Join Our WhatsApp Group

UMMIE Complete Hausa Novel Document by UMMIE


UMMIE

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 102871



UMMIE

Reading Time: 8 Hours

Added On: 02, Sep 2023

Author: Autar Mama ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : *EXQUISITE WRITER'S FORUM*

Author Phone : 08142904255

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 583.51 kb

File Type: txt

Views: 546+

Download: 642+

Last download: 6 hours ago

Description/Story: An dauko wannan littafi daga shafin www.dlhausanovels.com.ng ku ziyarci shafin na www.dlhausanovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya

Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,

Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490

A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,

Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu

Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC

Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from www.dlhausanovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services

Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us

Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it

Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT✨✨ *UMMIE* ✨✨

_Labari daya danganci soyayya da kuma ƙalubalan rayuwa_

*FREE BOOK*

*MALLAKAR*
*Autar Mama*

*EXQUISITE WRITER'S FORUM*
(E.W.F)

*Follow me on Wattpad @Autarmama56*

*Comment da voting shi zai sa a dinga samun update da wuri*

I just published "Chapter 1" of my story "UMMIE". https://www.wattpad.com/1168359507?utm_source=android&utm_medium=com.gbwhatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=AutarMama56&wp_originator=ZbVY0Hth4KHji9qv%2FBvA2vMptu3DyOH4d4aL08P69EeYz0GH7DNo7UlicEiFv12F1Xyw3%2Fz32gI3NZ%2B9pj851f0McDdsKOMsH0APbdmHFHGd5EW65lmVTvxuB3tRqT0d

*Whatsapp group pls banda maza*

https://chat.whatsapp.com/CWWKwL2Fbuf2OXISNrUtNH

*Shafi na ɗaya*

*NIGERIA*
*KANO STATE*

*YEARS AGO*

Cup din tea dake bakinta ta sauke tana kallon Umma dake shafa butter a jikin bread ta ce " Zan tai dan akwai wasu client ɗin *_YUSUF_* da zasu zo by 9am, ɗakin taron ba'a gyara yake ba ya kamata inje office kafin 8"

Bata jira cewar Umma ba ta dauki hand bag dinta ta rayata tana gyara mayafin abayar dake jikinta.

"Toh Allah ya kiyaye, ki kula kinji?

Murmushi Budurwar tayi wanda ya bayyanar da dimple dinta me matukar kyau. Gyara zaman gilashin dake fuskarta tayi tana faɗin " Amin Ummana"

Daga haka ta fice daga gidan. Murmushi Umma tayi a fili ta ce " Allah yayi miki albarka *_ZARAH_* Allah ya tsare miki mutuncinki a duk inda kike"

Tana fita ta samu napep kasancewar kusa da titi gidansu yake.

Tafiya ce me dan tsayi kafin ta iso wani gini me dan karan kyau da kuma tsayi dan ya kai hawa 5, a saman ginin an rubuta *TWO BROTHER'S*

Sallamar me napep din tayi tana shiga ginin ta ƴar ƙaramar ƙofar da aka tanada saboda shiga.

Sai da akayi checking ɗinta saboda tsaro sannan ta wuce tana sauri tana gaisa kuma da mutanen da ke daga ma ta hannu.

Lifter ta nufa dan bazata iya bin stairs ba saboda zai ci ma ta lokaci. Tana isa office ɗinta ta ajiye jakarta ta fito. Wani office din ta shiga wanda ke ɗan nesa da nata bakinta dauke da sallama.

Matashi ne zaune yana amfani da na'ura me ƙwaƙwalwa. Ɗagowa yayi yana kallonta fuskarsa a sake ya amsa ma ta sallamar yana ɗorawa da cewa " Yanzu nake ƙoƙarin kiranki ai"

Zama tayi a kujera tana fadin " Lafiya dai?

"Eh, ya shirye shiryen biki?
Ya faɗa yana mata murmushi.
"Komai normal fa, so nake ka kira Kabiru saboda inaso a gyara dakin taro sannan ayi ordering abinci sai a kawo ruwa lemo by 9am wasu client da za muyi wani project tare zasu zo"

"Uhm, Zarah sarkin aiki! Kiran da zan miki ai a kan wannan taron ne, Me gida ya ce in sanar da ke ya baki hutu sai bayan bikinki"

"Seriously?! Ta fada tana zara idonu cike da mamaki.

