8

Yayi kyau?

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album