Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

ZULFA Complete Hausa Novel Document by ZULFA


ZULFA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 78144



ZULFA

Reading Time: 6 Hours

Added On: 22, May 2023

Author: Aysha Ya'u Kurah ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 420.66 kb

File Type: txt

Views: 5602+

Download: 6313+

Last download: 16 hours ago

Description/Story: : ●● ZULFAH ●● 1⃣
By Aysha Ya'u Kurah

Dare ne mai cike da dumbin rahama, kowa na cikin gidanshi sakamakon Ruwan da ake tsugawa, masu abin hawa suna ciki, masu tafiya a kafa da mashin sun fake saboda ruwan yinshi akeyi kamar da bakin kwarya, ma'aikatan dare suna wajen aikinsu,
A wannan lokacin zulfa'u na cikin ruwan tana wanke kwanukan da aka ci abincin dare a gidan, yawan ruwan da akeyi baisa goggo marka ta tausaya mata ba, yayin da ita kuma take dakinta na kasa, kan rubabiyyar katifarta, rushi ne a gefenta suna shan dumi ita da yarta Salaha, can gefe kuma mahaifin zulfa ne zaune yayi tagumi yana leken yarshi dake faman aiki cikin ruwa, zuciyarshi na zafi amma bashi da yadda zaiyi saboda marka ta fi karfinshi, Allah Allah takeyi ta gama ta shiga dan karamin dakinta da bai wuce taku shida ba, tana gamawa ta gyara gurin da sauri saboda ruwan kamar dada ingizoshi akeyi, tayi maza ta tsaya bakin kofar dakinta ta cire kayan jikinta saboda kar ya jika mata daki dama ga dakin ba kofa ruwa duk ya jika kofarshi, matse kayan tayi ta shanya a saman kwanonta, tasa wasu yagaggun kaya da suka zaizaye saboda tsufa, da sauri ta hau kan katifarta wacce bata da maraba da tabarma, yunwa sosai take ji dan ragowar da take samu ma yau basu rage ba, gara ma na kabiru yayan salaha ya dan rage kadan saboda ta samu, amma saboda tsabar ta kosa taji muryar dake debe mata kewa tasata bacci cikin farin ciki, muryar dake sata manta ko wani irin bacin rai yasa ta share yunwar da takeji, ta dakko redionta da gurin kunnanawan a cire yake, in ka ga radion bazaka taba cewa in an kunna zaiyi aiki ba, kibiyarta tasa ta kunna shi, cikin zakuwa ta kamo tashar liberty ta kure muryar radion dan battery ya kusa mutuwa, ta tura kanta cikin zaninta ta kara radion a kunnenta, saura 5mints takwas tayi, ta dinga sauraren wakokin da akeyi, takwas dai2 taji ansa sassanyar waka mai tsuma zuciyar masoya, lumshe idonta tayi saboda tasan taken isowar gwaninta kenan, kara gyara kwanciya tayi ko kadan sanyin da takeji ya gushe, muryar "Abubakar sadiq marafa" ita ta daki dodon kunnenta cikin salonshi na isa da kasaita, salon dake burge dubban mata masu aji dake cikin garin kaduna da kewayenta, sallama ya fara yi cikin harshen hausa da larabci, ya mika gaisuwa gurin masoyanshi da turanci, sannan ya fara programme dinshi cikin harshen hindu (indianci) cikin kwarewa yake gabatar da program dinshi, duk wata mace da ta isa a duk ranar friday to tana manne da radionta tun takwas har tara na dare, wasu ma da radion suke fita tadi saboda gudun kar a barsu a baya, ko wata shida sadeeq marafa baiyi da fara program dinshi ba amma saboda kwarewarshi da yadda mutane ke sonshi zaka rantse tunda aka bude gidan radion yake aiki a gurin"""!,

