Join Our WhatsApp Group

MASIFAFFAN NAMIJI Complete Hausa Novel Document by MASIFAFFAN NAMIJI


MASIFAFFAN NAMIJI

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 157308



MASIFAFFAN NAMIJI

Reading Time: 13 Hours

Added On: 05, Apr 2024

Author: Janafty ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 841.59 kb

File Type: txt

Views: 212+

Download: 331+

Last download: 2 minutes ago

Description/Story: *MASIFAFFAN NAMIJI..!*

*Wattpad:Jamilaumar351*

*DEDICATED TO:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi...!*

_Bismillahir rahmanir Rahim in the Name of Allah,The Most  Beneficent The Most mercefull Praise be to Allah Lord of The Words..._

*001*

*ZARIA..*
Area:Tukur-Tukur...

'"Hafsah!...Hafsah...!Hafsah...! sunan danaji Megidana Abdullahi na Tsagamin shi da Asuban fari,wanda hatta mazan da suke wucewa ta kofar gidanmu in sun dawo Daga masallaci suna iya Jiyo kwakwazon Kiran Sunana da Abdullahi keyi muryansa Kakkausa kamar zata tsaga gidan.

Kaina na Dafe ina Daga Durkushe acikin karamin Kichen dinmu Dake tsakar Gida Ina Faman kunna Risho sai na kunna Lagwanin sai ya mutu da kanshi Tun Wajen 6 da wani abu na safe na Fito ina idar da sallar Asuba ban ma yi Tunanin komawa ba Saboda yau din Litini ne farkon Sati Su Amira nada Makaranta kada su makara Abdullahi ya Dora Laifin akaina Tunda tare yake Wucewa dasu in zai tafi aiki Bisa Mashin Dinsa mai Suna Wayyo Kudina.

Saurin Mikewa nayi Jin kiran yafara Kusantoni kada na Kular Dashi dogon Sikat din Jikina na gyara Lokaci daya da Hijabin danayi sallah wanda ban cire ba Jin garin yau din an Tashi da sanyi sanyin Damuna dayake Jiya an kwana Tsala ruwa,ina kokarin Shiga Dakin muka ci karo Dashi zai Fito,Da Sauri nayi baya ina Raba Ido Cikin Kulufuwa da Takaichi yake Jifanta da wani kallo kafin ya Daga Murya yana Fadin"Wani sabon Iskanci kuma kika samo Hafsah..!?

Muryanta cikin Sanyi nace"Name fa Abban Amira..? Harara ya wurgamin yana Fadin''Bansani ba..Nace bansani ba bandama Salon iskanci kira nawa nayi miki Tun ina Daga cikin Daki baki amsa ba sai da na Fito..? Yafada yana wani karkace tsayuwa Cikin Jin Haushinta,Ajiyar Zuciya ta sauke kafin ta kada kai kawai ta wuce shi Zuwa Cikin Dakin bayanta yabi yana Fadin"Hafsah ina mgana kina Tafiya..? Yafada cikin Mamakinsa.

Atsakiyar Falon Taja ta tsaya tana Fadin"A"a kayi Hakuri ba Tafiya nayi ba na Shigo Daki ne kada makota su jiyo Fadanka,mganar kuma Kira banji bane Lokacin danaji na amsa kenan zan taho Dakin sai ga ka kayi Hakuri.."Tafada Cikin Sanyin Murya Kawai Tsayawa yayi yana Kallonta cikin Fada,sai yanzu na karemai kallo Dogon Namiji ne mai Cikar zati da kamala mai Fadin Kirji da cikar Cikakken Da Namiji mai iko Ba fari bane ammh Wankan Tarwada ne,Fuskarsa bata da Tsawo sosai sai dai tana da Fadi kadan Hancinsa Dogo ne Turbarkallah Masha Allah Sajensa daya zagaye bakinsa shi yake karamai kyau da Kwarjini.

