Join Our WhatsApp Group

HALITTAR ZUCIYA Complete Hausa Novel Document by HALITTAR ZUCIYA


HALITTAR ZUCIYA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 21886



HALITTAR ZUCIYA

Reading Time: 1 Hours

Added On: 21, Oct 2023

Author: Rashuna ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : 09037093702

Book License : Paid

Category: Love Novels

File Size: 118.27 kb

File Type: txt

Views: 656+

Download: 208+

Last download: 13 hours ago

Description/Story: [9/18, 2:59 PM] Mtn Number: BEBE'ARTH

2023

Wattpad@Rashuna
Mama Jiddah
Heenah
Silar soyayya
Masoya
Rabee'ah
Babbar Cuta
Muguwar surika
K'addarar Rayuwarmu
Cikin Duniyarmu500
Katanga500
Cin Amana500
Wadjda500
Halittar ZUciya500
Compleet guda hud'unnan ga masu buk'ata zan iya baku a 1500 da kuma samun damar karanta HALITTAR ZUCIYA KYAUTA.



HALITTAR
ZUCIYA

(1)

Shimfid'a

Jajare garin jajaye in kaga bak'i to bak'o ne ya ka zo,wannan inkiya ce ta garin Jajere.Jajere gari ne na fulanin damaturu,Malam Madu yana d'aya daga cikin mutanen garin,haifaffan garinne shi tun iyaye da kakanni,mahaifansa ne suka wanke Mariya suka bashi,Mariya kamar 'ya take a gurinsu saboda su sukayi rik'onta tun tana yarinya,sun tsinceta ne a wani kango da ake gini suka rik'eta ba tare da k'yamata ba,suka kuma d'auketa suka bawa d'ansu duk saboda soyayya,anman Madu sam ba ya k'aunar Mariya,ya karb'i auranta ne saboda biyayya ga iyayansa,suna zaune,lafiya ba mai jin kansu duk da Mariya tana matuk'ar hak'uri da wasu halayen na Madu dan baza ta iya fitowa ta fad'a ba ne ana haka ta samu ciki inda ta haifi 'ya mace,zo kuga ruwan tijara gurin Madu shi ba ya son mace,mace ai k'arin wahala ce babu abinda za ta tsinana maka yak'i yin komai na haihuwa sai iyayansa ne suka yi mata,sunama babansa ne ya rad'a mata Halima,(Sunan mahaifiyar Madun kenan)a haka rayuwa ta gangara Mariya na matuk'ar hak'uri da halayen Madu duk saboda darajar iyayansa wanda su take kallo a matsayin nata iyayan da Allah ya bata sama ta ka,gashi yanzu k'asa ta rufewa Inna Halima idanu wacce ta kasance tana tausayinta da taimaka mata da wasu abubuwan,a haka rayuwa take ta juyawa Madu ya sake auran Hajara, haihuwar fari ta haifo masa namiji zo kuga murna gurin Madu sai a wannan haihuwar Mariya ta san mijin nata ba k'aramin arzik'i ne da shi ba dan sosai ya saki bakin aljihu yana wa Hajara da d'anta hidima har zuwa ranar suna inda yaro yaci sunan mahaifin Madu Idris.

Tun daga haihuwar Halima,Mariya ba ta sake haihuwa ba har sai da Hajara tayi haihuwa uku a jere duk maza wanda suke ganin so da k'auna da gata gurin Madu,Halima kuwa ko kallo ba ta isheshi ba a cewarsa bazai wahalta mata ba,dan su mata sai dai ka wahalta musu a banza ba tare da kaci moriyarsu ba,inda Allah ya taimaki Halima sai ya yota mai sanyin hali,ko kad'an ba ta dosar mahaifin nasu saboda ta san halinsa,abu kad'an za tayi ya mangareta har yanzu kuwa da take da shekaru takwas a duniya.
Hajara da Mariya a lokaci guda suka haihu inda Mariya macen dai ta kuma haifa,inda Hajara ta dinga yadar mata da maganganu shi kwa Madu ba ta isheshi kallo ba daga ita har jinjirar da ta haifa,inda Allah ya taimaketa ta tanadi komai na haihuwarta saboda tana sana'arta ta kayan miya bushashe da kuma wainar gero da k'uli da safe,tunda mai taimakon nata babu ita yanzu a doron k'asa,kamar haihuwar Halima wannan ma mahaifin Madu shi ya nad'awa jaririya suna RAHEENA.

