Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

SAI NA AURI MARUBUCI Complete Hausa Novel Document by SAI NA AURI MARUBUCI


SAI NA AURI MARUBUCI

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 30263



SAI NA AURI MARUBUCI

Reading Time: 2 Hours

Added On: 23, Jun 2024

Author: Aisha Mohammad Sani (Xayyishatul Humaira) ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : 08103080717

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 173.27 kb

File Type: txt

Views: 719+

Download: 428+

Last download: 3 hours ago

Description/Story: _*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_
_(Nafseen)_




_GAJERAN LABARI📝_

NAH

AISHA MOHAMMAD SANI
(Xayyeesherthul-humaerath)


_*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_


_FREE NOVEL NE AMMAN RASHIN SHARHI ZAI IYA SAWA YA DAWO NA KUDI, YANAYIN YADDA KUKA DAUKA NIMA HAKAN ZAN DAUKA✌️JUST FOR MY FANS,LOVE YOU LODI,LODI🥰❤️💃_

MARUBUCIYAR👇
KUCHAKAR KISHIYA
BABU RUWAN SO
AZZAWAJUL-MUKADDAR
WASA DA SO
KWADAYI 2020
MATAR POLICE 200
JAMEEL 200

NA YANZU: SAI NA AURI MARUBUCI


PAGE 1/2

BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM.


_*FEJIN FARKO SADAUKARWANE GAREKU FAUZIYYA TARE DA JANNAT YAR BABA KUJI DADINKU🥰🥰🥰*_

........Wata Yar matashiyar yarinya na hango da bazata huce shekara goma sha bakwai ba aduniya, kwance take tana barci cikin nishadi da walwala domin da zaran an kalli yadda yanayin murmushi ke bayyana afuskarta wannan ka dai ya isa laburta cewa tana cikin yanayi na farinciki,ta kankame littafin Hausa akirji tamkar tana gundu a kwace mata, mafarkine Wanda ta sabayi kamar kullum Amman ko wanne da salonsa ko na yau din ya yake? Bara mu lekye cikin mafarkin Nafeesa.


"Nafeesa kin San cewa ba jin cewa akwai Wata 'ya Mace da zan so kamarki? Kina jin cewa zan iya furta Kalmar so ga Wata 'ya Mace bayan ke?, Hmm babu tantama cewa ke ce zabina sannan kuma kece burina,ina miki so fiye da yadda majnun ke son laila,ina kaunarki fiye da yadda kifi ke bukatar ruwa domin rayuwa." Cewar Nafseen da ke zaune gaban Nafeesa.




Gyara zama tai tare da kara kura mai kallo tai murmushi kan ta fara da, "Da ace ana Iya kidaye adadin soyayya a sikeli na tabbata cewa wadda nake yi maka bazata taba kidayuwa ba,kamar yadda Dan Adam ba zai Iya rayuwa batare da ruwa haka Nima nake jin cewa ba zan iya rayuwa batare da kai ba, ka zamemin jinin jikina,numfashina da walwalata, ada nakan ji cewa ka fi karfina ba zan taba samunka arayuwata Amman wai yau nice tare da kai har kake furtamin Kalmar so? Dan Allah Nafseen ka rayu da ni karka barni karkacemin wannan mafarkine nake yi."


Rik'o hannunta ya yi,yana kokarin yin magana.

Karaf Mama ta shigo tare da bugawa Nafeesa dundu abaya.

Sambatu take,"Ka kara cewa kana so na ko da sau dayane Dan Allah kar ka tafi."


Dukan da Mama ta kara kai mata ne ya sa ta saurin razana tare da dawowa hayyacinta, "Mama kin kuran min shi, Mama kice ya dawo yau ya fadamin cewa yana sona mama Dan Allah kice ya dawo."


Tsaki Mama tayi, "Ki bar min wannan shirmen tun kan na kai miki mari maza tashi kije kiyi sallah wawiya kawai."