Abdullahi Usman Direba kenan Dan Misalin Shekaran Haihuwan 32 da biyu Aduniya Mai iko ne kuma mafadacin Namiji ne ga iyalansa bai da sauki ko kadan Ballatana Ragowa a kallan Farko in kayi mai bazaka taba Zaton Abdullahi ya iya Fada ba ammh Ranar dakayi katarin zuwa gidansa nan zaka ga Abunda ake Kira Tijara da kudinka Sai kayi Mamakin Dama Abdullahi na iya Dogon Mgana ne..?haka yake baka iya yankema Abdullahi Hukunci ga Dabi"unsa matarsa Hafsah ce kadai Zata iya Fadar Wanene Abdullahi 90%Cikin Halayyarsa wanda Mutane basu sani ba,sai yan"uwansa makusantansa.

Numfashi ya Sauke Lokaci Daya yana Fadin"Eh Lalle wato kada makota Sujiyo Fada na ko Hafsah..? Wato ga mafadaci ko..? Yo in gaskiya kikeso Uban wa ke sani Fadan in bake ba.Kullum kwakwalwarki bata Daukan Mgana Koda yaushe sai dai adinga nanata miki Mgana Daya,ko karatu ya isa ki gama Haddaceshi acikin kwakwalwarki ammh Ina baki da Buri illah Kiga Ina Mgana Shine Burinki sai anyi Mgana kiwani Langwabe kai kamar Wata marainiya kina Sharan kwallar karya.."Yafada yana kallonta tana goge kwallarta da gefen Hijabinta,Bata dagoba ta kara kwantar da Murya tana Fadin"Allah ya baka Hakuri.."

Tsaki yaja yana Fadin"Ameen...Sai ana mgana ki wani fama ma mutane kuka kina wani Allah baka hakuri"yafada yana kwaikwayan Muryanta cike da Haushi ita dai bata Dago ba kanta na kasa tana kallon Center Capet din Dake tsakiyar Dan madaidacin Falon nata wanda yaci Kujeru saiti Daya mai Dauke da Karama Mai zaman mutum biyu Guda biyu da kuma Mai zaman mutun uku guda daya na kuma mai zaman mutum biyu,Babu komai daga kujerun sai Tibin Bango Plasma dake kafe a bangon Dakin,wanda ya samu mahadin Dish din da suke kallo Dashi..

Hannu ya yarfa yana Kallonta yace"Kinga Malama ni ba Hayaniya na Fito nayi dake ba ina Takarduna wanda na Dawo dasu gida Daga wajen aiki Ranar Jumma"a saman Madubinki na ijiye kuma yanzu nazo zan Dauka bangani ba.."Cikin Sanyin Murya ta wuce Cikin Bedroom din tana Fadin"Suna cikin Dorowan gado ni na Dauke da zan gyara Dakin Jiya.."Binta yayi abaya Cikin Fada yake Fadin"Kinji ko..?kai Hafsah wai ke Wata irin macece..? Sau nawa zan gaya miki kidaina Tabamim kayana ko wani abu nawa in na ijiye da Hannuna Ehe..?

Yafada yana Tsareta da manyan Idanuwansa kamar ya maketa Baki ta saki kafin ta Bude tana Fadin"Haba Abban Amira ina Laifina anan?,na dauke maka ne saboda kada Amira ko Amir su dauka su bannata maka.."Tafada Cikin karya Murya Wani Dogon tsaki yaja yana fadin"Na sakaki..? Ki barsu su bannata mana bani na ijiye ba..? ko kinfini sanin akwai su Amiran ne..? Nifa wannan Sanaben naki sam baya Burgeni Hafsah in ma zaki chanza Ki chanza Tunkafin dare yayi miki,Dillah Malama daukomin Takarduna zan Fita dasu ne..!

Yafada yana Yarfa mata Hannu batayi musu ba ta Juya Ta Bude Drower din gadon ta Daukomai Takardun ta mikamai bayan ta Ramkwafa Fizgewa yayi cikin Fada yana Dubawa Zuwa chan yace"Allah ya Soki Wlh da wata Takarda ta bace sai kin Raina kanki..Daga yau sai yau karki kara Tabamin kayana Daga inda na ijiye am i Clear..? Yafada yana Taba kunnansa Numfashi ta Fesar tana Fadin"Naji insha Allahu haka bazata kara Faruwa ba.."Bai kalleta ba yawuce gefen gadon yana zama ita kuma ta Fice tana kada kai.

