Join Our WhatsApp Group

THE GOVERNOR'S WIFE Complete Hausa Novel Document by THE GOVERNOR'S WIFE


THE GOVERNOR'S WIFE

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 81930



THE GOVERNOR'S WIFE

Reading Time: 6 Hours

Added On: 07, Oct 2023

Author: Azizat Hamza ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 428.75 kb

File Type: txt

Views: 1948+

Download: 1812+

Last download: 18 hours ago

Description/Story: 01



***



"Nana ki fito mu yi breakfast da Daddy" muryan Mahirah ya doki kunnen Nana da ke zaune chan ƙuryan gado tana maƙyarƙyata. Minti biyar da suka wuce ta fito zata je dinning ta yi kiciɓis da macijin mommynsu ta koma ɗaki a guje jikinta na maƙyarƙyata. Ba yau ne hakan ya fara faruwa ba, ranan da ta fara ganin macijin a nannaɗe a hannun mommynsu sai da ta kusa shiɗewa saboda tsoro, a hakan sai Mommyn na su ta shiga yi mata faɗa wai babu abinda macijin zai mata it's just a pet snake. Pet snake kamar wanda suke zaune a daji. Tunda suka zo gidan ko kyanwa babu balle kare amma a rasa pet ɗin da za a kawo gida sai maciji.

Su uku ne zaune a wajen dinning ɗin, yau ne ɗaya daga cikin ranaku biyu da Gwamna ya tilastawa kansa zama yai breakfast da 'ya'yansa. A yanzu kam zama da 'ya'yansa shine kaɗai ke saka masa nitsuwa.

Mahirah ta miƙe ganin har yanzu Nana ta ƙi fitowa, bayan tafiyar Mahirah Gwamna ya zubawa Junior idanu yana kallon yadda yaron ke wasa da abincin da ke gabansa, gani yai yaron ya rame masa kuma babu walwala a tattare da shi kamar da.

"Babana" Gwamna ya kira shi a hankali, amma maimakon da idan ya kirashi da hakan yake cewa shi ba Babansa bane, yau kam ko ɗaga idanunsa bai yi ba balle ya tanka masa.

Gwamna ya riƙo hannun yaron yana faɗin "Sa'ad junior"
Ai kafin ya ƙarisa maganar Junior ya challah ƙara yana faɗin "Mommy no snake, please no snake"

Gwamna ya taso ya rungume Junior tsam a jikinsa yana bubbuga masa baya. Shi kansa wannan maciji da Bilkisu ta kawo gidan ya tsaya masa a rai amma ya kasa yi mata magana a kai.


Mahirah ta fi minti biyu tana buga ƙofar ɗakin Nana kafin da ƙyar Nanan ta ja jiki ta zo ta buɗe mata.

"Miyasa kika kulle ƙofa?... Nana miya sameki?... kuka kika yi?"

Shiru babu amsa sai kuka da Nanan ta sake fashewa da shi.
"Nana minene please?" Mahirah ta faɗa itama kaman zata yi kuka.

"Mom...Mom... Mommy's snake" ta faɗa da ƙyar.

"A ina kika ganshi, Mommy ta fita da shi ɗazu"

Nana ta yi shiru ta kasa magana dan kanta ya ruɗe shin kafin Mommyn ta fita da shine ta ga macijin ko bayan an fita da shi?

"Kar ki damu babu abinda zai miki, ki zo muje mu karya Daddy na ƙasa kin san ba wai koyaushe muke ganinsa ba"

Da ƙyar Nana ta amince suka sauko ƙasa. A nan suka tarar Daddyn nasu na fama da lallashin Junior.

Mahirah tace "Daddy dan Allah ka ce Mommy ta dena yawo da macijin nan. Nima ba wai ina son shi bane, amma Nana da Junior always panic idan suka ganshi. Daddy dan Allah kayi wani abu akai"

"Ku kwantar da hankalinku, zan mata magana"

Safiyar ranan dai sun ci abincin ne a darare dan kowa ba wai ya ci da kwanciyar rai bane.

***

Nana da Mahirah suka shiga haɗa kayansu da sauri-sauri saboda basa so mahaifiyarsu ta dawo ta samesu a gidan. Kwana uku kenan da Daddy yai musu alƙawarin zai yiwa Mommy magana amma babu abinda ya chanja dan ko yau da safe da macijin Mommynsu ta fita. Jiya da yake Mommy ta wuni a gida Nana ko iya fitowa bata yi ba saboda tsoro dan idan Mommy na gida tana barin macijin yai ta shawagi tsakanin ɗakinta da kuma falon ƙasa.

Sai da suka gama haɗa komai sun sauko da akwatunan kawai suka ji ƙaran siren.

