Join Our WhatsApp Group

ABNUR Complete Hausa Novel Document by ABNUR


ABNUR

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 48788



ABNUR

Reading Time: 4 Hours

Added On: 12, Mar 2024

Author: Maimoon ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Elegant writer association

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 259.68 kb

File Type: txt

Views: 247+

Download: 308+

Last download: 2 days ago

Description/Story: *💖ABNUR💖*

By maimoon🤓

Elegent Online writers

*Free book* page 1



Bismillahi ar-rahmani ar-raheem_______

Hasken farin watan daya haske illarin garin shiyake bata daman ganin inda take sanya ƙafafuwanta gabaɗaya she is not in her right senses tafiya kawai takeyi ba tare da tasan inda ta nufaba

Tafin hannunta ta sanya ta share hawayen da ya zubo mata a karo na ba adadi she really wish all dis was a dream cigaba da tafiyan kawai takeyi a ƙauyen da ko sunansa ma bata saniba Ita dai kawai burinta tayi nesa da inda ta fito

A daidai kofar wani gida ta ja ta tsaya saboda batajin xata iya cigaba da tafiyan saboda galabaitan da take sake yi rabonta da abinci tun breakfast shima ba wani sosai taci ba gashi a yanda xata ƙiyasta saboda yanayin shirun garin da kuma duhun dare aƙalla ƙarfe 11:00 zai iyayi

Guri ta samu ta zauna a ɗan dakalin dayake ƙofar gidan tare da kifa kanta tana cigaba da kukan da har takejin zuciyarta kamar ba'a jikinta yakeba batasan iya lokacin data share a zaune a wajen ba kawai dai taji idanunta na lumshewa alamar bacci takeji

Muƙewa tayi a hankali akan dakalin tana jin zuciyarta na mata zafi batason tuno abinda ya rabo ta da gida a cikin wannan tunanin bacci ɓarawo yy nasaran fizgarta duk da ba ɗaɗin baccin takejiba sam

Sanyin asuba tare da kiraye kirayen sallah a masallatan da suke ƙauyen yasata ɓuɗe idanunta a hankali waɗanɗa suka kumbura Sukayi jajir saboda tsananin kukan ta sha zaunawa tayi akan dakalin tana jin duk jikinta na mata wani irin ciwo ta shiga ƙare ma ƙauyen kallo tanason tuno inda take dafe kanta da ke tsananin ciwo tayi tana jingina da bango wasu hawaye Masu ɗumi suka sake gangaro mata

Hannunta tasa da sauri da kare fuskarta saboda hasken fitilar daya haske mata fuska
"Subhanallahi mutum ko aljan" mutumin ya tambaya da alamar tsoro a tare dashi yana tsaye daga ƙofar gidan da take zaune kasa cewa komai tayi sai hawayenta da ya ƙara ƙarfin gudu juyawa mutumin yy da sauri ya koma cikin gidan sai gashi ya ƙara fitowa tare da wani ɗan saurayi da alama shima alwala yayi na tafiya Masallacin

"Kaganta nan wlhy nidai har na tsorata" tsohon ya faɗa yana nunama saurayin ita da alama ɗansa ne ƙarasowa kusa da ita yy ya tsaya ɗan nesa kaɗan da ita yana faɗin " baiwar Allah " ɗago kanta tayi a hankali tana kallonsa hawayen idanunta na cigaba da kwarara tsura mata ido kawai yy sai kuma ya juya ya kalli babannasa yace "baba ko xata shiga ciki kafin mu dawo daga masallaci lokaci na ƙurewa "wani kallo babannasa yy masa yana nuna ta yace "ta shiga ina wai, kasan wacece ita xakace ta shiga ciki "miƙewa yy yana sake kallonta sai kuma kawai yy wucewarsa baban ma ya bisa a baya suka nufi masallaci

Har aka idar da Sallah gari ya soma haske tukun suka nufo gida tun daga nesa suka hangota still tananan zaune inda suka barta baba ya kalli kamal yace "anya wannan yarinyar mutum ce kuwa "murmushi kamal yy yace muƙarasa mugani "daidai kusa da ita ya durƙusa ya sake cewa "baiwar Allah" a karo na uku sannan ta ɗago kai ta kallesa murmushi yy mata yace "me ya sameki haka kike zaune anan da alama ma anan kika kwana ki faɗa min ko akwai taimakon da xan iya baki "nan ma shiru tayi ta sake miyar da kanta shiru yy kamar mai tunani sai kuma yace to ki tashi mu shiga ciki kiyi sallah nasan bakiyi ba ko kallonsa kawai takeyi kamar statue sai da ya sake maimaita abinda ya faɗa tukun ta miƙe a hankali jiri na ɗibarta saboda gaskiya tana buƙatar tayi sallolin da ake binta

Kallonta yy tayi saboda baiga alaman yar ƙauyen bace ko duba da irin suturar da ke jikinta kaɗai to itakuwa me ya kawota ƙauyennan haka har suka shiga ciki ta tsaya a zaure tana raba ido baba da tunda yaga kamal ya tsaya wajenta ya shige cikin gida ya samu a tsakar gida zauren ya nuna masa yace "wannan yarinyar baba nace ta shigo ko xatayi sallah "saída baba yy shiru sai kuma yace "kamal mutum fah yanxu abin tsorone kuma kwata kwata batayi kamar yar nan ba bawai bana son taimaka mata bane" kamal yy murmushi yana komawa zauren tare da faɗin "karka damu baba banji ajikina mai cutarwa ce kuma mu ai dan Allah mukayi da kyakkyawar nufi idan ma ta cucemu Allah baxai barta ba