Kichen ta koma Sai lokacin ta Duba taga ba Kalanzir ne Da Sauri Ta Daga glan din kalanzir din nasu taji ba komai sai da gabanta yafadi sanin Halin Abdullahi yanzu kan mganar ba Kalanzir sai Ranta ya kara baci tayi Kokarin samun wata Dubara ammh Ashana taki kama Lagwanin Dole dai uwar naki Dakin ta koma tana Sunne kai yana Saka Takardun Cikin karamar bakar Jakarsa ta Briefcase ta Shigo yana ganinta ya Daga kai yana kallonta,Tunda yaga tana wani Sunne kai yasan akwai matsala Baki ya Tsuke yana kallonta yace"Da wani abu ne..?

Yafada kai tsaye Cikin Sanyinta tace"Eh...Eh...Dama da..."Dama mene in zaki yi mgana kiyi malama..! Ya katseta cikin Dauriya tace"Eh dama Kalanzir ne na duba naga babu wanda zan kunna Rishon dashi.."Tafada tana Sosa kanta Wani irin kallo ya sakarmata kafin kawai ya kada kai yana Fadin"Bazaki taba Chanzawa ba Hafsah narasa Wata iriyar macece ke..? Sau nawa zan gayamiki duk Abunda babu ki dinga Fadamin tun kofa da Nisa..? Yanzu ki duba agogo 7am  ake nema kuma kina sane da cewa 7:30am nake fita na Biya na kaisu Amira makaranta kana na wuce wajen aiki, baki ma sa mana Ruwan wanka ba ballatana akai ga Abun karyawa.."yafada cikin bayyana Takaichin dake cin Ransa.

Kasa tasakeyi da kai kafin tace"Kayi hakuri Wlh Allah bansan babu sai ya..."Wannan ya Rage naki ga Naira Dari ki Dauka ki Siya gawayi kiyi amfani dashi Domin yanzu babu inda zan samu kalanzir sai dai in na tashi Daga Office na Taho dashi.."yafada yana Jefamata Naira Darin daya Dauko Daga Cikin Walet dinsa bata tsaya wata mgana ba ta Duka ta Dauka ta Fita zuwa Falo karamin Dakin dake kallon nasu ta Shiga inda suke ijiye kayan abinci sai kuma wata karamar katifa Inda Amir da Amira ke kwana Mirmishi ta saki kafin ta karisa ta zauna gefen gadon tana Dukan Kafar Amira Lokaci daya tana Fadin"Amira...ke Amira Tashi maza.."

Ido Amira yar Shekara Shida ta Bude tana kallon mamanta Cikin Sauri ta mike tana Fadin"Mommy ."Mirmishi Hafsah ta sakarmata tana shafa kumatunta tace"Tashi kiyi sallah kiyi Sauri kizo ki shiga gidan Asiya ki Siyomin gawayi yau mun Tashi kalanzir din mu ya kare sai Abbanku yatashi aiki zai taho mana Dashi.."Amira bata koma ba Tatashi tana Fadin"Mommy ina Abba...? Hafsah tana kokarin Tada Amir tace"Yana daki kije ki gaisheshi Dagachan sai ki shiga bayi kiyi awala kiyi sallah kizo ki siyomin ina Jiranki kinji ko..? Dakai ta ansa mata kafin ta Ruga ta Fita da Gudu Amir ta Tada daga Barci waje ta Fita dashi ta sakashi Bisa Foo yayi Fitsari,kana ta wanke mai Fuska ta mai alwala ta turashi Daki tace yaje yayi sallah ya wuce yana Dan Gudunsa na yara wanda shima Ashekaru iyakarsa Shekara uku da wani abu.