"Mommy" Nana ta faɗa a tsorace

"Inaga Daddy ne fa"

"Mommy ce Mahirah" Nana ta faɗa tana shirin kuka.

Mahirah tayi ƙarfin hali tace "koma Mommyn ce mu tsaya mu gaya mata matakin da muka ɗauka"

Suna tsaye riƙe da akwatuna Bilkisu Kachallah ta shigo biye da ita kuma wasu manya-manyan mata ne guda biyu da suke matsayin personal bodyguards ɗinta. Ko a ina ta samo su oho, dan kuwa basu yi kama da 'yan Nigeria ba. Sun fi kama da black Americans da suka ƙware a body building. Da za su cire rigan jikinsu babu tantama sai ka ga 6 abs kaman a jikin shaharraren ɗan damben nan The Rock. Suna sanye da baƙaƙen kaya riga da wando da kuma baƙin gilashi da suka toshe idanunsu da shi, fiskarsu a ɗaure babu alamun fara'a ko kaɗan.


"Ina zuwa?"

Nana ta ɗan matsa bayan Mahirah, duk da babu macijin a hannun Bilkisu amma a karan kanta Mommyn na su yanzu tsoro take bata.

Mahiran ma tsoron ne ya ɗarsu a zuciyarta lokacin da suka haɗa ido da Bilkisu Kachallah.

"Ehen, ina zaku je kuka tattaro kaya kaman masu shirin ƙaura?"

Mahirah ta haɗiye miyau tana karanto addu'a a ranta *Allahumma lah sahla illa ma ja'altahu sahla...*

"Khadijah, Mahirah, baku da baki ne?"

"Mommy.... Kachallah house zamu je. Ba zamu iya zama a nan ba, idan kina so mu zauna ki zaɓi ko mu ko macijin ki"

Bilkisu ta yi mamakin ƙarfin halin Mahirah. Yarinyar da ada bata iya buɗan baki tayi magana idan tana wajen sai gashi ita ce ke ɗaga murya a gabanta. Ita fa yanzu ta kai matsayin da babu wani mahaluki da zai ɗaga mata murya, not her parents, not her husband and especially not 'ya'yan data haifa balle bare.

Hannu ta ɗagawa guards ɗinta masu suna Vayentha da Mistica nan da nan suka sara mata suka bar falon da sauri.
Bayan fitan su Bilkisu ta maida dubanta ga Mahirah tace "ni kike ɗagawa murya Aisha, are you cra...zy" ta wanke Mahirah da mari sai da yarinyar ta faɗi ƙasa.

"Nobody shouts at me. Nobody gives me orders. Kai ku sawa ran ku cewa daga yanzu babu mai fita daga gidan nan sai da izinina. Kachallah house or not babu inda zaku je daya wuce makaranta, Islamiyya ma na soke shi daga yau, zan sa malami ya dinga zuwa gida yana koyar da ku. Now get out of my sight"

Kafin ta ƙarisa maganar Nana ta yi sama a ɗari. Mahirah kuma ta miƙe riƙe da fiskarta tace "Mommy dan Allah ki bari mu tafi ko ba dan ni ba, Nana zata iya suma idan ta sake ganin macijin nan, Junior ma..."


"Oh! Ba za ki dena magana ba kenan. Mahirah ni kam aiko ki aka yi ne?"

Mahirah ta juya zuciyarta cike da ƙunci tana addu'ar Allah ya shiryi mahaifiyar su.

***



*Ya Hayyu Ya Qayyum. Ya Hayyu Ya Qayyum* abinda Asiya ke maimaitawa kenan lokacin da warden Maida ta buɗe ƙofar cell ɗinta.

"Asiya Kachallah ki fito Lawya zata ganki"

Lokacin da suka ƙarisa wajen da Barr. Zaytoonah ke jiranta sai Asiya ta yanki jiki ta faɗi ƙasa. Warden Maida ta daka mata tsawa akan ta tashi, sai dai tana ƙoƙarin tashi ta sake faɗuwa saboda jikinta da babu ƙwari. Warden ta sa kulki ta ɗan shureta hakan yasa Barr Zaytoonah ta daka mata tsawa.

Bayan fitan warden Maida Asiya ta ƙyaftawa Barr Zaytoonah ido, Zaytoonah ta ɗaga mata babbar yatsa alamar jinjina.

Ba wani magana suka yi mai tsawo ba daya wuce ta kwantar da hankalinta komai zai tafi dai dai.