kasancewarshi mutum mai girmama soyayya da son yanayi na damuna yasa aka kayata mishi wannan daren da wakoki masu sanyaya zuciya, karfe 8:40 bayan ya kammala da gabatarwa, ya rage amsa tambayoyin masoya, tambaya uku kadai yace zai iya amsawa a ranar saboda yana son yin bankwana da masoyanshi, gaban zulfa ya fadi hankalinta ya tashi, ta yaye xanin da ta lulluba dashi saboda wani gumi da taji ya keto mata"", cikin taushin murya zee gayu ta fara wurgo mishi tambayar farko, tace tambaya ta farko ta fito daga gurin "Salma Ibrahim, " tambayar da akullum sai MARAFA ya amsata babu mamaki malama salma bakuwace a cikin wannan shirin namu, tambayar itace shin sadeeq yana da aure,,, dariya sadeeq yayi saboda yadda zee ta karasa maganar yace zeee kenan, malama salma bani da aure, sai dai kuyi min fatan samun mace ta gari kuma kamila, zee tace bakayi niyya ba dai ga mata nan kamar zasu ci kansu, murya can kasa saboda kar masu sauraro suji yace zee ban hadu da muradin raina ba har yanzu, ya lumshe idonshi yana siffanto irin macen da yakeso tun yana yaro, zee ta bude murya da karfi tace to masu sauraren mu marafa dai yace bai hadu da muradin ranshi ba har yanzu, sai ku tayashi addu'ar samu nan kusa, in kuma wacce zata kasance muradin ran nashi tana sauraronshi to sai tayi fatan Allah ya hada ta dashi komin daren dadewa, zo kuga mata a gidajensu yadda suke amsa ameen, zulfa ta share kwallar dake idonta, dama ita tasan bazata taba haduwa da sadeeq ba, saboda yayi mata nisa sosai yafi karfin ajin mace marar galiho da gata irinta, amma muryar dake sata manta bacin ran da ake mata a gida yau zata ma kunnenta bankwana, , to saboda me zaiyi bankwana?? Ta tambayi zuciyarta, kafin ta samo amsar tambayar har ya gama amsa tambayoyin, cikin taushin murya yace zanyi bankwana daku masoyana, zan ajiye wannan progrm din saboda bukatar hakan ta taso, ina rokonku da duk wanda na taba batawa a rayuwa ya yafe min, na yafe ma duk wanda ya bata min, wadanda basu sanni a fuska ba ina adduar Allah ya hada mu daku a aljanna firdausi, nagode da kaunarku Allah ya kawo wanda zai maye muku gurbina, a karshe ina bukatar addu'ar ku akan Allah ya taimakeni ya bani nasara akan abin da nake nema, nagode, nagode Allah ya barmu tare,,, wakace ta cigaba da tashi a kunnuwan masoyanshi dake kuka, zulfah ta wurga radion bayan yagalgalalliyar jakar kayanta ta shiga kuka baji ba gani, daren da ya kasance mai cike da sanyi da dadi ga ma'abota soyayya, ya kasance dare mafi zafi da kuncin a gurin baiwar Allah zulfah....

Mrs tijjani shattima ...
[15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ●● ZULFAH ●● 2⃣
By Aysha Ya'u Kurah

Washe gari tun biyar na asuba ta farka duk da ba wani isashshen bacci ta samu ba, tsakar gida ta fito taga tulin kayan wanki a kofar dakinta kayan goggo marka ne da na salaha, ta kalli kayan cikin faduwar gaba saboda yawansu ga danshin damina, ga kanta na masifar sara mata saboda rashin bacci da bata samu ba, ta zauna ta buga tagumi da buta a gabanta tana tunanin irin rayuwar da take ciki tun bayan rasuwar mahaifiyarta tana yar shekara goma take aikin bauta bata da wani lokacin farin ciki kullum tana cikin wahala, bata ko samun isashen abinci, wannan dalilin ne yasa ko da yaushe in kaga zulfa bata cikin walwala, bata kula kowa koda a makaranta ne, magana mai yawa tana yi mata wuya, in tayi magana ko kai wanda take ma maganar ba lallai bane kajita saboda tsabar sanyin maganar, tasha dukan asara gurin goggo saboda yanayin maganarta amma duk da haka bata sauya zani ba, saboda babu wanda zai iya canza nature, rankwashi mai karfin gaske shi ya katse mata tunanin da ta keyi, tayi maza ta sauka daga kan dakalin da take rike da kanta, goggo tace uban me kika zauna kikeyi agurin nan, duk ga ayyukan gidan nan babu ko daya da kika fara saboda tsabar iskanci da lalaci, to bari kiji kinga wannan wankin wallhy kika kuskura gari ya waye baki gamashi ba sai nayi mugun saba miki shegiya mai suffar mayu, ta wuce gurin kullun wainarta ta na masifa kamar zata ari baki, makota sun riga sun saba dajin muryar marka me waina a ko wace safiya, bare mahaifin zulfa malam ado da abin ya zame mishi jiki kuma bashi da yadda zaiyi ya fitar da yarshi daga cikin bautar marka, shiyasa a ko da yaushe yake fata da yi mata adduar samun miji tayi aurenta ta bar gidan, ya kudura a ranshi ko dan garuwa ne yazo neman aurenta in dai zai dauke mata ci da sha wallhy zai bashi, zulfa ta idar da sallah tayi yan adduointa, ta fito da sauri ta dauki katon bokitin penti ta shiga jido ruwa a mono din dake masallacin layinsu Allah ya taimaketa babu layi saboda gari bai waye ba,,,
saleem dan limamin unguwarsu kuma malamin islamiyyarsu shi ya ganta tana diban ruwa bayan ya fito daga sallah, cikin tausayawa ya karasa gurin mono din, tanata bugawa tana haki taji sallamarshi tayi murmushi a hankali tace ina kwana malam, lafiya lau yace mata yana kokarin fara tayata buga panpon, tace ka bari malam nama gama wannan shine na karshe, bai saurareta ba saida ya gama cika bokitin, ya sa hannu zai dauka ta rike gefen bokitun tace dan Allah malam ka barshi kar in baka wahala, kallonta yayi yace saki bokitin ki wuce muje, batayi musu ba ta saka suna tafe har suka kai kofar gidan, ya ajiye
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download ZULFA

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album