Kara kallon dakin tai da kyau ta ga da alamar gaske dai daga itane sai Mama, kuka kawai ta fara tana, "Mama wallahi in ban gan shi na aure shi ba mutuwa zan yi, ni kan sai na AURI MARUBUCI." ta kara fashewa da kuka.


Wani irin bakin cikine ya kara tirnik'e mahaifiyarta ta, ta fice batare da tace komai ba illa azuciyarta da take fadin, "Ban San wannan wani irin bala'in so bane ga mutumin ba ba a taba gani ba, daga karatun littafi kawai, anya kuwa ba aljanune suka shiga jikin Nafeesa ba kuwa? Ya Zama dole in sanar da Abhee abin da ke faruwa adaren yau."

Ta shige daki.


Ita kuwa Nafeesa kara kyankyame littafin tai tana kuka sai da tai mai isanta kan ta dauro alwala tai sallah, tana idarwa ba abun da ta fara rok'a illa Allah ya nuna mata marubucinta Nafseen Sanan kuma Allah ya bata ikon auransa.

Bayan ta kammala addu'ar tashi tai ta fita waje da littafinta ahannu, zama tai afilin tsakar gidan na su tare da chok a hannunta Zane ta farayi tana waka Wanda da farkon zanen duk Wanda ya kalla zai dauka cewa shirme take zanawa,Amman ahankali kyahun zanen na fitowa,da mamaki duk da kasancewar Nafeesa ba ta San Nafseen ba Amman tsaf yanayinsa da kamaninsa take zanawa,ba musu duk Wanda ya San Nafseen kuma ya ga zanen Nafeesa zai dauka cewa ta San shi kuma kyakkyawan sani ma, azahirin gaskiya ko bata taba ganinsa ba bin abun da zuciyarta ke rada mata kawai take ya yin zanen tundaga farko har karshe.


Kallonsa ta tsayayi tana mai farinciki ji take tamkar na gasken ne agabanta, cikin littafan da ta fito da su ta dau daya mai suna YAR AUTA NA JAMEEL NAFSEEN, Karatu ta fara cikin nutsuwa da zakuwa akowanni feji ganin ta riski gaba, labari Indai na shi ne ko wani irin salo na tafiya da zuciyar Nafeesa.

Gabadaya hankalinta ya tafi ga karatun kaninta da ba zai huce shekara Takwas bane ya fito yana buga boll ta gabanta ya huce ba tare da sanin Sa ba har ya goge mata zanen Nafseen.


Ji tayi ajikinta hakan ya Sa ta saurin kallon kasanta gani tai tamkar na gasken ne ya yi hatsari hakan ya sa ta Jan dogon numfashi tare da suma awajen nan take.

✌️YAWAN SHARHI YAWAN TYPING

Urs Xayyeesherth
_*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_
_(Nafseen)_
12/1/2021



_GAJERAN LABARI📝_

NAH

AISHA MOHAMMAD SANI
(Xayyeesherthul-humaerath)


_*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_





PAGE 3/4

BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM


*🥰🥰 WANNAN FEJIN SADAUKARWANE GAREKA YAYANA,ABUN ALFAHARINA,YAYA MUSADDAM😘YAYANAH YA FI NA KOWA💃ANGON MAI AWARA SON SO FISABILILLAH*


MY GROUP XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH FANS GROUP INA KAUNARKU HAR CIKIN RAINA MASOYAN ASALI😘😘


Sabeer bai San lokacin da kurma uban ihu ba, "Mammah kizo Anti Nafeesa ta mutu,Mammah."


A rikice Mammah ta fito tana, "Sabeer wai meyafaru ne ba yanzu ta fito karatu kalau ba?"


Sabeer na kuka ya ce, "Ban San tayi zane bane na goge mata tana kallo shine ta fadi."


Dafa kai Mammah tai tare da fadin, "Yah Allah!

Kokarin daga Nafeesa daga wajen tai domin maidata cikin gida, da yake Mammah malamar asibitice kokari tai domin dawo 'Yartata cikin haiyacinta a Dan kankanin lokaci.