"Barr Zaytoonah jaridar"

Zaytoonah ta fito da jarida daga jaka ta miƙa mata, hoton Gwamna Saifuddeen daya ke shafin farko ne ya ɗauke mata hankali. *Gwamna Saifuddeen Kachallah ya riƙe albashin ma'aikata*

"Wannan watan ma bai biya albashi ba ko?" Asiya ta faɗa a hankali

"ya rage albashin malamai ma ki duba shafi na biyar zaki gani"


Duk da Asiya ta sani shafi na biyar shine shafin da Zaytoonah ta rubuta mata saƙo amma a yanzu ta fi damuwa da chanjawar da Gwamna yai, wai wata biyu kenan bai biya albashin ma'aikata ba.

Ta buɗo shafi na biyar ta fara karanta saƙon da Zaytoonah ta rubuta.


"Zasu kawo Timothy mutumin da BBC eye tayi hira da shi, na san an riga an biya shi akan ya nuna cewa ke ce uwar ɗakinsa, amma kar ki damu na san yadda zan yi na rushe duk wani hadda da aka sa shi yai. There's hope, ki cigaba da addu'a"

Asiya ta rintse ido sai hawaye. Ba komai ke damunta ba fiye da yadda Gwamna ya koma azzalumi.


***


A zaman kotu na gaba, Barr. Zaytoonah ta gabatar da video da ta naɗa lokacin da warden Maida ke ƙoƙarin ture Asiya tana mata tsawa.
Ta yi nuni da cin zarafin client ɗinta da aka yi bayan kotu bata zartar da hukunci akanta ba. Idan Kotu ba ta bada bail ɗin Asiya ba hukumar human right zasu shigar da ƙara saboda an take haƙƙin Asiya.

Da wannan kotu ta bada bail ɗin Asiya, amma zata zauna under house confinement ba me zuwa wajenta kuma ba fita sai idan zata je kotu ko kuma idan akwai emergency.


Bilkisu na jin wannan labari ta dinga ihu dan a yadda ta tsara Asiya ba zata bar kurkuku ba sai ta serving jail sentence na aƙalla shekaru goma.

"Ban gane an bada bail ɗinta ba, yaushe za a gabatar da Timothy ne?"

"Sorry Boss Lady ya kamata Agent Dahlia ta zo da shi kotu wannan zama da aka yi amma bata zo da shi ba, i think... "

" Don't think Lamara, you should act" Bilkisu ta daka masa tsawa.


***

Ranan da aka maida Asiya gida haka ta dinga ƙarewa ɗakinta kallo domin ya mata faɗi, zaman sama da wata ɗaya da tayi a ɗan ƙaramin ɗakinta na kurkuku sai take ganin ɗakinta na gidan Gwamna ya zamo tamkar wani mansion.

Bata yi tunanin ganin kowa ba dan Zaytoonah ta faɗa mata cewa babu wanda zai zo wajenta aside ita da take lawyarta sai kuma masu kawo mata abinci. Ko ina Sumayya da Jummai suka shiga? bata gan su ba har aka shigo da ita cikin falonta. Kuma ya kamata ace suma sun tsaya a ƙofar gida kamar yadda Yaya Bello ya tsaya suka gaisa a tsanake.
Lokacin da ta yi sallar Isha sai ta kwanta dan ta huta amma sai ta kasa bacci, ta takure gefe guda tana maƙyarƙyata. Yadda sauro suka cizeta a kurkuku, ka ɗauka duka sauron cikin kurkukun ne suka tare a ɗakinta.

Washegari da safe kamar Barr. Zaytoonah ta san bata da lafiya, lokacin da ta zo sai ta taho da wata likita mai suna Dr Hoodah. Ko dama zazzaɓin jira yake ta sha magani, tana shan magani ko minti shabiyar bai kai ba ta fara kela amai. Ƙarshe dai allura aka mata aka saka mata ledar ruwa saboda ta samu ƙarfin jiki.

Kwananta na biyu a gidan da ta samu ta ci abinci sai gashi ta ɓarke da gudawa saboda system ɗinta ya fara sabawa da abincin prison.


***

A yau ma Gwamna ya sake yunƙurin zare jiki dan yaje ya duba Asiya amma yana buɗe ƙofar ɗakinsa yai kiciɓis da macijin Bilkisu ya fasa kai yana zaro harshensa. Ƙirjinsa ya buga dam yai saurin rufo ƙofan ya koma ya kwanta.

Tunda aka bada bail ɗin Asiya Bilkisu ta tare a ɗakinsa da kwana, rabon da ta kwana a ɗakin har ya manta, amma tunda aka sako Asiya ta dawo kwana ɗakinsa. Ta riga ta masa kashedin akan bata yarda ya je ya ga Asiya ba amma duk da haka idan ya kwanta sai wani sashe na zuciyarsa ya dinga ingiza shi akan yaje ya dubata musamman da yaga videon da ya watsu a media na yadda ake maltreating matar gwamna a kurkuku.

