Join Our WhatsApp Group

NAJWA Complete Hausa Novel Document by NAJWA


NAJWA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 114854



NAJWA

Reading Time: 9 Hours

Added On: 29, Oct 2023

Author: Maryam S Indabawa ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITERS

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 611.48 kb

File Type: txt

Views: 665+

Download: 526+

Last download: 16 hours ago

Description/Story: ο»Ώο»Ώο»Ώο»ΏNAJWA*


BY *MARYAM S INDABAWA*
*MANS*


🌐HAJOWπŸ“πŸŒ

πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘§πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘§πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘§ HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITERS✍🏾✍🏾✍🏾



*1-5*

Bismillahir Rahmanir Rahim
Alhamdulilah Allah kulli Halim.

Da sunan Allah mai rahama da jin kai duk kan yabo ya tabbata ga Allah da kuma annabin sa Muhammad (SAW).

Ina godiya da Allah da ya baninikon kammala *MIJIN UMMUNAH* Ya bani damar fara wani sabon littafi *NAJWAH*

To Alhamdulillah ina godiya ga rabbil samati wal ardi. Kuma ina rokan Allah ya bani ikon farawa lafiya tare da kammalawa lafiya
*Ameen*

Ya Allah ka jagorance ni wajen mika sakon da nake son mikawa. Allah ka shigen gaba.

Allah ka sa mu gama lafiya.
*Ameen!*

Yau gani na shigo da wani sabon littafi me suna *Najwa*

*ASMA'U HUSNAH* nayi niyar farawa to Allah yayi *Najwa* ne zai fara zuwa ina fatan zaku biyo ni cikin dan jin me ya kunsa

*Najwa* labari ne wanda na kirkire shi bakoyi rayuwar kowa ba.

Ni na zauna na tsara ban juua labarin wani ko wata ba. Hasali.ma sai zama da nayi na tsara.

In wani yaga nayi irin rayuwar sa to banyi dan shiba.

Ni na kageshi kuma ina fatan ya fadakar sannan ya nishadantar.
Allah yasa Ameen.

*Nagode*



.

Dedicated to u Sis *Rashida A Kardam.*
*Aunty Rash*

Allah ya daukakai ya sa kifi haka yasa ki gama da duniya lafiya. *Aunty Rash!*

Allah bar mu tare ya kara mana dankon soyayya da zumunci Sis *Rash*





Addu'ar ta gareki baza ta taba karewa ba. *Mahaifiya ta abar alfahari na a ko ina*

Allah sanyaya miki zuciyar ki yasa miki farin ciki ya saki a gidan aljanna.
*Mommy nah.*

Ur love make me feel like crazy.
So much love u dear tah.

Tnx for all ur supporting *Mamah!*

Kanwqta bazan manta dake ba. Kina sona kina taimakona. Kina ddamin gwarin gwiwa Nagode sosai.

*---*--*--*--*--*--*
Babban falo ne wanda ya hadu iya haduwa, Manyan kujeru ne a dakin bakake da ruwan zaiba.

Haka nan komai na adon dakin ruwan zaiba akai masa ado dashi.

Zaune take akan kujera, sai danta dake Kwance akan cinyar ta sai shaggwaba yake zuba mata.

Baki ne amman bakin nasa me mkyau ne, wanda ya dace da tsarin halitar sa ta ba fulatani.

Dogo ne sannan yana da faffadan kirji, Yana da manya idanu da dogon hanci bakin sa karami dashi, sai girar sa dake cike kansa ma gashi ne kwance irin na yan indian.

"Mami ni dai gaskiya muje kano wannan satin kinsan fa muna da bikin abokina."

Ya fada cikin shagwaba. Mami ta ce,
"Naki, bazani ba ince wancan satin ki kayi muje."

"Kiyi hakuri. Dan Allah!"
Najib ya fada yana daga kan kafar ta,

Mami ta ce,
"Aah in Dadyn ka ya yadda."

"Nasan zai yadda ma tinda sauran sati biyu ya dawo."

"Kai ni na fasa ma."
Mami ta faa tana kallon fuskar sa.
Fuska ya bata.

Ya ce,
"Mami na please kinji,"

Murmushi Mami tayi, ta ce,
"To shikenan zan fadawa Dadyn naka sai yadda mukayi."

Dariya yayi dan yasan Ddy ma kamar ya bari ne.
"Zan ma same shi tukunna."