Kichen din ta koma tana Tunanin me zata yi musu na karyawa Sharp sharp,ganin Lokaci ya tafi ya sa ta Fito da Murhun gawayin nata tsakar gida saboda yasha Iska Duk da Tsakar gidan bai da girma ammh kana gani zaka Fahimci komai na gidan Muhallin mace Daya ne,Buhun gawayinta ta Zazzage duk da ya kare ammh ta samu Kadan tayi Sauri zubashi Cikin Murhun gawayi ta kwafkwafi Sauran kalanzir din glan ta kunna wuta dayafara kamawa Da mafici ta tada gawayin da Sauri ta Dora yar madaidaiciyar Tukunyarta Ta cika da Ruwa,Dayake suna da Rijiya Tun Jiya almajiranta yunusa ya cikamata babban Robanta da Ruwa.

Kwai ta fasa,lokaci daya tana yanka Albasa ta gama kenan tana Jajjaga kayan miya da kayan kamshi Wanda zatayi amfani Dashi Wajen Soya kwai da Dahuwar indomie,Sai ga Amira ta Fito tana sanye da karamin Hijabi bayanta ta Rumgume tana Fadin"Gud mrning mommy.."Tana Dariya ta Dakata da Abunda takeyi tana Fadin"Ehe Amirata ta zama baturiya kin gaida Abbanku toh yaji kin iya Turanci..?

cikin Farinciki Amira ta gyada kai tana kallon Mahaifiyarta Kumatunta Hafsah ta ja tana fadin"Gud girl...Maza muje na Bude miki gida ki siyomin gawayin kafin wannan ya mutu.."Tafada tana mikewa Daga kan kujeran Tsugunee,Taja Hannun Amira suka nufi hanyar waje ita ta cire sakatar kofar gidan kana ta Damkama Amira Naira Darin,Fita tayi da gudu itama kuma Hafsah ta tsaya nan tana Lekenta dayake gidan yana kallon Gidansu ne,ko minti goma Amira batayi ba sai gata ta Fito Dauke da kullin bakaken leda Guda Biyu masu Dauke da gawayi Da Sauri Hafsah ta tarbeta suka Dawo cikin Gida,cikin Sauri ta Dauki Wata Karamar Roba acikin kichen dinta ta Juye Ruwan zafi har ya fara Tafasa,ta shiga daki dashi Cikin Bedroom dinsu ta shiga inda Ta Iske Abdullahi na wasa da Amir cikin bayin takai Ruwan ta zubamai Rabi Cikin Botikin karfen dake bayi wanda yafi kama dana gargaji ko Tiolet dinsu na Tsuggune ne ammh mai Floshing din nan,ammh kuma bayin Shinfide da Siminti sai Tashin kamshin Detol yake yi Domin Hafsah akwai Tsafta kwata kwata bata da Kazanta.

Akwai Wata katuwar Bombi mai Cike da Ruwa,cikinta ta Debi Ruwa ta surkamai Ruwan wankan Daidai Misalin sanin Komai tama Abdallah bata iyamai,Sauran ruwan kuma ta kauda dashi gefe Ta Fito tana yarfa Hannunta Lokaci Daya take fadin"Abban Amira ga ruwan wankan chan.."Bai amsa mata ba ita kuma bata damu ba ta Fice sanin yajita Sarai,koda ta Fito Tsakar gidan Amira ta karisa jajjaga mata kayan kamshi da Hanzari ta Bude Ledan gawayin ta kara Ta Fifita yatashi taDauko wata karama Cikin Tukwananta ta Dora ta zuba Ruwa Daidai,Daki takoma ta Dauko Indomei guda Biyar wanda zasu ci da kuma wanda su Amira zasu tafi Dashi Makaranta.

Agurguje take komai sai da ta Zuba Indomie ta tura Amira ta Dubo mata ko Abbansu ya Fito Daga wanka ta Dawo tace bai Fito ba, bata damu ba ta cigaba da aikin gabanta Cikin Sauri ta Sauke Indomie ta Dahu ta maida kaskon Ta Zubo mangyada Cikin wata karamar Roba da Cokali ta fara So kwan sai da Tagama tas kana tatashi ta Shiga Kichen ta dauki basket din su Amira ta zuba musu harda kwan,ta mikama Amira ta kai Daki Sauran kuma ta Zuba cikin kula,Ruwan zafi ta maida Saboda Sauri bata saka Cittan da ta saba Dafawa dashi ba Sauri take ta kamallah komai kafin ta Shiga Daki,kawai suma su Amira wanka ya Rage Ruwan yana zafi ta Juye cikin Flaks kana ta maida Wani Ruwan wanka.

