Join Our WhatsApp Group

AKAN AIKINA Complete Hausa Novel Document by AKAN AIKINA


AKAN AIKINA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 35622



AKAN AIKINA

Reading Time: 2 Hours

Added On: 18, Oct 2023

Author: Ummu Maher ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 202.19 kb

File Type: txt

Views: 499+

Download: 254+

Last download: 1 day ago

Description/Story: ๏ปฟ๐Ÿ’š๐Ÿ’š๐Ÿ’š
(แƒฆห˜โŒฃห˜แƒฆ)(แƒฆห˜โŒฃห˜แƒฆ)
*AKAN A'IKI NA 2021*
(แƒฆห˜โŒฃห˜แƒฆ)(แƒฆห˜โŒฃห˜แƒฆ)
๐Ÿ’š๐Ÿ’š๐Ÿ’š



*Labarin gaske*โœ๐Ÿป


Na
*Rabi'atu.B.Abdullahi*
(Ummu Maher)
Miss green๐Ÿ’š๐Ÿ’š


_BISMILLAHIR_ _RAHMANIR RAHIM_

GABATARWA:dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah(S.W.T)Salati Mara Adadi Zuwa ga Manzon Rahma(S.A.W)


Tsokaci:Wannan littafin Ban rubuta shi don cin mutuncin wani/wata ba duk wanda yayi dai dai da rayuwarshi to yayi hak'uri akasi aka samu,Wannan littafin gaske ne ma'ana ba labari ne k'irk'irarre ba.


Sadaukarwa:Ga dukkanin mosayana Ummu Maher,Mu samman๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡

Nabila dikko
Nabiha Aminu
Ummu Najma
Zahara'u Nasir Aliyu
Amina .m.Baso

duk ina godiya,da dukkanin mutanen da ban ambato su ba to suyi hak'uri.

Abbakar.Ak saraki
da
Ahmad isah Koko
Inq godiya sosai da kulawarku gareni๐Ÿ™


*Babi na d'aya๐Ÿ“*



Malam!Malam!!Malam!!fito kaga i'kon Allah yarinyar nan ta suma,Malam ya fito da gudu yana kallon yarinyar ya kalli Inna Majaifiyarta yace maza ki d'auki Mumtaz ki ku fito bari in kirawo Alhaji mu tafi asibiti,Sunan yarinyar kenan Mumtaz.
Kafin Malam ya dawo Inna ta kalli k'afar Mumtaz sai taga jini yana malala kamar ruwa da gudu ta fito k'ofar gida tana kiran Malam.