Akwai bam-bamcin halaye k'ara k'ara tsakanin Halima da Raheena,Halima mai shiru shiru ce da sanyin hali,duk inda aka nuna ba'a sonta ba ta dosar gurin,yayin da Raheena ta kasance mai kwaraf niya ga tsokanar tsiya a cikinta kamar me,inda kuma Allah ya d'ora mata k'aunar mahaifinsu Madu duk da kasancewar shi yafi tsanarta ma akan Halima,dan dukan da take sha gurinsa bai daki Halima haka ba ga kyararta da yake anman ba shi zai hana ta koma gurinsa ba,zasu had'u ita da Mubarak tsarar haihuwarta d'an wajan Hajara suyi k'iriniya anman idan Madu ya tashi ko dunguri ba zaiwa Mubarak ba anman in ya kama Raheena da duka kamar Allah ya aikoshi.
Halayen Raheena suna mugun ciwa Mariya tuwo a k'warya anman babu yadda za tayi sai addu'a ta san k'uruciya ce ko wani yaro da kalar k'uruciyarsa nan gaba idan ta san ciwon kanta ba za tayi ba,gashi yanzu ta aurar da Halima tana cikin shekarunta na sha hud'u kenan Raheena kuma shida,komai na auran Halima Baffa Idris mahaifin Malam Madu shi yayi,har yau yana nisar da d'an nasa anma ya kasa ganewa shiyasa ya d'au ido ya zuba masa ya tabbata akwai ranar da zai gane kad'an daga cikin ni'imar da Allah ya yi maka idan ya azurtaka da samun 'ya mace.

Wannan kenan

……

Da gudu ta yanko layin gidansu k'afafuwanta fututu hakama kayan jikinta,kafin fitarta sai da Innarta tayi mata wanka tas anman yanzu wani ya ganta zaiyi zaton tafi sati rabonta da wanka,tana gab da shiga soron gidansu suka ci karo da Babansu wanda ya doso kai zai fita,k'afafuwanta ya tad'e ta zube a gurin had'e da sakin k'arar dake nuni da ba k'aramin buguwa tayi ba,kuma taji zafin fad'uwar ainun,ko sauraranta baiyi ba yasa kai ya fice daga soron gidan,yayin da kuma Innarta ta yo soron gidan dan jin ihunta da ya karad'e cikin gidan gaba d'aya,da sassarfa ta isa gareta ta d'agota tana kallon yadda bakinta ya fashe,ba ta kai ga tambayarta abinda ya faru ba sai ga Ramatu ta shigo zauran rik'e da hannun k'aninta jikinsa kwata ce gaba d'aya.
‘’Lafiya?‘’
Inna ta tambayi Ramatu,bayan ta mik'ar da Rahina tsaye har lokacin tana kuka sai dai kuma ta rage sautin kukan nata.
‘’ Rahin ce ta jefashi cikin kwatar gidan Ade,shine Innarmu tace na kawoshi ki wanke masa,ita baza ta iya saka hannunta cikin kwatar ba.‘’
Ba tace komai ba bayan ta gama saurarar Ramatu sai hanun k'anin nata da ta kama bayan ta saki na Rahin tayi ciki da shi,k'ilama sakayyar yaron ce ta saka Rahin d'in fad'uwa har ta fasa bakinta,ba manaki kuma kwatar da ta jefashin ce ta sakata nufo gida da gudu har ta fad'in ta fasa baki .
Kowa yasan kwatar gidan Ade da tsinannan d'oyi,k'azamai ne na k'in k'arawa,wani zubin a rariya suke kashi su koroshi waje,shiyasa kowa yake k'ank'yamin kwatar,anman haka Inna ta wankewa yaron kwatar tas,tayi masa wanka had'e da wanke kayan tas,to ya za tayi?D'an kuka ai shi ke janyowa uwarsa jifa.