Tattarra komai tayi zuwa Cikin Daki saman capet din dake Tsakar dakin ta Jera komai Ta Zura da Gudu ta Dauko Pure water guda biyu ta fasa ta Durama su Amira cikin goransu na Cikin basket dinsu,ta koma kichen ta kwaso kanann kofuna ta Dawo daki ta jera kusa da Falks din Ruwan zafi Dayan dakin ta koma ta kwaso kayan tea dinsu tazo ta jera duka cikin Sauri kafin ta Nufi Cikin dakinsu nan ta Iske Abdullahi ya Fito wanka yar yayi ma Amir wanka ma,Da Hanzari tatura Amira cikin bayi ta Tubeta ta mata wanka ta Fito Amir ta fara Shafa ma mai Abdullahi kuma yana tsaye yana saka maballin Rigarsa,Amira ita ta shafama kanta mai Hafsah ta Fito musu da Uniform,Amira ta saka ma kanta ita kuma ta sakama Amir harda safa da Takalmi ta Dauko musu Jakunkunansu ta jasu zuwa Falo ta zaunar dasu ta hada musu Tea ta zuba musu Indomie da kwan ta Turama kowanne gabansa tana Fadin"Oya kowa yayi Bismillah kuma kuyi Sauri in ba Haka ba Abbanku yatafi ya barku.."Jin haka yasa suka Fara cin Abinci bayan sunyi Bismillah.

Tea din Amir ta Dauka tana Fifitamai sanin baya iya shan Abu da Zafi sai ga Abdullahi ya Fito Cikin Shigar Riga da wando kalan Navy blue,sunyi matukar mai kyau Ta kallesa tana Mirmishi ammh shi ko kusa Fuskarsa ba Walwala kusa da Amira ya zauna Jikinta na Rawa ta Shiga Kiciniyar Zubamai Indomie din Hannu ya Dagamata yana Fadin'Barshi..Bani Tea din kawai.."Jikinta a sanyaye ta Tsiyayamai Ruwan Tea din ta Tura gabanshi da wata Harara ya Rakata kafin yace",Oh ni kike so na hada Tea din kenan yau..?

Da sauri Hafsah tace""A"a ba nufina ba kenan naso ka Hada da kanka ne kada kace ina cika maka Siga.."Hararanta yakarayi kafin yace"Toh bazan hada ba..Kuma ki cika sigan ki gani.."Numfashi ta sauke kafin taja Kofin gabanta Madara ta farama Zubamai Cokali Biyu Zata Rufe kenan yace mata,"Kina Nufin Iya madarar da zansha kenan..? Wai ni Hafsah ke ki ke siyan kayan Shayin ne da kike min Ididdiga..?

Saurin Taran Numfashinsa,tayi da cewa'Bafa haka bane..Gudun nayi na Saka maka da yawa kace na Cika maka madara.."Wani kallon kasa kasa yayi mata kafin yace"Commom malama Karamin madara kina batamin Lokaci.."Numfashi ta Sauke Aranta tana fadin komai akayi maka koda na Gudun karkayi mgana ne sai ka Tanka,Madara da Bonviter din da yawa ta Zubamai Siga kuma ta sakamai kadan ammh duk da haka sai da yayi korafin ta bashi Tea ba siga Kai ta dafe kawai tana kallonsa Sigan ta Turamai gabansa Lokaci daya tana mikewa kallonta yayi yana Fadin"Ina zaki..? Ke bazaki karya bane..? Tana kokarin Shiga Uwar dakin tace"sai anjuma."Baki ya tabe kafin yace"Kanki.."yafada yana Zakuda kafada irin ko ajikinsa dinan.

Takwas daidai suka gama karyawa Shi ya fara mikewa yana kwalama Hafsah kira sanin Kiran yasa ta Fito da Sauri Lokaci daya tana Dauke da...


Read / Download MASIFAFFAN NAMIJI

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album