*Wacece Mumtaz*
Mumtaz dai shine asalin sunan ta wanda Mahaifinta ya saka mata saka makon sunan Mahaifiyarshi ne ya saka wa Mumtaz, Asalin Malam Abdullahi Mahaifin Mumtaz y'an jihar Bauchine wanda sun kasance y'an kasuwa ne sosai gidansu suna siyar da kayan masa rufi ta hanyar ne suke samun na cin abinci kuma i'tace hanyar abincin su.
Kwatsam sai karayar Arzik'i ta samu mahaifinsu Malam Wannan abun ba k'aramin tada musu da hankali yayi ba.
dalilin da yasa karayar Arzik'i ta same shi shine Mahaifinsu su Malam Wato Alhaji Jibrin shine yanada wani aboki d'an asalin Maiduguri Alhaji Bukar kusan ma Amininshi shi ne sana'ar Alhaji Bukar shine siyar da dabbobi daga wannan gari zuwa wannan gari.
Kwatsam sai wataran Malam Bukar yakawowa abokinshi Alhaji Jibrin ziyara yaga yadda ya bunk'asa da kasuwancinshi na siyarda kayan masa rufi.
Abun ya tsayawa Alhaji Bukar har yaushe Jibrin zai zama haka a kasuwanci bayan ya fishi tunda ga nan Alhaji bukar ya kafawa abokinshi Jibrin tsana mai tsanani Ya fara bin bokaye don ya raba shi da dukiyarshi,Har yayi nasarar rabashi da komai nashi ya zamo duk abunda ya tab'a sai yayi asararshi tun daga wannan lokacin Alhaji jibrin Mahaifin Abdullahi ya shiga wani mummunan talauci ya zama na koda kayan da zaisa ma sun fara lalacewa sai ya shiga wanka sun bushe sannan ya saka su.
Ana haka wataran Alhaji jibrin ya fita neman tai mako gidan wani mai kud'i kawai sai ya jiyo kukan wata jaririya cikin bolar kusa da k'ofar wani gida kamar zai wuce kuma sai ya dawo ya duba yaga jaririya ce aka yar kyakkyawa da'ita kamar y'ar larabawa ya d'auketa hannunshi yana kakkarwa ya nufo gida,yana zuwa gida ya nunawa matarshi Adama mahaifiyar Abdullahi da yake ita kad'ai ce matarshi kuma Abdullahi shi kad'ai ne D'an ta don haka koda Alhaji jibrin ya kawo mata wannan jaririya ba k'aramin jin dad'i tayi ba sosai don haka ta rik'e yarinyar da hannu bibbiyu.
Abdullahi kuwa duk duniya ya nuna ba shi da wacce ya keso sai Wannan yarinya wacce Alhaji ya saka mata suna Maryam,Tun tana k'arama yake sonta duk abunda ya samo to na k'anwarshi ne Maryam koda ta girma sai abun ya koma soyayya sosai koda iyayen suka gani sunyi murna sosai.
don haka da taimakon y'an uwa da mak'ota aka hahhad'a akayi musu Aure.
Ranar bikinsu ne wani mummu nan labari ya samesu'cewae Mota ta buge Alhaji Jibrin ya mutu Har lahira.
Sunyi kuka sosai da mutuwar mahaifin nasu mai son Su da nuna musu k'auna.
Koda akayi Auren Inna Adama mahaifiyar Abdullahi tace su zauna agidan tunda gidan yana da girmanshi haka kuwa akayi suka zauna agidan.
Ana haka wataran Inna adama ciwon ciki ya kamatq cikin dare ko kafin a kaita asibiti tace ga garunku nan ta mutu har lahira tashin hankali sosai Abdullahi da Matarshi Maryam suka shiga,Ana hakane kuma Maryam ta samu Ciki watanshi biyar ya zube saboda rashin kulawa don har yanzu suna cikin talauci sosai.
Saida Maryam tayi shekara Goma sannan ta haifi Mumtaz wannan shine labarin Mahaifan Mumtaz.







*Ummu Maher ce* Miss green๐Ÿ’š



*Vote*
*Share*
And
*Comments*๐Ÿ“
*Tyiping*๐Ÿ–Œ๏ธ

ABOUT MY WORKโœ๐Ÿป
๐Ÿ’š๐Ÿ’š๐Ÿ’š
(แƒฆห˜โŒฃห˜แƒฆ)(แƒฆห˜โŒฃห˜แƒฆ)
*AKAN A'IKINA 2021*
(แƒฆห˜โŒฃห˜แƒฆ)(แƒฆห˜โŒฃห˜แƒฆ)
๐Ÿ’š๐Ÿ’š๐Ÿ’š


*Labarin gaskeโœ๐Ÿป*


Na
*Rabi'atu.B.Abdullahi*
(Ummu Maher)Miss green๐Ÿ’š๐Ÿ“—
ุจุณู… ุงู„ู„ู‡ ุงู„ุฑุญู…ู† ุงู„ุฑุญูŠู…
_________________
______
๐Ÿ…™๏ธŽ๐—ฎ๐—ฟ๐˜‚๐—บ๐—ฎ๐—ถ ๐Ÿ…ฆ๏ธŽ๐—ฟ๐—ถ๐˜๐—ฒ๐—ฟ๐˜€ ๐Ÿ…๏ธŽ๐˜€๐˜€๐—ผ๐—ฐ๐—ถ๐—ฎ๐˜๐—ฒ๐—ฑ๐Ÿ“š๐Ÿ–Š
https://www.facebook.com/101679598253281/posts/101680068253234/?app=fbl
_Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa illmantarwa, nishadantar tare da fadakarwa da jama'a bisa harshen hausa_

๐Ÿ”๐Ÿ…™๏ธŽ๐Ÿ…ฆ๏ธŽ๐Ÿ…๐Ÿ”