Gwamna ya dinga juyi ya kasa bacci, Asiya ce a ransa, Asiya yake son gani. Ƙarshe ya miƙe ya je ya ɗauko maganinsa ya sha guda huɗu maimakon ɗaya, duk da haka ya jima kafin bacci ya ɗauke shi...

***

Nana ta shige banɗaki a sulale dan bata so ta tayarda Mahirah. Tunda ta fara shan ƙwaya saboda ta dena jin tsoron macijin Mommy sai kuma muguwar sha'awar shan ƙwayar ya dawo mata fiye ma da da, sai abinma ya zamo kaman bata taɓa dena sha ba.
Ta buɗe wata baƙar leda da Kabir ya bata a school bayan ta bashi dubu goma cash. Jikinta har rawa yake lokacin data fito da ƙaramar takarda da aka nannaɗa ƙwayar a ciki, ta zuba rabin garin da ke cikin takardar akan cover na toilet sit, ta ja layi guda uku da garin cocaine da ta zuba sannan ta toshe hancinta ɗaya ta zuƙi garin da ɗaya hancin, ta girgiza kai sannan ta sake zuƙan sauran layuka biyu data zana sai a sannan ta fara jin kanta dai dai. Ta maida sauran ƙullin garin cikin leda ta cusashi cikin aljihun pyajamas ɗinta sannan ta koma ɗaki ta kwanta, wannan data shaƙa zai kaita har rana sauran na ledan zai kai mata zuwa dare, gobe Kabir zai kawo mata na dubu hamsin.

Bata jima da kwantawa ba Mahirah ta tashi sallar Asuba. Bayan ta yi alwala ta zo ta tashi Nana sallah.

Da alwalan da sallar duka babu wanda Nana tayi cikin nitsuwa dan dai tayi sallah ne amma bata san ma takamaimai mi take faɗa ba a cikin sallar. Tayi sujjada ya yi sau biyar kafin ta sallame. Hankalin Mahirah na kan Qur'ani da ta ke karantawa bata lura da irin shirmen da 'yar uwarta ta dinga yi a sallah ba.



***

Yau aka gurfanar da Timothy Igwe a gaban kotu, mutumin da yai iƙirarin matar Gwamnar jihar Congo yake wa aiki.

Bayan alƙalin Gwamnati yai masa tambayoyi. Tamkar wanda yai hadda haka Timothy ya dinga jero amsoshin tambayoyin babu ko fargaba ko wani gargada.
Bayan an ba wa Barr. Zaytoonah damar yi masa tambaya abinda ta fara yi shine tace a kira mata Asiya Kachallah. Gaba ɗaya sai aka fara kallon kallo saboda ga Asiyar da kowa ya sani tsaye a witness box.

Bayan matar da aka kira ta zo ta tsaya sannan Barr. Zaytoonah ta mayar da dubanta ga alƙali tace " wannan mata da kuke gani sunanta Asiya Kachallah, shekarunta hamsin da biyu a duniya kuma ta kasance cousin ga Alhaji Sani Kachallah"

"Objection my Lord Barr Zaytoonah ta sake layi daga abinda ake magana a kai"

Alƙali yace Barr Zaytoonah ta fito fili ta bayyanawa kotu mi take nufi.

"Ina so kotu ta tuna da bayanin Timothy Igwe a wannan video inda yace matar Gwamnar jahar Congo yake yiwa aiki, sannan ina so kotu ta tuna cewa yanzu kuma Timothy ya bayyanawa kotu cewa Asiya Kachallah yake yiwa aiki. A lokacin da yace matar Gwamnar jahar Congo yake yiwa aiki matan Gwamnan Congo su biyu ne, so Bilkisu Kachallah is also a suspect. Sannan yanzu da ya ce Asiya Kachallah yake yiwa aiki wannan mata mai suna Asiya Kachallah zata iya zama suspect saboda sunan client ɗina *Asiya Shahidah Faruƙ Baba* kafin aure da kuma bayan aurenta. So a nan, ya nuna cewa Timothy ya chanja magana kuma ƙarya yake yi"

"Objection my lord" Lawyan Gwamnati ya faɗa da ƙarfi.

"Objection sustained"

Barr. Zaytoonah ta girgiza kai dan ta san an siye alƙalin, idan ba haka ba abinda take faɗa yana kan hanya bai kamata a dakatar da ita ba.

"My Lord, Mr Timothy ya ƙi bayyana suna ne saboda yarjejeniyar da akayi...


Read / Download THE GOVERNOR'S WIFE

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album