Bayan ta gama wanke kayan ne ta nufi d'aki zata d'an zauna ta huta,dan Rahin ta faki idonta ta kuma ficewa,addu'ar shiriya kawai take nemawa Rahin d'in cikin ranta,har ta tsuguna zata zauna aka rafka sallama daga soron gidan,d'an dakatawa tayi da zaman gabanta na fad'uwa kafin ta amsa sallamar.
"Ina magana da Innar Rahin"
Cewar Muhammadai mai kanti dake tsaye a soran gidan,fuskarsa a murtuke babu sassauci a cikinta karma ayi tunanin zai d'aga k'afa,dan wallahi bazai d'auki asara ba.
Jin abinda akace ya sanyata sanyo hijabi ta nufo soron jikinta a matuk'ar sanyaye da tunanin wata maganar kuma ta innarta ta kuma d'auko mata?
[9/18, 2:59 PM] Mtn Number: BEBE'ARTH

2023

Wattpad@Rashuna
Mama Jiddah
Heenah
Silar soyayya
Masoya
Rabee'ah
Babbar Cuta
Muguwar surika
K'addarar Rayuwarmu
Cikin Duniyarmu500
Katanga500
Cin Amana500
Wadjda500
Halittar ZUciya500
Compleet guda hud'unnan ga masu buk'ata zan iya baku a 1500 da kuma samun damar karanta HALITTAR ZUCIYA KTAUTA.



HALITTAR
ZUCIYA
(2)

Idonta akan Ta innarta ya fara sauka wacce ke rik'e da hannun Muhammadai,d'aya hannun nasa kuma rik'e yake da wata yarinya wacce kayan jikinta duk ya b'aci da wani abu mai yauk'i wanda baza ta tantance meye shi ba,sanyi jikinta ya kuma yi don ta tabbatar wata maga Ta innarta ta kuma d'auko mata,don a rana in ba'a kawo k'ararta sau goma ba za'a kawo sau biyar.

"Na ajiye k'waina a bakin shago,kafin na bud'e shagon na shiga da shi ciki,shine ta hankad'o wannan yarinyar kai,gaba d'aya sun fashe."
Cewar Muhammadai yana kuma d'aure fuskarsa karma tayi tunanin zai yafe.

"Innalillahi wa inna ilaihir raji'un,yanzu Mhumadai k'wan har na nawa ne?"

"Kiret biyar ne"

"Nawa kenan ya kama?" Inna ta kuma tambaya.

"8000 a ma yadda na saro"Muhammadai ya fad'a yana k'ara tamke fuska,karma tayi tunananin zai iya ragin ko ficika"

Jinjina kai Inna tayi,tana shiga tunanin yadda zata lalibo wannan kud'i,don ko jarin wainarta bai kai haka ba,bare kuma d'an kud'in kayan miyan da sai lokaci zuwa lokaci ake cinikinsa."Dan Allah Muhammadai kayi hak'uri zuwa k'arshen watan nan idan na d'au dashina zan baka."
"A'a wallahi,ni yanzu nake son kud'ina don wani zan koma na saro kinsan d'an jarin nawa ba wani taka kara ya karya yayi ba."

"Yanzu yanzu kuwa ai sai Allah,don ni ko zuwa gobe ma kace ban san inda zan samo maka kud'innan ba,idan baza ka jirayi zuwa k'arshen watan ba,bansan kuma ya zan maka ba."

"Zaki san yadda zaki mini idan naje na d'ebo miki 'yan sanda,dan wallahi yau duk masifar da za'ayi sai an biyani kid'ina."