Murmushi tayi Kawai.
"Wai kai sai yaushe zaka fito da matar auren taka."

Murmushi Najib yayi, ya ce,
"Mami ai kema kin sani. Addu'ar ki nake jira Allah ya bani irin wacce nake so."

Itama Mami murmushi tayi, ta ce,
" *Najib* kenan! Addu'a kullum munayin ta sai dai lokaci da muke jira."

Dariya Naijb yayi, ya ce
"Yauwah Mami na. Mami ina da son samun mace ta gari wacce zata kula da tarbiyar yara na."

"Allah baka *Najib* "
"Ameen!"

"Son kayi hankali da har kake hangen yarinya me tarbiya dan samun tarbiyyar yaran ka."

"Wallahi Mami, kyau bai dibata nidai nasamu yarinyar yar mutunci me hankali da nutsuwa, mai ilimi kuma me amfani da shi"

"Masha Allah! Nima zan samu zuri'a ta gari kenan. Allah ya baka mace ta gari."

Juyar da kansa yayi, yana kallon ta, sannan ya ce,
"Ameen! Mami nah. Bari naje nayi wanka zan fita."

"To *Najib* "

Fita yayi ya nufi bangaren sa. Waje ne guda wanda yake kamar gida. Daki ne guda daya na bacci sai falo da ban daki a falo da cikin daki.

Dakin a gyare yake sai kamshi dake tashi. Komai na dakin fari ne tas dashi. Kamar a lokacin aka zuba su.

Ban dakin sa ya shiga yayo wanka ya dauro alwala.

Yana fitowa ya goge jikin sa ya zauna ya shafe jikin sa da mai me kamshi ya feshe jikin sa da turaruka.

Farin jeans ya dauko da farar T-shirt sai takalmi boot da ya saka shima fari. Glass ya dauko, fari tas dashi ya saka.

Turare ya kara fesawa sannan ya fito falo. Gefen Mamin sa ya zauna.

Mami ta kalle shi, sannan ta ce,
"Masha Allah gaskiya yaron ya hadu, kyaun sa ya kara bayyana.

Murmushi yayi, yace,
"Mami nayi kyau kenan."
"Masha Allah! Kayi kyau yaro na."

"Nagode bari naje."

"Ince gun suruka ta zakaje,"
Mami ta tambaya da tsokana.

Murmushi yayi, ya ce,
"Mami ban da ita ai. da nayi Budurwa ke zan fara fadawa"

"Allah ya sa."
"Insha Allahi!"

Ya fada yana mikewa. Kumatun sa ya mika mata.

Sumbatar sa tayi. Murmushi yayi.
"Nagode Mami na sai na dawo.

Harabar gidan ya nufa, katon waje ne wanda zaici akalla motoci guda goma.

Wajen wata mota ya nufa, baka wulik da ita, sai sheki take yi.

Drivern gidan ne, ya nufoshi da sauri
"Barka da zuwa Alhaji. Dan Alhaji."

Murmushi yayi, ya ce,
"Ya akayi dan juma."

"Ranka ya dade ina zuwa kuma."
"Gari zan dan zaga."

"Nazo na kai Kane."
"A'ah aboki na. Nagode sai na dawo."

"Toh dan gidan Alhaji. Allah kiyaye hanya Allah ya dawo dakai lafiya."
"Ameen! Ga wannan."

Ya zaro kudi a aljihu ya mika masa.
"Nagode Alhaji nah."

"Ba komai."
Ya bude masa kofa, ya shige.

Baba me gadi na hango sai ya bude masa gate
"Sannun ka dan Alhaji. Allah kiyaye hanya."

"Ameen Baba ya aikin."
"Lafiya Alhamdulillah."

"Kai ma ga wannan kaci goro."
"Nagode Alhaji Allah kara budi da daukaka."

"Ameen!"
Ya fice.





*INDABAWA*

ο»Ώο»Ώ*NAJWA*



BY *MARYAM S INDABAWA*
*MANS*





🌐HAJOWπŸ“πŸŒ

πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘§πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘§πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘§ HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITERS✍🏾✍🏾✍🏾


PAGE *11-15*






DEDICATED TO *RASHIDA A KARDAM*
*AUNTY RASH*

SO MUCH LOVE U









"Honey!"
Dady ya fada daga dayan bangaren.

Ido Najib ya zaro ya sheke da dariya.

Hararar sa Mami tayi. Ta amsa da
"Na'am sweety nah'

Ido ya kara warewa yana dannen baki dan kar dariyar sa ta fito.

