Join Our WhatsApp Group

SILAR DA NAMIJI Complete Hausa Novel Document by SILAR DA NAMIJI


SILAR DA NAMIJI

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 9728



SILAR DA NAMIJI

Reading Time: 0 Hours

Added On: 03, Nov 2023

Author: Mujahida Matar Malam ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : 07064904617, 07031012948

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 63 kb

File Type: txt

Views: 544+

Download: 104+

Last download: 24 hours ago

Description/Story: *SILAR ƊA NAMIJI😭!!!*

*FREE BOOK*


*LABARI TSARAWA DA RUBUTAWA MUJAHEEDAH (MATAR MALAM) HEEDAH HAYDAR OSTHMAN,... AMMYN KHAUSAR CEEE.....*



https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c










Godiya da yabo dika suntabbata ga Ubangijin talikai mairayawa dama kashewa A sanda yaso, ina mai godiya ga Allah dayaban damar kawomu wannan littafin mai ɗauke da darusuka da dama Acikinsa ina roƙon Allh yarda yaban damar farashi lafiya Allah yaban damar kammalashi lafiya,...



Ada nason jingine typing gaba ɗaya zuwa koda bayan sallah ne ganin watan da muke ciki Amma bisaga wasu dalilai zan fara wannan littafin kuma zan sake muku shi, Amma sai ƙarfe 7:40 bayan shan ruwa A sannan zandinga posting ɗinsa insha Allh, kuma bazaku sameshi kullum ba saboda sabods ina Azimi kuma inada Ayuka ga rashin wuta banida chager so kubiyoni sannu A hankali danjin wannan ƙasaitaccen Littafin maitaken *SILAR ƊA NAMIJI!!!* Kuma tsaraba ne gareku fansss na watan Ramadan.....






*Dikkan ni maisona inasonai basai na faɗe kuba ku kunsan kanku masoyana ngd ngd ngd Allh yabar Ƙauna*