Dariya yayi yana faɗin "Nima nayi mamaki ai kinsanshi baya son wasa a aiki, maganar taro kuma nasan maybe ya soke dan yace in sanar dake ma karkizo aiki"

Relaxing tayi a kujerar tana Murmushi tayi " Gaskiya naji dad'i wallahi"

"Ok naji karki cikani da surutu ki tashi ki tafi gida, anjima Zainab zata zo maybe tayi deciding abubuwan da zakuyi a bikin"

Tashi tsaye Zarah tayi tana gyara glashin dake fuskarta ta ce " Ai Umma tayi fushi da kai _*ZAYD*_ ko Allah ya sanya alkhairy baka zo kayi ma ta ba ko?

Tsayawa yayi da abinda yake kafin ya kalli Zarah ya ce " Zanzo insha Allah ki bata hakuri"

Taɓa baki tayi tana ficewa daga office ɗin.

Zarah bata tafi gida ba, office ta nufa ta fara rage wasu ayyukan ta har kusan 10am.

Ganin ko ina yayi tsit yasa ta game Yusuf yazo dan baya son hayaniya kowa yasan da hakan. Zaro ido tayi waje tana kalle² ko zata samu wajen ɓuya tasan by now Zayd ya sanar masa da cewa ya faɗa ma ta sakonsa amma kuma ta zauna a office har yanzu tsaf zai iya cewa ya soke hutun daya bata.

A gaban cabin dinta ya tsaya dan yaji motsi. Matashi ne ɗan gaye me ji da kanshi yasha Desmond merrion supreme suit me dan karan kyau da tsada, ƙafarsa sanye da Crockett shoe, hannunsa sanye da smart watch, bashi da suma haka zalika bashi da saje amma fa akwai kyau, ba fari bane yana da duhu.

A hankali ya ƙarasa bakin cabin dinta yana ɗan kalle² kafin ya ce " Zarah! Cikin muryarsa me amo.

"Na'am" Ta masa batare da ta sani ba. Riƙe bakinta tayi cike da takaici kafin ta fito a hankali cikin sanɗa. Kallon sama da ƙasa yayi mata kafin ya ce " Zayd be sanar dake saƙona ba?

"Eh" Ta fada a takaice.
"A'aaaaa... Uammm.. I..ina nufin ya sanar dani yanzu nake shirin tafiya"

Daga haka ta koma cikin cabin ɗin ta da sauri har ta fito yana tsaye a inda ta barshi.

"Nagode" Ta fada tana ƙoƙarin wucewasa. "Tsaya" Ya faɗa yana juyowa. Itama juyowa tayi tana murmushin dole.

Envelope ya ciro a aljihunsa na cikin suit din ya miƙa mata yana faɗin " Inji *_FAROOQ_* yana miki fatan alkhairy.

Girgiza kai tayi da sauri tana faɗin "Ka ce masa Nagode"

Ajiye wayi a kanta yana fadin " Allah ya baku zaman lafiya"

Daga haka ya barta a wajen. Hannu ta saka ta ciro envelope ɗin tana murmushi.

*****

"Zarah! Zarah! Yadda yake kiran sunanta shi ya dawo da ita daga duniyar tunanin da ta tafi na rayuwarta na baya kafin ta auri wannan azzalumin mutumin......

*Comment da voting nake buƙata! Idan babu zan mai dashi na kuɗi*

Autar mama ce.
✨✨ *UMMIE* ✨✨

_Labari daya danganci soyayya da kuma ƙalubalan rayuwa_

*FREE BOOK*

*MALLAKAR*
*Autar Mama*

*EXQUISITE WRITER'S FORUM*
(E.W.F)

*Follow me on Wattpad @Autarmama56*

I just published "Chapter 2" of my story "UMMIE". https://www.wattpad.com/1168718784?utm_source=android&utm_medium=com.gbwhatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=AutarMama56&wp_originator=g1o05WXd5%2BE9QwoBVAL%2Bho6KW8po2enK%2Bd4M7ism3i%2BY%2BZDM1Ol2SbVQkkxMzN3xvkF06pxaQzEBH%2FK8P3%2FrpJhb942UPTWPB%2FKznl9DR8c2tJRN77uTCFrHFYo4Pxiy