Yakai k'arshen maganar yana hankad'a Rahin d'in gaban Inna,saurin tareta Innar tayi bacin haka da sai tayi muguwar fad'uwa.
"Hankalinki ya kwanta ko Rahina,kin fi son ki ganni cikin tashin hankali ko yaushe?."
"Innarmu wallahi ita ta fara tsokanata,ni kuma ban san ya ajiye k'wai ba da bazan turata gurin ba."
Innar ba tace komai ba sai hannunta da ta jaa suka shiga ciki,suna shiga ciki sai ga Halima tayi sallama da gudu Rahin taje ta tarota,duk da a rana takan je mata sau kusan uku,anman idan taga Haliman a cikin gidansu ba k'aramin dad'i take ji ba,ko don ba ta fiya ganinta cikin gidan nasu ba ne oho?tunda ba kasafai takan zo ba,saboda Baba ba ya barinta,da tazo yake korarta indai yana cikin gidan.
Rungume k'anwarta Halima tayi cike da so da k'auna,anman da sun zauna guri d'aya sai sun raba gari saboda k'iriniyar Rahin d'in.
"Inna ina yini?"
"Lafiya lau Mamana,ya kuke ya Abdullahin?"
"Lfy lau wallahi yana gaisheki,lafiya naganki wani iri?"
"Ina amsawa "Kafin ta numfasa ta kuma cewa.
"Ta Innarta ce ta tura wata yarinya kan k'wan Muhammadai suka fashe,yanzun nan yabar k'ofar gidannan yace sai na biyashi kud'inshi ko ya kira mini 'yan sanda."
"Innalillahi,kud'in har nawa ne?"
"8000 yace,wai akan ma yadda ya saro"
Duka ta kaiwa Rahin d'in da ke kusa da ita tana danna wayar Haliman,duk da ba ta san inda take shiga ba,wani wawan ihu ta saki saboda yadda dukan ya shigeta ba zato ba tsammani,aikwa ba shiri tayi jifa da wayar Haliman inda tayi gefe tai fisis fisis.
A fusace Haliman tayi kanta ita kuma tayi bayan Inna tana zunduma ihu.
"Yi hak'uri Mamana,kinji,sau nawa zan gaya miki ki dinga hak'uri da k'anwar nan taki,idan kowa ya kasa hak'uri da ita ke ya zamar miki dolen doliya ki hak'uri da ita,wata rana idan ba na raye ke zata rab'a taji sanyi domin ke zaki zame mata gurbina."
Cike da takaicin Innar ta hanata dukan Rahin d'in take had'a wayar tata,dama wayar ba wata wayar kirki ba,sam ba ma ta saurari me Innar ke fad'i ba saboda ranta da yayi mugub b'aci."
"Amman Inna har da d'aurin bayanki Rahin ke samu tana wani iskancin wallahi"
"Haba Mamana,yau ke kike gaya mini wannan maganar,maganar da in an jefeni da ita kin fini jin d'acinta?Nonon da kika sha shi Rahina ta sha,tarbiyar da na baki ita na bata ba kuma hakanne zai hana halayyarku bam bamta ba,ba zab'ina bane ba kuma son raina ba ne Rahina ta zamo a haka,duka zagi hantara ba shi zai sauyata ba illa addu'a ina kuma fatan Allah ya tsayar mata iya k'uruciya."
"Ba ina nufin ba ki bata tarbiya ba,ba kuma ina nufin ke kike sakata yi ba,ina ganin kamar soyayyar da kike mata ce ta saka hakan saboda tasan baza ki tab'a iya dukanta ba."
"Ke kanki shaida ce,da duka yana gyara mutum da ko dukan da Babanku kewa Rahina yasa ta gyaru,so kike Babanku ya daka yayyanta su daka 'yan waje su daka,nima na daka,babu inda zata rab'a taji sanyi kenan?Itama ba zab'inta bane Allah ne yayi ta haka,kuma ko wani yaro da kalar k'uruciyarsa duk me kallon ni na sangarta Rahina Allah ne zai mana sakayya."
"Allah ya huci zuciyarki Innarmu" Halima ta fad'a cike da dana sanin furucinta.Sallama aka rafka daga k'war gida,Inna na jin sallamar tace.
"Ina to Muhammadai ne ya dawo."
"Inna ke a gurinki nawa za'a samu? mu had'a mu bashi kud'insa,ni bana son harka da 'yan sanda"
"Ai ina jin kud'in hannuna idan na had'esu gaba d'aya baza su huce dubu hud'u ba."
"Kawo na bashi,anjima idan na koma na fasa bankina na cikasa masa sauran."
"Yaa Halima zaki bani biyar in kin fasa bankin?"
Wata shegiyar harara ta zabga mata kana ta anshi kud'in gurin Inna ta fita kai masa,anci sa'a ya karb'a,da sharad'in anjima tana komawa zai biyo bayanta ya ansa.