Kai Mami ta dauke. Ta maida hankalin ta kan wayar.
"Baby na kina lafiya ya gidan wallahi sai kewar ki nake."

Wani murmushi ta saki me kayatar wa.Β  Ta ce,
"Nima haka ya aikin?"

"Aiki Alhamdulilah! amman ba kamar yadda zaiyi sauki ba in kina gefe na."

Mami ta rausayar da kai. ta ce,
"Ayyah kayi hakuri ai yanzu ma kana dauka ina gefen naka."

"Zan na gwadawa."
ya fada daga dayan bangaren.

Sannan ya ce,
"Me kike yi yanzu."

Mami cikin sanyin murya, ta ce,
"Bacci zan kwanta."

Murmushi yayi me sauti sannan, ya ce,
"Kin min kwalliyar da kika saba min."

Ido Najib ya kara ware wa ya mike zai fice. Janyo shi tayi.

Sannan ta ce,
"Wallahi ba inda zaka, sai da nace a'ah ba kaki."

Dady ya ce,
"Ke da waye ne?"

"Kai ma ka sani ai."
Dady yayi dariya dan yadan Najib da tsokana.

"Me yayi miki."
Ya tambaya daga dayan bangaren.

"Ka kira ya nace sai nasa a speaker. Shine yake ta wani ware min ido da yin dariya yanzu kuma ya mike zai fice."

Dady ya kira shi.
"Son!"

Najib ya sunkutar da kai, ya amsa da,
"Na'am Dady!"

"To ai sai ka zauna ka koyi soyayya tinda abinda kake son gani kenan."

Najib ya rufe fuska da hannun sa, ya ce,
"Nifa Dady ba haka nake nufi ba. Kawai hira nake son muyi gaba dayan mu."

"Kai ka sani dai. Ka bari in kayi budurwa da kai na zan na koya maka yadda zaka sace zuciyar ta. Kamar yadda na dauke ta Mamin ka."

Dariya sukayi gaba daya daga nan kuma yake tambayar sa ya aiki.
sai hira ta barke kamar duk suna tare.

Sun jima suna hira sannan sukai sallama. Alwala Mami ta mike tayi ta canza kaya ta kwanta.

Najib ne ya gyara mata rufa sannan. Ya duka gefen ta. Ya ce,
"Mami sai da safe."

"Allah tashe mu lafiya."
Ta sumbace sa a kumatu.

Ya mike ya kashe mata kwai sannan ya fita.

Dakin sa ya nufa yayi wanka yayi alwala sannan ya haye gadon sa.

Addu'ar bacci yayi ya tofe jikin sa sannan ya lumshe idanun sa.

Karfe biyar nayi ya mike. Bandaki ya shiga ya watsa ruwa sannan ya dauro alwala.

Karatun kur'ani yayi na minti ashirin sannan ya wuce massalaci. Raka'atanil fijir yayi sannan suka tada sallah asuba.

Sai karfe shida ya fito daga masallaci sannan yayo gida.

Yana dawo wa dakin Mami ya shiga. Tana zaune akan sallaya tana jan carbi.

Durkuswa yayi. Ya ce,
"Mami ina kwana."

Mami ta kalle shi cikin kulawa ta amsa,
"Lafiya lou Najib. Ka dawo!"

"Eh Mami."
Ya fada yana shirin Zama.

Kallon sa Mami tayi,
"To tashi kaje ka shirya, kar ka makara bari na shiga kitchen nima."
Ta fada tana Mikewa.

Shima mikewa Yayi, ya ce,
"muje tare."

"Kar ka makara fa."
"Bazan makaraba."

Kitchen suka shiga. Dankalin da ta bayar aka feraye mata shi ta wanke ta bade shi da gishiri ta fara soyawa.

Ruwan tea ya daura wanda ya zuba masa kayan kamshi.

Sai kwai da ya dauko ya fasa. Mami kuma ta miko masa albasar da ta yanka.

Magi ya zuba akai ya soya musu. Tean da ya dafa ya juye afulas. Wani ya dauko ya dibi nashi.

Lokacin Mami ta gama suyar dankali. A fulas ya zuba mata sannan ya juye sauran a wani fulas ya dauko basket ya zuba a ciki.

Tare suka wanke kayan da suka gama amfani dasu. Sannan suka fita dakin Mami yayi wanka ya fito ya shafa mai ya bude doruwar ya dauko wata suit ash colour yasaka ta.