*Comment da voting shi zai sa a dinga samun update da wuri*

*Whatsapp group pls banda maza*

https://chat.whatsapp.com/CWWKwL2Fbuf2OXISNrUtNH

*Shafi na biyu*

Idanunta na zubar da ƙwalla ta kalleshi ta ce " Na'am baban _*UMMIE*_

"Idan kika ƙara dangantani da wannan baƙar yarinyar sai na ci..... Ƴar akuya kawai, bansan dalilin daya sa na aureki na wallahi! Kaf matan duniyan nan na rasa wadda zan aura sai ke! Nasan ba haka kuka barni ba ke da mayyar uwarki kunga me kudi! Yan matsiyata kawai"

Sosai taji zafin kalmansa, taso tanka masa amma kalaman mahaifiyarta na karshe suka dawo ma ta.

*'Zarah shi gidan aure wahalar sa tafi dadinsa yawa, kuma hakuri akeyi! Duk macen da zaki gani zaune a gidan mijinta to ki tambayeta sirrin, zata ce miki haƙuri ne! Toh kema inaso kiyi wannan haƙurin, duk abinda *_SHEHU_* *zai miki kiyi hakuri karki bar aurenki ko dan Ummi saboda idan kika bar gidan aurenki ƴarki itace a wahala kuma baki san hannun wanda zaki faɗa ba gwanda kiyi zamanki a gidanku kiyi ta haƙuri, watarana sai labari'*

"Ka...ka .kayi haƙuri" Ta faɗa tana jin wani ɗaci a zuciyarta.

"Ai kullum cikin haƙuri nake dake! Tashi ki bani abinci sakarya kawai"

Yana gama fada ya nemi waje ya zauna a cikin ɗaya daga cikin royal chairs ɗin dake tafkeken falon.

Jikinta ba kwari ta nufi dining area ta jero masa abincinsa a babban tray, a gabansa ta ajiye tana faɗin " Me zaka fara ci?

Ba tare da ya kalleta ba ya ce "Har kala nawa kika dafa abincin?

A ɗan tsorace ta ce " Biyu"
Kafin yayi wata² ya dauke ta da mari, yana shirin ƙarawa yaji an riƙe masa rigarsa ta baya.

Waya yarinya ce wadda bazata wuce 7-8yrs ba, Black beauty me tsananin kyau kamar ita tayi kanta, cikin Muryar yarinyata ce " Abba dan Allah ka daina dukan Ummana tana jin zafi"

Cikin ko in kula yasa hannu ya ture yarinyar tana faduwa a ƙasa tare da buga kanta a tiles, aikuwa ta tsandara ihu. Da sauri Zarah ta nufi inda take tana daukar ta hawaye masu zafi na zuba daga idanunta.

"Ummi! Ummi! Ta fada da karfi tana jijjiga yarinyar. Cikin bacin rai ta kalli Shehu ta ce " Wai baka da imani ne? Kai wani irin azzalumi ne?

Ƙarasowa yayi inda suke yasa hannu ya riƙo habarta cike da mugunta ya matse sosai yadda zata ji zafi.

"Uban waye azzalumi Zarah? Ya faɗa yana kara matse ma ta haɓarta.

Kasa magana tayi dan zafin da take ji ya wuce misali.

Dan kanshi ya sakar ma ta bakinta yana huci ya wuce ya barsu a wajen.

Hawayen idanuwanta kasa daina zuba sukayi, daukar ƴarta tayi ta nufi daki da sauri, a kan gado ta kwantar da ita tana shiga banɗaki da sauri ta ɗauko jikaƙakken towel ta ɗorawa shi a kan UMMIE tana faɗin "Allah zai saka miki"

A hankali Ummi ta fara buɗe kyawawan idanunta tana kallon Mahaifiyarta ta ce " Ummana kaina ciwo yake"

Da sauri ta goge hawayenta tana shafa kan Ummi ta ce " Sannu, bari na baki paracetamol kisha"

"Ummana ni dai bana son shan magani" Ummi ta faɗa tana son tashi zaune.

"Kwanta Mamana karki tashi kinji? Haƙuri zakiyi kisha magani"

"Toh Ummana" UMMIE ta faɗa hawaye na zuba a idanuwanta.

