Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

TA GYARU Complete Hausa Novel Document by TA GYARU


TA GYARU

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 47156



TA GYARU

Reading Time: 3 Hours

Added On: 13, Aug 2024

Author: Asma Baffa ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : +234 8061929616, 08033933642, 09032409668, +227 90795939

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 242.82 kb

File Type: txt

Views: 709+

Download: 846+

Last download: less than 1 second ago

Description/Story: 
COPY BY ZAINAB BUTALAWA

Official


By
AsmaBaffa




TA GYARU COMPLT NAIRA DARI UKU NE 300. GA MASU JIRANSA.

RASHIN SA'A COMPLT SHIMA DARI UKU 300 GA ME BUKATAR WANNAN NOVELS:

MASU SON TURA NUMBER KATIN WAYA MTN GA NUMBER DA ZAKU YI MIN MAGANA
08033933642.

MASU BUKATAR YIN TRANSFER KATIN WAYA KO VTU GA NUMBER DA ZAKU YI
09032409668.

MASU BUKATAR BIYA TA BANK GA ACCNT NUMBER DA ZAKU TURA KUDIN
2177560408, YAHAYA GARBA MUHAMMAD, ZENITH BANK.
YAN NIGER GA NUMBER DA ZAKU NEMA IDAN KUNA BUKATAR SIYE.
+227 90795939

INA MIKO GAISUWA GAREKU FANS DINA BAKI DAYA INA KUMA JINJINA.😂🥰🥰
[4/16, 9:20 PM] Sis Asma: 📙TA GYARU📙











1






FREE PAGE






Official










By
AsmaBaffa






NA KUDI NE

Kamar yanda kuka sani Allah yasa an Gama RASHIN SA'A lfy, ga masu bukatar Complete Rashin Sa'a Naira Dari Uku ne 300 ku min Magana ta pc ta wannan Number
0803 393 3642. Tnx.


NA KUDINE

TA GYARU na kudi ne Naira Dari biyu 200 ne ga masu bukata.

Ga masu son tura Number na katin MTN ta WhatsApp to ga Number
0803 393 3642.

Masu son siye ta Hanyar Transfer ko Vtu ga Number din da zaku iya turawa 09032409668

Masu son siye ta Hanyar Turawa ta bank ga Accnt Number 2177560408, Yahaya Garba Muhammad, Zenith bank.








BISMILLAH





Alhmdllh Muna godiya ga Allah da ya bamu Rai da Lafiya har ya sake bani ikon Rubuta sabon Novel Ta Gyaru.
Kamar yanda na Fara lafiya Dani daku Baki daya Fans Allah bamu ikon gamawa Lafiya.

Ina matukar Godiya da jinjina ga Fans Dina Wanda Allah ya Basu ikon siyen Novel Dina da Kuma Wanda ma Basu samu damar siye ba Ina godiya Ina kaunarku Baki daya.

Jinjina ga masu Sharhi har kullum kune a gaba mutanena,da Sa hannunku typing ke tafiya dai dai tnx alot.






Page kacokan na DIYAR KATIBI ne da FULATAH LUV.










Hamshakiyar Barauniya ce ni Raudat, Asalina Sunana
Raudat M. Usman
Babana Muhammad Usman Yan Asalin Adamawa ne,Fulanine usul, gaba daya danginmu Suna Yola cikin kauyen Fulani,Babana Malam Muhammadu shi kadai Iyayensa Suka Haifa,tun Yana Karami Allah ya karbi rayuwar Babansa Wanda yake da gida a Kaduna wannan gidan shi kadai ya Mallaka sai gonaki da sauran dababbobi na kauye, Malam Muhammadu ganin bashi da Wasu Yan Uwa na jini sosai ya tattara gadonsa kaf ya siyar sai gida daya ya Bari na Kaduna Wanda shine muke zaune a ciki har yanzu.
Da kudin gadonsa yayi aure ya Auri Salamatu Mahaifiyarmu kenan,Salamatu Yar larabawan Yemen ce Amma iyayenta Suka zauna a Niger Wanda Allah yayota Kamar Balarabiya har ma tafi wasu Larabawan kyau gashi da diriin sura,Danginta kaf suna Niger wasu Kuma suna Yemen.
Bayan ya Auri Salamatu Marainiya Bata da uwa Bata da Uba,sai dangi Marasa zuciya,Salamatu Mahaifiyarmu wacce muke cewa Mami ya daukota zuwa gidansa Daya rage na gado dake Rigasa Kaduna,gidane Karami tun irin na da Wanda ko a da gidaje namu gidane na talaka futuk, Mahaifiyarsa wacce take Kakarmu ta wajen Uba tal data rage Binta Muna ce Mata Inno, Abbanmu Malam Muhammadu ya dauko Uwarsa ta dawo Kaduna gidansa da Zama ya Bata daki Daya,Suna zaune Lafiya da Mami.
Malam Muhammadu karatun Muhammadiya yayi kawai,itama Mami Salamatu Na Muhammadiya tayi Amma tayi Primary ta boko.
Muhammadu Messenger ne a Office din Wani ma'aikaci a Ministry of Justice dake Garin Kaduna, yana daukan Albashi duk wata fiye da dubu ashirin.