*BABI NA 2*๐Ÿ“

Malam kazo da sauri Mumtaz tana zubar da jini da sauri "Alhaji yace to Mumtaz d'ince babu lafiya yanzu Malam yake fad'amun bari muyi sauru mu tafi Asibiti kiyi sauri ki fito da'ita.
Umma tayi saurin komawa gida ta fito da Mumtaz suka tafi Asibiti,shan kwanarsu kefa wuya su hancin motarsu Amal ya kawo kai Amal tace Mama kamar Motar Dadyne naga yafita daga gidan kuma naga yana sauri sosai Allah dai yasa lafiya Mama tace to Amin.
Amal da zumud'inta ta nufo gidansu Mumtaz tana son ta nuna mata kayan da ta suyo akasuwa sai taga gidan Arufe an saka kwad'o ta ce Afili to yau kuma ina su Umma suka tafi dukkansu Allah dai yasa lafiya tayi saurin komawa gida don gayawa Mamanta.
Likitan tace Alhaji munyi iya k'ok'arinmu don ganin cikin jikinta ya tsira Amman hakan ya faskara sakamakon maganin zubarda ciki da tasha.
Malam da Alhaji harda Umman Mumtaz saida abun ya tab'asu sosai sakamakon jin wai Mumtaz ce take da ciki ne da'ita to waye yayi mata cikin? suka had'a baki wajen fad'ar hakan likitan kuwa har tayi tafiyarta ta barsu anan sunata sambatu su kad'ai.
Banko k'ofar da'akayi ne yasa Mumtaz bud'e idonta da k'er don jin yadda sukayi mata nauyi sosai kamar ba jikinta idon yake ba.
Umma tace Wallahi Mumtaz kin cuceni yanzu daman cikine dake kika d'aukomun abun kunya kinsan kuwa abunda kika Aika ta,yanzu duk i'rin tarbiyyar da muka baki abanza saida kika zubar mana da mutunci yanzu sai ki fad'amun waye yayi miki ciki,eyeh dake nake kike kallona munafuka,Kuka na shigayi ina cewa Wallahi Umma ban zubar muku da tarbiyyar da kuka bani,k'addarace tafad'amun Umma ta k'ara sha k'o Mumtaz tana tambayar cikin d'aga murya wanda duk wanda ke kusa zai iya jin ta.
Su Alhaji ne da Malam mahaifin Mumtaz suka shigo cikin d'akin saboda yadda suka jiyo hayaniya cikin d'akin,Alhaji yace haba Umma kiyi hak'uri ki k'eleta tayi mana bayani da kanta,Umma ta saki Mumtaz tana haki tare da hararar Mumtaz.
Alhaji yace Mumtaz ki fad'i tsakani da Allah Muntaz ki fad'a mana waye yayu miki ciki,domin idan kika b'oye mana Allah yana sama yana kallan ki don haka ki fad'ama na kinji.
Mumtaz ta share hawayen da ya b'ata mata fuska tace hak'ik'a zan gaya muku gaskiya,Alhaji yace to Mumtaz muna jinki?Muntax tayi shiru tabbas tana son gayawa i'yayenta gaskiya Amman tana tsoron Abubda zaije ya dawo domin tasan Iyayenta baza su tab'a i'ya jayayya da iyayen wanda yayi mata wannan Aika Aikar ba saboda nesa ba kusa ba sunfi duj yadda kake tunani kud'ine dasu kamar Bankin CBN saboda suna da kud'in da ko shugaban k'ada bazai had'a k'afa dasu ba,koda Kuwa Alhaji ne Mahaifin Aminiyarta Amal.
don haka sai tayi k'arya dacewa,Don Allah Umma ku ya feni hak'ik'a wadannan mutanen da suka saceni wata biyu da ya wuce har nayi tsawon wata biyu agidansu sune suka yimun wannan Aika Aikar mu biyarne y'an mata kuma duk saida suka lala ta mu.
Alhaji yace to meyasa Mumtaz baki gaya mana ba don mu d'auki mata ki kinga yanzu gashi sun sakaki cikin wani hali muma sun saka mu tabbas biri yayi kama da mutun tabbas nasan Mumtaz ba mazina ciya ce ba bazata tab'a Aikata abunda kuke zarginta dashi ba.
Malam ya shard'e wata zufa da ta tasomai yace hak'ik'a nafi kowa sanin halin Mumtaz yarinyace kamila maijin tausayin iyayenta akoda yaushe gata da Addini,hak'ik'a mungodewa Allah da yasa cikin ma ya zube saidai muce Allah ya bata lafiya dukkansu suka Amsa da Amin.