*********

"Ina cikin farin ciki Sa'adah ina cikin tsananin farinciki yau zan auri wanda zuciyata take muradi! Inason Shehu sosai Allah na gode maka da zaka mallaka min wannan bawa naka a matsayin mijina"

Wadda ta kira da Sa'adah ce tayi wani Murmushi tana dan taɓa baki ta ce " Kedai shaukin ya isa haka ki tashi ki shiga wanka kafin yamma tayi kinsan yace da wuri zai aiko motoci"

Tana murmushi ta tashi ta fito daga ɗakin.

Wata budurwace me kyau wadda zasuyi sa'anni ɗaya da Zarah ba ta zo inda take tana faɗin " Amarya! Tun dazu yah Farooq da Yah Yusuf suke jiranki a soro zakuyi magana, na dauka ma bacci kike kwanta"

Kai Zarah ta girgiza tana Murmushi ta ce " Bari naje"

Mayafin dake jikin Budurwar ta karba ta kutsa cikin mutane ta nufi soron gidan.

A zaune ta gansu a kan sallaya su uku har da ɗan me gidanta Yusuf yaron bazai wuce 6yrs ba.

Bakinta ɗauke da sallama ta karaso kanta a ƙasa. Amsawa sukayi suna murmushi. A ɗan gefen sallayar ta zauna tana gaidasu.

Amsawa sukayi kafin Yaron y gaisheta itama ta amsa tana kalllonsa.

"Zarah ga wannan ba yawa zamu wuce Allah ya baku zaman lafiya"

Kallon bandir din kudin tayi daga dan ƙasan idanunta kafin ta girgiza kai ta ce " Nagode Sir amma bazan iya karba ba"

Tashi sukayi Yusuf ya kalleta ya ce " Idan ba rainawa kikayi ba ki dauka, ki gaida Umma Allah ya albarkaci aurenku"

Da Amin ta amsa tana yin murmushi tare da furta kalmar Nagode.

Fita sukayi daga gidan, Yusuf yana ta shafa bayan Farooq a hankali.

A hankali ta tashi ta ɗauki kudin ta koma cikin gida.

*****

"Ke wai tunanin ubanme kike yi? Taji Muryar Shehu ya faɗa daga bayanta.

Da sauri ta tashi tana juyowa ta kalleshi tana goge hawayen idanunta.

Matsowa yayi kusa da ita yana gyara hannun armless din dake jikinsa fuskarsa a ɗan sake.

Juyowa tayi taga Ummi na kallonta.

Matsawa bayi tayi tana kallonsa ta ce " Menene?

"Meyasa kike gudu? Ni ba mijinki bane?

Tun da taji yana magana a hankali tasan bukatarsa ce ta kawosa. Haɗe rai tayi kaɗan ta ce " Zan biyo ka daki Ummi na nan"

Riƙo hannunta yayi da ƙarfi yana fadin " Ban damu da ita ba idan ma zata nade komai a kwanyarta ne ban damu ba! Zara ina zaune dake ne kawai saboda ban samu macen aure ba amma bazan iya cigaba da zama da fasiqa ba!

"Fasiqa?! Zara ta faɗa hawaye na kwaranyo wa a idanunta. "Karya nayi? Uban waye uban yarinyar nan idan ba wannan me gidan naki ba nawajen aikinki?

Tureshi taso yi dan ta gaji da maganganun da yake faɗa ma ta, amma ko motsi beyi ba dan ba rikon wasa yayi ma ta ba. Murmushi yayi yana saka hannunsa bisa ƙugunta yana matso da ita jikinsa.

Da sauri ta kalli Ummi, itama kallonsu take.
"Me haka Ummi fa tana gani" Zarah ta faɗa tana ƙoƙarin sake tureshi gabanta na faduwa, wannan bashi ne karo na farko da Shehu yake ma ta haka ba a gaban Ummi, tana tsoran tarbiyyar ƴarta ya lalace dan shi bai damu ba......

*Comments da voting kawai nake bukata idan ba haka ba zan mai dashi na kuɗi😝*

*Naji dadin yadda ku ka karbi littafin nan*

Autar mama ce
✨✨ *UMMIE* ✨✨

_Labari daya danganci soyayya da kuma ƙalubalan rayuwa_

*FREE BOOK*

*MALLAKAR*
*Autar Mama*

*EXQUISITE WRITER'S FORUM*
(E.W.F)

*Follow me on Wattpad @Autarmama56*

I...


Read / Download UMMIE

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album