Abinda yasa Muhammadu ya dakko Inno Babarsa Gidansa shine Zuciyar Muhammadu Matacciyace matuka,Yana samu dai dai gwargwado Amma baya godewa Allah, burinsa Roko da Maula gaba Daya ya zubarwa da yaransa Mutunci a Unguwa kaf,har samarin yayansa rokonsu yakeyi,Haka duk Wanda ke mutuntashi to sai ya je Maula gidansa,Salamatu Shuru Shuru ce Bata da zafi ko kadan shi yasa kowa abinda yaga dama yakeyi har yaranta,sai dai tace Bari ko ba kyau shike Nan.

Inno Kakarmu kuwa Itama sabo da son danta da jikokinta Bata iya musu fada ko kadan,sannan ita take Kara Goyawa danta Muhammadu Baya yake ci gaba da maula da roko gida gida.
Ita kanta Inno ta tsufa Amma Danta bashi da Imani ko kadan,baya tausaya Mata,maimakon ya dau nauyinta ya hutar da ita sai itace ke daukan Nauyinsa.

Gidajen Masu kudi Inno take zuwa duk tsufanta take musu aikin wahala iri iri Ana biyanta,Ana Bata ragowar Abinci da sauran jagwalgwalo, Yan kwancen sutura ta kawowa Muhammadu da yaransa,komai ta samu shi Danta ko jikokinta,Itace ta kaita da yawon Maula itama tana daukan Raudat da tafi kowa kyau a gidan sai ta daukeni muyi ta zaga unguwa unguwa gidajen manyan Yan Siyasa,.
Tun ban Saba ba Har na Saba na koma kasurgumar Barauniya,yayin da idan nayi wata satar sai mutum yace Aljanune sabo da tsabar kwarewa ta,Babanmu ba ruwansa da Ina na samo zai karbe,Mami kuwa sai dai ta kalleni ta girgiza Kai tace Ki Bari ba kyau shike Nan fadan.

Yayyena Mata da kanwata Mace gaba dayanmu Allah ya zuba Mana Iyayin tsiya ka rantse yaran shugaban kasa ne,nice Raudat kadai sabo da salon sata da Maula na nemi yanga ta da iyayi na rasa, Halin Mahaifinmu yasa gaba Daya samari Suka gujemu,aka tsanemu, bamu Dame son mu bare ya aura.

Malam Muhammadu Da Salamatu yaransu Biyar gaba Daya mata Kuma duk manya ne mu ba Yara,Sabo da matacciyar zuciyar Abba yace Dole sai Mami tayi tsarin iyali ta daina Haihuwa Dole sabo da ya gaji da Haihuwa nauyi zaiyi Masa yawa musamman gamu mata.
Aymana 25yrs itace ta farko, ta gama secondary da kyar Inno ce ta biya mata kudin schl har ta Gama Abba cewa yayi bazai iya ba,Aymana tayi sana'a kala kala Amma Abba ya cinye kudin hakan yasa ta daina gaba Daya Babu jari ta zauna a gida ba makaranta ba aure sai kayan iyayi da yanga sabo da gaskiya Allah ya zuba Mana kyau gaba dayanmu musamman Ni Raudat uwar kuri.

Daga Ayamana Sai Fadeela 23yrs itama Inno ce ta tsaya Mata tayi iya Secondary da Islamiyya tana Nan itama a gida a zube sai dai mukan Dan leka Islamiyya jefi jefi, itama tayi sana'a daban daban Abba ya Lashe kudin.
Sai Khairat 20yrs itama an Gama schl iri Daya dai da yayyenta Sai dai ita akwai cin kudin samari tana yaudararsu idan ta samu, sai Ni Raudat 18yrs Nima kwana Nan na Gama secondary schl da kyar Inno ta biya sai da aka tsallake min Shekara Guda ma sannan tayi min komai har na zana exam na Gama,sai dai Ni Halina Ya banbanta, Sata tasa bana yanga bana komai sai gantalin tsiya, Amma Abba duk yafi Sona sabo da Samo kudi da abinci harda sutura,duk gidanmu kowa yasan sata nakeyi don a gidanma in dai Zan ga Dan sabulu wuf Zan dauke Amma bana satar kudi a gida,Amma Abinci,sabulu,man shafawa etc Zan daukesu kuwa.

Daga Ni sai Autar mu ta biyar Rufaida 15yrs tana Ss1 itace kanwarmu last itama ta girma sai Jarabar cin tsiya sabo da Haka Abba yafi tsanarta Sabo da Wai tana cinye Masa abincin gida.
Dukkanmu Allah ya zuba Mana basira da kokari a aji Kamar Ana Bude Kwakwalwarmu Ana zuba Mana.
Mun Dade Muna tunanin me Abbanmu yakeyi da kudi baya iya tsinana Mana komai sai daga baya Muka gano Ashe gidan rawa da kallon Hawan Bori a kauyuka,sai Gidan kallon Dambe acan yake Karar da kudinsa acan yake zuwa ya dinga Lika musu kudi,idan ya Tara kudin sai ya tafi can ya kadarsu a banza.

A Haka Muna mutuntashi Muna bashi mutuncinsa na Uba,nice kadai ma nake Fitowa na fada Masa gaskiya ba ruwana sabo da ba wata kunya gareni ba.
Kadan kenan Daga cikin Tarihinmu gaba zaku ci gaba da ji.
Ni Raudat Fara ce Kamar yanda duk Yan gidanmu suke har Abbanmu da Inno zuwa Mami kaf dinmu.

Amma Ni ta daban ce Allah ne yayi Ni Haka,duk yanda kuka san me kyau wacce ta Dace a buga a labarai to na kai, kyan diri da
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download TA GYARU

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album