Bude Idon da Nafeesa za tayi ta fara, " Mammah Nafseen dina Sabeer ya gogemin, sai ta kara fashewa da kuka."

Mammah bata da zabin da ya wuce ta rarrashi 'Yartata awannan lokacin hakan ya sa ta Jan Nafeesa jiki tana shafa mata baya, "Ki yi hakuri kinji Nafeesa bai sani bane, kuma ai zanene na San zaki Iya zana Wanda ya fi wannan kyau ko?"


Wani Dadi Nafeesa taji aranta nan take ta mik'e "Sabeer Bani Littafina zan tafi madarasa."


Mammah ta ce, "Madarasa da littafin Hausa? Haba Maman Abhi kibari in kika dawo kyayi karatun."


Nafeesa ta fara buga kafa, "Ni dai da abuna zan tafi wallahi."


Tashi Mammah tai kawai tana fadin, "Allah ya kyauta."

Nafeesa kuwa Hijabinta ta Sa har kasa tare da nikabinta ta yafa jakar makarantarta agefenta na hagu sannan littafin hausanta na marubucinta NAFSEEN a hannun dama wato Yar Auta.


Ko da ta isa makaranta anfara karatu Neman waje kawai tai ta zauna tare da bude littafinta domin cigaba da karatu.

Karatu ake yi masu Amman gabadaya hankalinta na kan littafin da take karanta, murmushi ne kawai ke bayyana afuskarta, kara gyara zama tai tare da Jan dogon numfashi ta cigaba da karatun, Malamin ne ya lura da yanayinta ganin cewa hankalinta baya tattare da shi duk da kasancewar bai hango me take kallo ba.

"Ke Nafeesa, ta shi ki karantomin hadisin farkon nan da na kawo."


Cikin Sauri ta ta shi arikice take maganar, "Mallam, ai Nafseen bai fadamin ba aciki."


Sake baki ya yi yana kallonta kawai cen ya daka mata tsawa, "Waye Nafseen? Karatu muke ko maganar wani anan, Iye ba tambayarki na ke ba?"


Sunkuyar da kai Nafeesa tai batare da ta kara kallon malamin ba.


Cikin tsawa ya kara fadin, "Nace waye Nafseen?"


Karaf wata yarinya ta ce, "Malam wani marubucin littafan hausane."


Kara fusata malamin ya yi, "Ah ya yi kyau aiko yau zakiga Nafseen a makarantar nan ganin idonki bani littafin."


Jiki asanyaye Nafeesa ta mik'a masa littafin .


Yana karba ya karema littafin kallo kamar yadda aka Fada sunan marubucin Nafseen,tsaki ya yi Sannan ya fara fata-fata da littafin yana yankawa.



Kuka Nafeesa ta fara yi bilhakki da gaskiya,tun tanayi ahankali har ta fara shidewa daga karshe ma ta k'ame awajen nan take.


Ganin yadda tai, abun ya matukar ba malam mamaki daga yaga littafi, tsaki ya yi yana fadin, "kar in ga kowa ya fita kuzo mu cigaba da karatun mu in iskancine nawa yafi nata.


Kwance take awajen cen kuma ta mik'e tare da wani irin gawartaccen kara,Malam ta nufa kawai tare da damkosa tana wani irin numfashi.


Ihu ya fara yana, " Dan Allah Ku kwaceni Nafeesa za ta kasheni,wayyo Allah na."


Dalibai kuwa sai dariya.


Nafeesa kuwa bata fasa jibgar malam ba.

Dalibanne suka kira sauran malaman dakyar aka karba Malam a hannun Nafeesa sai numfarfashi take tana kara kokarin cacumosa.

Malam na samun hanya ya fice adari yana, "Wallahi Yarinyarnan ba mutum bace Ku bincika." maganar yake cikin Sauri da hakki domin ji yake tamkar zata kara damkar shi.


Suko dalibai ba abin da suke ban
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download SAI NA AURI MARUBUCI

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album