*Asalin labarin rayuwar Mumtaz da kuma abunda ya shafi rayuwarta dan gane da cikin da akayi mata*


โ˜…โ˜… โ˜…โ˜…
Tunda Muntaz ta taso da wayonta taga iyayenta suna cikin wani matsanancin talauci sosai,hakan yasa ta taso da jin tausayin iyayenta duk abunda tasan zata tai maka musu dashi tanayi indai baifi k'arfinta ba akan Aikin gida tun tana k'arama take Aikin gidansu,sannan Mahaifinta yana faskare dashi suke ci suke sha don haka duk ranarda Mumtaz taga Mahaifinta ya tashi zai tafi Aikin faskare sai ta tashi tace nima Malam zan bika,don gaskiya bazan iya bari kana shan wahala ba jibi yadda fa hannunka yake duk ya farfashe,Sai Malam yayi dariya yace Mumtaz kenan kinga duk aikinnan da nakeyi don ke da mahaifiyarki ne don hakk'inku yana kaina kuma sannan inason insakaki makaranta kiyi karatu kinji,sai Mumtaz ta wangale kyakkyawan bakinta tace Malam nidai i na girma inason inzama irin matar nan da kullum kake jinta aradion ka wadda take shiri nima inason inzama mai Aiki a gidan Radio don in taima ka muku da jama'ah baki d'aya.
Malam kuwa inda sabo ya saba don kusan kullum sai sunyi wannan hirar da y'arshi tilo aduniya wato Mumtaz ya lura yarinyar ta taso da wani ginshik'i azuciyarta wanda ta keso ta cika burinta akanshi Ma'ana tana son ta zama ma'aikaciyar gidan Radio ma'ana y'ar jarida don haka duk ranarda wannan zancen sai yaji yanason ya cika mata burinta,don haka sai yace Mata babu komai Mumtaz Insha'Allah zaki cika burinki na zama y'ar jarida don ni zan tabbatar miki da kin cika burinki don Insha'Allah zan sakaki makarantq don kema ki amfana da karatu kinji.
Suna wannan abun Kullum Umma sai ta lab'e tana jinsu cike da sha'awar y'arta da mijinta Allah ya sani suna son su bunk'asa rayuwar yarinyar wajen sakata makaranta don ta Amfana Amnan ya zamar musu dole wajen cikawa Mumtaz burinta bunk'asa karatunta har ta zama y'ar jarida kamar yadda kullum take muradi.








To fah wasa farin girki don yanzu wannan labarin ya soma kubiyoni don jin tarihin Mumtaz kachokan.





*Ummu Maher ce*


*Vote*
*Share*
And
*Comments*โœ๐Ÿป
*Tyiping*๐Ÿ–Œ๏ธ


ABOUT MY WORKโœ๐Ÿป

๐Ÿ’š๐Ÿ’š๐Ÿ’š
(แƒฆห˜โŒฃห˜แƒฆ)(แƒฆห˜โŒฃห˜แƒฆ)
*AKAN A'IKINA 2021*
(แƒฆห˜โŒฃห˜แƒฆ)(แƒฆห˜โŒฃห˜แƒฆ)
๐Ÿ’š๐Ÿ’š๐Ÿ’š


*Labarin gaskeโœ๐Ÿป*


Na
*Rabi'atu. B.Abdullahi*
(Ummu Maher)
Miss green๐Ÿ’š๐Ÿ“—

ุจุณู… ุงู„ู„ู‡ ุงู„ุฑุญู…ู† ุงู„ุฑุญูŠู…
_________________
______
๐Ÿ…™๏ธŽ๐—ฎ๐—ฟ๐˜‚๐—บ๐—ฎ๐—ถ ๐Ÿ…ฆ๏ธŽ๐—ฟ๐—ถ๐˜๐—ฒ๐—ฟ๐˜€ ๐Ÿ…๏ธŽ๐˜€๐˜€๐—ผ๐—ฐ๐—ถ๐—ฎ๐˜๐—ฒ๐—ฑ๐Ÿ“š๐Ÿ–Š
https://www.facebook.com/101679598253281/posts/101680068253234/?app=fbl
_Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa illmantarwa, nishadantar tare da fadakarwa da jama'a bisa harshen hausa_