JINJINATA GA ƘUNGIYATA DAMA MEMBERS NACIKINTA WATO ROYAL STAR WRITERS ASSICIATION





•••°°°•••°°°•••°°°•••°°°•••°°°••

*BISMILLAHI RAHMANI RAHEEEM*


```WEDNESDAY 6/4/2022----- 5 DAY'S TO RAMADAN```



*SILAR ƊA NAMIJI!!!😭😭😭 FREE BOOK*

*PAGE 1&4*



Banzame ko inaba sai
A harabar *HINDAT GOVERMENT GIRLS COLLAGE SCOOL* Na hango dandazon ƴan mata natafitowa Acikin makarantar ƙaramar secondry ce kuma ta gwamnati ce A garin sokoto, Sokoto garine maitarin Albarkatu kala kala musamman Ada zuwan sababin shuwaga banni ne yaɗan rusa sokoto bama iya sokoto ƙaɗaiba garuruwa da dama A wannan lokacin sun samu nakasu na matsin rayuwa rashin tattalin Arziki dama rashin Kwanciyar hankali, Amma dik wanda yasan matan sokoto yasansu da kamewa tsoron Allah ilimi tebiyar dama kame kai, badai ina ƴar sokoto yasani faɗar hakan ba A'a sanin gaskiyar garin yasa nafaɗe hakan.




Wata matashiyar budurwa na hanga saifaman sauri take tana tafiya bisaga dukan Alama gida tanufa,



Abayanta taji Anata ƙwaɗamata Kira Deeyam Deeyam kitsayani mana!"




Badan tasoba taja tatsaya yauɗin ma tana tare da ƴan iskan samarin nan dake bata haushi yau kaganta da wannan gobe da wannan jibi da wancan kullum kalan saurayinta daban Neera kenan!



Saida suka ƙaraso kusa da ita neera Tace," Haba deeyam kullum Akatashi bakisan kijira mutum ba saikawai kikama hanya kiyi tafiyar ki? kuma A ƙasa bayan kinsan Anazuwa ɗaukata maza kizo kishiga ga motanan Haris yazo ya sauke mu gida,"




Cikin takaici da ganin irin rayuwar ƙawarta Neera yasa batace Uffan ba takama hanya tayi tafiyar ta Abunta tanaji tana faman ƙwalamata kira Amma bata tsayaba.




Bataji komai ba A ranta takoma tashiga tanafaɗin "yi haƙuri nasaka jira tariga tawuce,"




Murmushi yayi danshi inda sabo yasaba da halin Deeyam yasani sarai koda duniyace zata taru bazata taɓa shiga motarsa ba, ta tsane maza irinsa shigo yafison rayuwar sakewa,






Wani ɗan madaidaicin gida naga tashiga talakawa ne gaskiya Amma sunada rufin Asiri Itaƙaɗaice A gidansu shiyasa tana shiga tafara shirya wasu kayan dake watse Mama tafito daga banɗaki tanafaɗin A'a ƴan makaranta Andawo? kings daina wannan kankancin naki maza kije kicire kayanki ki huta kici Abinci da sallah daga baya kyayi waɗannan Ai'yukan,"




"To mama,"



Baba dake shigowa Yace," Allah yabarmun ke mamana ƴata tagari ɗaya fiye da dubu ni wllh kinfiye mun natara yara dan yawan yara wani lokacin bakomai saitarin matsala ka kasa tarbiyarsu suzo su Addabi Al'umma da musulunci, Allah nagdema dakaban ƴa tagari kamar deeyam,"



Murmushi kawai tashige ciki tabarshi suna fira da Mama...







Neera kuwa saida suka jima A motar sunafirarsu tabanza kafin tashiga gida,



Saida tagama laɓaɓe ta tabbatar Abbanta bainan sannan tashiga Kaitsaye Abunta, Mamarta bata tanbayets meya tsaidataba,

kishiyar Mamar ce Tace," Neera meyatsaidaki haryanzu bayan dik ƙannan ki da yannan ki sundawo kece kawai kika jima haka ina kikaje ne,"?





Tana tura baki Tace," Baishafeki ba," tawuce Abunta Umma najinta batace komaiba



Girgiza kai kawai Mama hanna tayi taci gaba da aikinta tana roƙon Allah yasawa bakinta linzami tadaina magana Akan harkar Neera dan talura Uwarta ke ɗaure mata gindi, batun yanzu ba tana ɗauko rigimu iri iri Amma koda yaushe Umma bin bayanta take har Abbansu tasha rigima dashi Akan ƴaƴanta musamman Neera,

A gidan su 2 ne matan Alhaji Shu'aibu Mariya da jamila, mariya nada ƴaƴa 3 2 maza ɗaya macce itace Amarya, sai jamila nada ƴaƴa 5 namiji ɗaya huɗu mata, Acikinsu 2 Neera da jasmin suke da rayuwa iri ɗaya kansu narawa sosai Duniya na ruɗinsu, Neera nada matiƙar farin jini fiye da tinanin maikaratu, tanada ƙira da siffa mai kyau ita farace saidai tanada babban jiki tintana 12 take Masha Allah balantana yanzu datake 16 year's komai ya bayyana Aƙirarta idan kaganta karantse takai 20 years, samun damar hakan yasan maza dayawa ke bibiyar rayuwar ta, Abba na ƙoƙari sosai gurin ganin yagyara tarbiyarta Amma Umma na warwarewa Acewarta baza'a takura ƴarta ba...........







*NIKUWA MUJAHEEDAH MATAR MALAM NACE" MUDDIN KIKACE ƳARKI BAKISON GANIN KUKANTA TOFA TABBAS ITA ZATASO GANIN KUKANKI, HUNMM TO MUDAIJE ZUWA..*





_Labarin yana kamanceceniya da rayuwar gaskiya Na wata, idan yazamo yazo daidai da ke to kiyi haƙuri kisani badanke nayi ba kawai dai kiyi ƙoƙari kibi littafina idan kinga rayuwar kaga rayuwar tayi kalan taka to plazz kaje kagyara ma'ana kasauya hali........_




*Allh yasa mudace MUSHA RUWA LPY RAMADAN KAREEM*








WhatsApp number 07064904617 or call number 07031012948






_BASEERATA ITACE ARZIKINA😍_




[07/04 6:26 am] 🥰Mujaheedah🥰 (MATAR💖MLM): https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c


*SILAR ƊA NAMIJI!!!* *FREE BOOK Page 5&10*