"Inna sati mai zuwa Abdullahi zai tafi habuja cirani."
"Ke dan Allah."
"Wallahi kuwa,nima yace idan yaje yaga yanayin garin zai turowa D'ahiru k'aninsa kud'i na bi bayansa,dan yace in ya tafi zai jima bai zo ba,zai dai dingawa su Innarsa aike,saboda matsa masan da suke sai ya k'ara aure wai tunda ni nak'i haihuwa,shiyasa ma ya tsiri tafiyar."
"Hmmmm,Allah ya kyautawa wasu mutanen wallahi,da yake ke zaki bawa kanki shiyasa kika k'i haihuwa kenan,in banda jahilci na mutane sun san Allah ke bada haihuwar nan anman da mutum ya kwana biyu bai samu ba za'a jingina masa laifi,dudu auran naku da ko shekara biyu bai rufa ba har an sanya muku idanu,banda ma haihuwar ta zama ta zamani yanzu wata tara cif zaki ji mace ta haihu,da kwa da sai a 'yebi shekaru kafin kiji ance wance ta haihu."
"Wallahi kuwa Inna,shiyasa ma bana damuwa,saboda ban isa na bawa kaina abinda Allah bai bani ba,shima kuma bai damu ba,ko nayi zancen sai dai kiji yace"To ke zaki bawa kanki,ba sai sanda Allah yaso ba"
Dai dai k'arshen maganarta Hajara tayi sallama ta shigo,taje yinin biki a can mak'otan gidansu,sai yanzun ta dawo,sallamarta kawai suka amsa suka cigaba da hirarsu dama Halima ba kulata take ba,tun wani fad'a da akai tun kafin bikin Haliman,babu yadda Inna ba tai da ita ba akan taci gaba da gaisheta anman fir tak'i,tace gaisuwa kam tsakaninsu da ita har abada,Halima akwai zuciya ban bancinta da Rahina kenan,ita Rahina yanzu zaki mata abu kuma anjima ta komo gurinki.


Bayan sallar magariba Inna na cikin zubowa Halima d'anwaken da tayi dominta sai ga sallamar Baba ya shigo cikin gidan,idansa akan Haliman ya fara sauka ya wani had'e fuska,ko gaisuwar da take mik'o masa bai amsa ba yace tazo ta shige ta koma inda ta fito,tsam ta mik'e tana saka hijabinta a ranta fad'i take."Banda arzik'in mahaifiyarta dake cikin gidan da ko fuskarta baza su k'ara gani ba,har sai sun manta ya kalar fuskar tata take.A kwano mai murfi Inna ta juye mata d'an waken ta k'ulle a leda ta bata."To Inna na gode,idan da sauran canji zan bayar a kawo miki sai ki sayi sauran abinda babu a kayan wainar."
"To na gode Mamana,Allah ya yiwa rayuwa albarka,ki gaishe da mutan gidan."
"Amin Innarmu,zasu ji in sha Allah"

"Yauwa Babansu...


Read / Download HALITTAR ZUCIYA

START READING

OR

DOWNLOAD TXT NOW
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album