Kansa ya taje, ya shafa masa mai sai kyalli take. Sai bakin takalmi da yasaka.

Mami na zaune tana kallon sa. Sai da ya gama sannan ta dauko turaren ta fesa masa. Sanna ta gyara masa kwalar rigar sa.

Murmushi ya sakar mata. Ya duka ta sumbaci goshin sa.

Sannan ya ce,
"Mami na tafi "

Mami ta ce,
"Muje na rakaka."

Suka fice a daining ya dauki basket din sa da briefcase din sa ya fita.

Yana Fita dan juma ya mike. Yana washe baki.
"Barka da fitowa dan Alhaji."

"Yauwah!"
Ya mika masa hannu sukai musabaha.

Durkusawa yayi yana gaishe da Mami.

Ta amsa masa cikin sakin fuska. Mukullin motar ya amsa, ya tafi ya bude masa.

A sit din gaba ya zuwa abubuwan hannun Sa sannan ya juyo.

Najib ya dubi Mami, ya ce,
"Mami na, sai na dawo."

"Allah kiyaye hanya. Allah bada sa'a!"
"Ameen! Mami nah"

Ya shige motar.

Sai da ta daina hango sa sannan tayi wani part dake gefen can.

Tana shiga wata dattijuwa ta karaso wajen ta.

Murmushi ta sakar mata.







*INDABAWA*

*TNX U ALL*

NAJWA*



BY *MARYAM S INDABAWA*
*MANS*



🌐HAJOWπŸ“πŸŒ

πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘§πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘§πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘§ HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITERS✍🏾✍🏾✍🏾




PAGE *16-20*



DEDICATED TO *RASHIDA A KARDAM*
*AUNTY RASH*

GODIYA MAI TARIN YAWA GARE KI. ALLAH YASA KI GAMA LAFIYA AMEEN.



MASOYA NAGA SAKON KU NAGODE ALLAH BAR KAUNA DA ZUMUNCI.

*AMEEN*







Tana shiga. Wata dattijuwa tayo gun ta.

Murmushi ta sakar mata. "Barka da fito wa Hajiya."
matar ta fada.

Murmushi MamiΒ  tayi, ta durkusa tana gaishe ta.
"Baba ina kwana."

Tsohuwar matar ta ce,
"Lafiya lou. Dafatan kun tashi lafiya. Ya najibullahi."

"Ai daga rakiya nake. Ya dan makara shi yasa be shigo ba."
"Allah sarki bawan Allah kenan. Allah bada sa'a toh!"

"Ameen Baba. Me kuka yi na karyawa ne."
"Kunu da kosai."

"Baba ke dai bakya gajiya da kunu nan."
"Yo ai dashi muka saba Ki bazan tacin wannan dankalin ba. Ya sani basir. Su dai in suna so suna yi."

Mami tayi murmushi ta ce,
"To shikenan. Ina talle da Bara'atu."

"Suna can wai indimo zasu dafa."
"Baba kenan ke bakya ci."

"Ina ni ina abincin yara."
"To bari na shiga daga ciki. Daman gobe zamu tafi kano nida Najib. Shine nace bari na fada miki."

"To Allah ya kaimu goben."
"Ameen. sai anjima."

"To sai anjima."
Mami ta mike tayi ciki.

Wanka tayi sannan ta gyare gidan ta zauna cin abinci.

Karfe sha biyu nayi, sai ga kiran Dady nan. Sun jima suna hira sannan sukai sallama.

Kiran Najib ne ya kara shigowa.

"Son Ya akayi ne?"
"Na kira naji lafiyar ki."

"ina lafiya. Shine kabar aiki ka kira ni ko."
"A'ah Mami na gama aiki sai karfe biyu zamu shiga aiki kuma."

"Ok Allah bada nasara."
"Ameen""

"Kaci abinci dai ko?"
"Yanzu zan ci."

Mami ta bata fuska ta ce,
"Yanzu Son!"

Najib ya marairace. Kamar tana ganin sa. ya ce,
"Eh! Aiki ne ya hanani ci."

Mami ta dan saki fuskar ta, ta ce,
"Oh toh maza kaci kaji."
"To mami sai na dawo."

"A dawo lafiya!"
ta kashe wayar.

Kafin dai ya dawo sai da ya kira Mami sau uku. Bai shigo gida ba sai bayan sallah isha'i.

Dakin Mami ya shige da sallama. Amsa masa tayi tana daga kan sallaya.