```RUBUTA LABARI DA TSARAWA 🥰MUJAHEEDAH🥰 (MATAR 💖 MALAM) HEEDAH HAYDAR OSTHMAN..... AMMYN KHAUSAR CEEE....```



*BESIDE IN TRUE LIVE STORY,...... SHOURT STORY*




_Ina godiya sosai da jajircewarki gurin yin sharing wannan littafin nawa Mmn Hibba Allh yasaka da Alkhairi km Allh yabar zumunci ina godiya sosai, dama waɗanda kemun sharing batare da nasani ba dikanku ina gdy Allh ya biyaku_





_Barkanmu da shanruwa Abokai Fatan kowa yasha ruwa lafiya, Allh kasa muna cikin ƴantattun bayi, Allh kasa munacikin bayinda Akama rahama haɗida rangwame Afuwa dama sassauci, Allh kabawa ƙasarmu nageri'a zaman lpy da kwanciyar Hankali Alfarmar fiyayyen halitta Annabi Muhammad S.A W. ✨🌙RAMADAN MOUBARAK✨_






Ƙawance Deeyam da Neera Allah ne kawai ya haɗashi domin da bayin Allah bane da tini sun rabu dan ko ƙaɗan halayyarsu ba iri ɗaya bace.






Tinda safe Nawar yafalka yahau shirye-shiryen zuwa sokoto dan gabatar da wata wani taro da babansa zai jagoranta saikuma fita Ƙasar waje ya kamashi saiya tura Ɗan nashi Nawar, Nawar matashi ne kyakykyawa fari sol kamar idan ka taɓashi jini zaifara zuba daga fatarshi, A kwai wanka ga ƙwalisa saidai sam bai ɗauke Halayya maikyau irin ta Mahaifiyarsa yariga ya sangartu da ƙuɗi baisan rashi ba dole dik Abunda ya keso yasamu, Hakan yasa ba wata Hotel da cholove daka babban birnin Rives da bata sanshi ba, yakan taɓa shaye shaye ga shegen biyar matan tsiya Momyn sa kanyi faɗa sosai Amma ga banza dan baji zaiyi ba,



Ya shirya tsaf cikin riga da wando na suit black hatta glass ɗin idansa da ta kalmansa zuwa Watch Hand ɗinsa black ne,Masha Allh kawai nace dana ƙare masa kallo danfa Nawar Ajin farko ne gurin kyau da kwalliya,


Saida ya sauko ƙasa ya ɗagawa Mahaifiyarsa hannu kawai yasa kai yafice Abunsa baiko bi takan maganar da take masa ba,


" Allah kashiryamun wannan yaron Mommy tafaɗa cike da damuwar halin nasa,"




Baijima ba jirginsu ya sauka kankace me Motoci sunzo daga Gwamnan garin sun ɗaukeshi zuwa ƙasaitaccen holl ɗinda za'ai taron..




Bayan gama taron Aka bashi driver dan maidashi Air-port ɗin Sharara gudu kawai driver keyi dan Nawar sai zazza gamasa masifa yake Akan yayi sauri yana da wani badget dazai gudanar A river.





Deeyam yau tatashi da ciwon kai dan ko School bataje,

Mama tace "Mamana kidaure kije bakin titinnan kisiyo magani kinji,"



Da to kawai ta ƙarɓa dan baƙaramin jin jiki take ba, Hijab tasa har ƙasa tahau hanya , yau deeyam bata tsaya duba titin ba saboda tsananin zafin ciwon kanta kawai ta hau, tindaga nesa suka zuba mata hong Amma ina sam bataji danma kamar bata hayyacinta wannan lokacin, jikake kipppppppp yabuge Deeyam tafaɗi A gun ƙasa..................