๐Ÿ”๐Ÿ…™๏ธŽ๐Ÿ…ฆ๏ธŽ๐Ÿ…๐Ÿ”



*BABI NA 3&4*๐Ÿ“

Mumtaz ta taso da wata irin baiwa wadda take bawa kowa mamaki saboda yarinyar akwai gaskiya bata tab'a yin abu ta nuna rashin gaskiya kosa zaka kashe ta sai ta fad'i gaskiyar lamari,Ana haka Malam ya samu Aikin nik'a ya nayi albashinshi na farko ya saka Mumtaz makaranta da shi Mumtaz kuwa ta ringa murna saboda mahaifin nata ya cika mata burin ta nayin karatu,Kullum Malam i'dan zai tafi wajen nik'ansa tare suke tafiya da Mumtaz ya sauketa amakaran ta ya siya mata biskit da alawa sannan ya tafi wajen Aiki yana mata Bye bye i'tama Mumtaz bata tafiya sai taga Mahaifin nata ya tafi sannan take shiga aji.
Karatu sosai Mumtaz ta keyi don bata wasa a makaranta sam,ga ta bata surutu a'aji kawai i'ta karatu ta saka a'gabanta.
makarantar Mumtaz tayi nisa gashi Allah ya taimaki Malam yana biya mata kud'in makarantar ta akan kari baya bari lokaci ya k'ure bai biya ba kuma yana jin dad'in yadda take karatunta tana mayar da hankali,Mumtaz duk cikin ajinsu babu wanda ya kaita k'ok'ari da mayar da hankali wajen karatu gata da k'ok'ari don duk term ita take zuwa na d'aya ko Na biyu A'ajinsu haka duk Malam man makarantar sun san cewa Muntaz tana da baiwa sosai gata tun tana k'aramarta akwai ta da hankali da hangen nesa.
Mumtaz tana dawowa daga makaranta ta ajje jakarta ta cire unifoam d'inta na makaranta ta fito tsakar gida don taya Umman ta Aiki,ta gumin da taga Umman ta tayine tace Umma lafiya me yafaru kike ta gumi me akayi miki?ta jerowa Umman tata tambayoyi lokaci d'aya,Umman tata tayi saurin cire ta gumin da tayi tace Mumtaz kin dawo ne?Eh Umma na dawo Amman meya faru naga kin rik'e kunkuminki?Umma tace Mumtaz nasan kina jin yunwa ko?Eh Umma inajin yunwa sosai me kika dafa,Umma tace Mumtaz babu abunda na dafa shiyyasa ki kaga nayu tagumi kuma na buga na buga ban samu ba,Mumtaz tace to Kuma Umma shine kika saka kanki cikin damuwa ki daina damuwa kinji,Indai na girma na samu Aiki zaki huta indunga siyo miki kayan dad'i,Umma tayi murmushin da yafi kuka ciwo tace to Mumtaz Allah dai ya cika miki wannan burin naki,Mumtaz tace Amin Ummana.
Umma tace yanzu ki tashi akwai wata y'ar sauran kamu da na dama miki da kwad'on k'anzo ki tashi kici kinji Umman ta kalleni tana mai jin tausayin d'iyar tata.

Akwana atashi asarar mao rai wataran asamu aci wataran kuwa Iyalan Malam mahaifin Mumtaz basa cin abun abinci wataran haka suke kwana abunsu,gashi Allah ya basu yarinya mai hankali da tausayi ko ta samu ko kar ta samu bata tab'a d'agawa iyayenta hankali wai don tana jin yunwa ko wani abu haka take hakura taci koda bai mata ba haka ta ke hak'ura taci.
Har Allah ya kawo lokacin da su Mumtaz suka zana jarrabawar fita daga primary Mumtaz da iyayenta sunyi murna sosai gashi ta fito da saka mako mai kyau.
Mumtaz tace Malam ina Addu'ah Allah ya cika mun burina na zama y'ar jarida sai dai bansan aikin da zanyi ba in taimaka muku ba kuna...


Read / Download AKAN AIKINA

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album