Fuskar sa a shagwabe, ya c,
"Mami nagaji."

Harara sa tayi.

Murmushi yayi. ya ce,
"Mami sannu ya gida?"

"Lafiya! Ya aikin?"

Najib ya marairai ce fuska. ya ce,
"Aiki da wahala kiga fa Mami wai sai yanzu na shigo gida yau mutum uku mukayi wa aiki wallahi."

Murmushi Mami tayi, dan tana son yaron ta yana kwazo ba lalaci ba. Duk da tasan beda lalaci.

Tasan ya aikatu amman tana nuna masa kamar ve ba dan kar ya sangar ce da rashin son aikin.

"To Sannu kaji. Allah sa anyi a sa'a. Tashi ga ruwan zafi can, kaje ka gasa jikin ka."
"Toh!"

Ya fada yan cire kayan sa.

Bandakin ya shiga ya gasa jikin sa sannan ya fito. Mami bata dakin.

Mai ya sha a jikin sa ya saka kayan bacci riga da wando.

Kan gadon ta ya hau ya kwana. Bude dakin tayi ta shigo da katon faranti a hannu.

Mikewa yayi da sauri ya karbo mata. Ya ce,
"Sannu Mami. Yau ke kadai kikai girki."

"Yauwah. kuma kaga abincin ka nayi maka ba."

Ido ya bude, yana murmushi, "Wayoo dan Allah fa. Wanne daga ciki."

"Wanda kafi so."
"Wow Mami Allah saka miki da gidan aljanna."

Ya fada yana bude fulas din gaban sa.

Waina shinkafa masa ita ta bayyana. Murmushi yayi. Ya sumbaci mamin sa a kumatu.

Miyar ya bude, wani.kamshi ya daki hancin sa. Ido ya lumshe yana hadiyar yawo.

Miyar agushi tayi wacce ta zuba mata naman kasuwa sai kamshi ke tashi tayi kyau da ita.

Sai lemon karas da tayi wanda ta saka tufa da lemon tsami da madara ya dau sanyi.

Zuba musu yayi suka fara ci. Sai santi yake mata. Har Mami ta koshi shikuwa zurawa yake.

Ragowar ya saka a firij yace da safe zai ci. Mami sai dariya take masa.

"Son Allah ya baka wacce ta iya girki dai dan bakin nan naka ko!"
"Ameen! Mami na."

Dady ne ya kira. Kallon sa Mami tayi, ta ce,
"Nasa a speaker."

Najib ya bude ido, ya girgiza kai ya ce,
"A'ah ku gama gaisawar ku tukkuna."

Dariya tayi ta dauki wayar.

Sai da sukayi kus kus din su sannan ta bude a speaker suka fara hira gaba daya.

Sai da suka gama sannan sukayi sallama. brush Mami tayo ta canja kaya ta kwanta.

Sallama Najib yayi mata. Sannan ya tafi dakin sa.

Yana zuwa ragowar abubuwan da yake bukata ya diba ya hade su gaba daya.



Kamar ko yaushe biyar saura ya tashi yayi wanka ya zauna karatu sannan ya shiga dakin Mami ya ganta zaune akan sallaya tana ta zikiri.




*INDABAWA*

NAJWA*



BY *MARYAM S INDABAWA*
*MANS*


🌐HAJOWπŸ“πŸŒ

πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘§πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘§πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘§ HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITERS✍🏾✍🏾✍🏾


PAGE *21-25*




DEDICATED TO *RASHIDA A KARDAM*
*AUNTU RASH*

ALLAH YASA KI GAMA DA IYAYEN KI LAFIYA.
ALLAH KAWO MIJI NA GARI. MUSHA BIKI.
*AMEEN*




Masallaci ya tafi inda bai dawo ba sai karfe shida. Yana dawowa ya wuce kitchen.

Bread ya hada dasu kifin kwankwani da tumatur albasa da kwai yai beakingΒ  nashi sannan ya daura musu tea.

Ya gyara kitchen din ya dauki kayan yayi Dakin Mami dasu.

Fitowar ta a wanka kenan.
Kallon sa ta tsaya yi.

Durkusawa yayi yana gaishe ta. Amsawa tayi cikin kulawa.

"Me kayi ne?"
"Abin kari."

Ido Mami ta bude, ta ce,
"Oh sai kace mace!"

"Ai gara na iya dan ina taya matata."
"Ni...


Read / Download NAJWA

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album