*Plzzzz comments and shariya dan Allah🙏🙏🙏🙏🙏🙏*


WhatsApp number 07064904617 or Call number 07031012948




_BASEERATA ITACE ARZIKINA😍_
[07/04 7:38 am] 🥰Mujaheedah🥰 (MATAR💖MLM): https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c


*SILAR ƊA NAMIJI!!!* *FREE BOOK Page 11&15*





```RUBUTA LABARI DA TSARAWA 🥰MUJAHEEDAH🥰 (MATAR 💖 MALAM) HEEDAH HAYDAR OSTHMAN..... AMMYN KHAUSAR CEEE....```



*BESIDE IN TRUE LIVE STORY,...... SHOURT STORY*





Ya Allah Wamuka bige kuma? tafiyar tawa tasamu tsaiko kenan, Cewar Nawar Atare suka fito shida driver ɗin har wasu mutane sunfara zagaye ta suna faɗin "Innalillahi Deeyam cefa,"

Saida ya maimaita sunan A zuciyarsa kafin ya iya cewa "ko zaku sata mota mukaita Asibiti mafi kusa Anan,"?


Wani daga cikin mutanen yace," ƙwarai kuwa da taimakonsu suka sata motar, wani daga cikin mazan Unguwar yaso bin bayansu Acewarsa baisan halinsu ba Amma kuma ganin motar gidan gwamna Hankalinsa ya kwanta yafasa bin nasu.



Har suka ƙarasa Asibiti idansa nakanta ganin sam bata motsi amma dik da hakan haryanzu jikinta Arufe yake shif Aransa Yace wannan kodai yar malamin garin nan ce?


Sani driver ne ya ƙatseshi dafaɗin Ankawo yallaɓai,


Fitowa yayi tare da ɗan kamota saida yaji wani bugawar zuciya da ƙarfi kamar A sannan yafara taɓa macce Abun ya bashi mamaki sosai ganin yasa harka da mata manya masu jini Ajika baiji komai ba Amma wannan daga kamata sai wani shock? lalle ɗiyar malamin garin ce.



Nurse's ɗin Asibitin suka nufosu da sauri suka ƙarɓe zuwa ciki, ganin motar daga gidan Gwamna yasa cikin mintuna ƙalilan Aka rufu kanta ƙarin ruwa sai Allurai kawai suka mata,



A ƙofar Ɗakin ya tsaya saifaman safa da marwa yake yana duba Agogon hannunsa yanata zuba tsaki,

Fitowa dr. yayi, Sani ne ma yayi ƙarfin halin cewa wane hali yarinyar take,"?



Dr Yace "muje Offi ko,"?



Nawar Yace," basai Anjecan ba muna sauri dr bafa jininmu bace kawai.......," gudun kar yace sai Ankawo ƴan sanda gashi kuma shi yana sauri yasa ya sauya Akalar zancen dacewa, kawai kafaɗa muna Anan munason muwuce ne,"




Girgiza kansa dr yayi dan yalura wannan giyar naira na ɗibarsa "Owk ba komai A yanzu kuma batada wani dogon rauni kawai taɗan goggoge ne Amma shima basosai ba sannan tana fama da wani matsanancin ciwon...,"



"Kaga dr wannan baishafe muba dan bamu muka ɗaura mata shi ba so yanzu ƙalau take ko"?



ɗaga masa kai kawai yayi "data farka kwa iya wucewa Amma Asiye waɗannan medice's ɗin"

Miƙama masa takardar yayi Sale yaƙarɓa shikuwa yanufe cikin ɗakin yanamai jin takaicin rasa Shagalin ligth beb in the world,


Kwance take fuskarta fayau still hijabin najikinta ɗan taɓe baki kawai yayi kafin yakoma gefe ya zauna yana faman zuba tsaki,



A ƙalla sai kusan Awa ɗaya tafarka da salati A bakinta,


Tinda yaji yarda take Ambaton Allah yasa ya maida kallonsa gareta ko ƙyafta idansa bayayi Wannan shine karo nafarka daya ga macce bayan mahaifiyarsa tafalka da Ambaton sunayen Allah,



Saida tagama Addu'o'inta sannan tafara yunƙurin tashi dama buɗe idanuwanta cikin nasa idan nata suka faɗa kallon kallo suka shigayi naɗan wani lokaci ita tanamasa kallon rashin yarda dama waye shi, Shikuwa kallon ma'anoni da dama yake mata haryanajin inama Ace ita ya Aura tinda bisaga dikanku Alamu kamilace ita.



"Sani Yaƙatse musu tinaninsu dacewa sannu ƴammata kin falka? ko zaki iya miƙewa muje gida ƴallaɓai nasauri ne,"



Maida kallonta tayi kan sani Ahankali Tace," meya kawoni nan,? su waye ku,"?




Murmushi yayi yayi kafin yabata labarin dik Abunda yafaru.



Ɗan zabura tayi da sauri ta miƙe tsaye hartana fisge canula ɗin hannunta,



Nawar yamatso da sauri kusa da ita yana mai kama hannunta inda tafisge canula ɗin jini na ɗiga wani bandage dake gurin yaɗauka ya maƙala mata yanajin bugawar zuciyarta daya riƙe hannunta kawai, Ahankali Yace," kada kiyi wasa da lafiyarki dik halinda kika tsince kanki Aciki muje musauke ki gida daganan muwuce muma,"



Kallonsa tayi tare da ɗan kwace hannunta daga nashi tana mai sauke idata ƙasa dan haka kawai taji gabanta nabugawa game dashi, cikin ƙarfin hali Tace," nagode zan iyakai kaina ma,"





Murmushinsa maikyau yayi kafin Yace," mu muka bigeki dan haka muzamu sauke ki gida malama nasan kina tsoro ko? to kada kidamu bamai cutarwa tsakanin nidashi, muje kawai,"



Badan tasoba tabi bayansa tanajin faɗuwar gaba,


Saids yatsaya babban phamacy yasaye maganukan da Abincin take Away sannan suka nufe kwatancen nata zuwa gidansu..


Bawanda yayi magana cikinsu harsuka isa saidai dik ta takure kanta gefe, lokaci lokaci yakan ɗan murmusa idan yaga yadda tawani takure kamar tahaɗu da dodo,

Suna tsaida motar tayi saurin fitowa hakan yayi daidai da fitowar baba daga gidan dan zuwa nemanta, ganinta cikin mota haɗaɗɗiya ba ƙaramin ɗa gamasa hankali yayi ba,

Gurinsa tanufa tanamai durƙusawa tana gaidashi kafin yayi magana Nawar yafito yanufoshi.


Cikin ladabi ya sunkuya yagaidashi yabashi labarin komai,

Baba Yace," to mungode kashiga daga ciki mana,"


"A'a baba ina sauri ne banan ne garin mu ba dik da dai narasa jirgina na yau saigobe zan koma Amma insha Allah kafin nakoma gobe zan dawo yanzu ga magungunnan ta Ajikinsu dik A kwai yarda za'ai Amfani dasu,"



Sallama sukayi Akan gobe zaibiyo sannan yawuce..............





WhatsApp number 07064904617 or call number 07031012948




_BASEERATA ITACE ARZIKINA😍_
[08/04 12:09 am] 🥰Mujaheedah🥰 (MATAR💖MLM): *SILAR ƊA NAMIJI!!!* *FREE BOOK Page 16&19*





https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c




```RUBUTA LABARI DA TSARAWA 🥰MUJAHEEDAH🥰 (MATAR 💖 MALAM) HEEDAH HAYDAR OSTHMAN..... AMMYN KHAUSAR CEEE....```



*BESIDE IN TRUE LIVE STORY,...... SHOURT STORY*




_Inama ɗaukacin dukan jama'ar musulmai barkda shanruwa Allah yaƙarɓe Ayukanmu nagari marasa kyau Allah ka yafemuna RAMADAN MOUBARK_





Gidan Gwamna ya koma suka zauna da najib ɗansa harzuwa goben dama Akwai sanayya tsakaninsu kusan tare sukayi karatu...


Read / Download SILAR DA NAMIJI

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album