A zauren ya sameta a rakuɓe yace baiwar Allah shigo yayi gaba tana binsa a baya har ƙofar ɗakin mahaifiyarsa sallama yy ta amsa sannan ya shiga itama ta bishi a zaune suka tarar da ita har lokacin akan abin sallan ta gaisheta yy ta amsa da fara'a tana kallon baƙuwar sai kuma tace " kamal wannan Fah a Ina ka samo ta" murmushi yy yana miƙewa yace" to muma dai a ƙofar gida muka ganta da alama ma anan ta kwana kuma taƙi magana shine nace mata ta shigo ko xatayi sallah" kallonta kawai umma takeyi sai kuma tace "to badamuwa bari tayi sallan idan mun karya sai muji daga ina take haka dan sam batayi kalar yan ƙauyennan ba" yauwa umma kamal ya faɗa yana ficewa daga ɗakin dan tafiya gona tare da baba dake jiransa a waje


Abuja nigeria_

A haukace yake sauƙowa daga matakalan da yake haɗesu uku uku hurhuɗu hankalinsa a matuƙar tashe ƙofa ya nufa da azama yana sake dialling din number a wayarsa ɗaya daga cikin securities ɗinsa ne ya ƙaraso da sauri yana faɗin "morning sir" wani kallo da yy masa ya sashi shiga hankalinsa ya sake faɗin "sorry sir" juyowa yy gabaki ɗaya yana kallonsa yace "ina take" a tsorace guard ɗin yace "sorry sir we have tried our level best but still we are not able to reach to her" cakumo wuyansa yy a zafafe Yana faɗin "what the heck do you mean baku ganta ba wata sani ,ina xata je she has no one but me so na baku nan da awa ɗaya ku nemo min *NOOR* duk inda ta shiga a garin Abuja" hankaɗasa yy baya tare da sake faɗin "sorry sir" sake kallonsa yy sannan yace "don't u dare ,keep ur fucking sorry to yourself , just make sure lokacin da na baku kundawo min da noor gidannan "sai kuma ya juya a fusace ya nufi motarsa ya fice a gidan a guje


To ABNUR has just started the story is yet to begin 🤓😇

*💖ABNUR💖*

*By maimoon*🤓

*Elegant online writers*

*Freebook*

*page* 2

Tunda ya fito gidan yake yawo a cikin gari yama rasa ta ina zai fara neman NOOR ,ina zata je ,wata sani bayan shi, ya tabbata bata da inda zata je da ya wuce gidansa ,har yamma yana gararamba.

Gefen titi ya samu yayi parking ya jingina kansa da steeryn motan, ya rasa ina zai nufa don neman ta, ɗago kanshi yayi da idanuwansa da suka gama rinewa sukayi jajir ya jingina kansa da seat ɗin motar .

Why Noor? ,am I really that bad to you da kika zaɓi ki barni? ,do you have any idea halin da nake ciki yanxu ?please Noor ki dawo gareni i promise I will mend my ways ,na miki alƙawari zan gyara please Noor.

Da ƙyar ya samu ya kai kanshi gida, har jiri yake ji dan rabonsa da abinci tunda ya fahimci Noor bata gidan .

Baibi takan kowa ba har bodyguards ɗin da suke gaishesa, ko takalmansa bai cire ba ya faɗa kan gadon katafaren ɗakinnasa yana kallon saman ɗakin, yana sake zurfi a tunanin ina zata shiga a garin Abuja .


Kamal ne ya fito daga ɗakin ,mahaifiyarsa na biye dashi ,zama tayi a tsakar gidan shima yaja ƙaramar kujera ya zauna yana fuskantar ta yace ,"umma da muka fita dama bata ce miki komai bane? ".


Ďan shiru umma tayi kamar baxatayi magana ba sai kuma tace," wlhy kamal nayi iya tambaya amma batace min komai ba, banda kuka babu abinda takeyi, yarinyar tana da babbar damuwa sosai ,amma rashin sanin daga ina ta fito shine babbar damuwar ".


Kamal yace ,"hakane amma gaskiya tana buƙatar taimako sosai ,kawai mu bari muga kwana biyu ko xata ji sauƙin abinda yake damunta, sai tayi mana bayani" .


Shiru umma tayi sai kuma tace "toh Allah dai ya kyauta gata kyakkyawa wlhy kuma daga dukkan alamu yar gidan masu kuɗi ce ,"kamal ya miƙe yana faɗin," wlhy nima haka na gani".


Fita yayi daga gidan dan yanaso ya je gidansu Abdul, dan yanaso ya amso kuɗin sa dake wajensa dan komai na gidannasu ya ƙare kuma gashi amfanin gona bai nuna ba bare ,
har ƙofar gidan yaje ya aika yaro ya kira masa shi, a ƙasan wani bishiya suka zauna Abdul ya kallesa yace "kuɗinka ko kamal" .


Kamal yayi murmushi yace "saboda bana zuwa wajen ka sai idan inason kuɗi koh ",Abdul yayi dariya yace "wlhy ba haka bane kawai dai nasan halin garin ne yadda babu kuɗi", shiru kamal yayi sai kuma yace "wlhy Abdul banso na tambayeka ba amma wlhy ina matuƙar buƙatarsu ".


Duk sukayi shiru kafin Abdul ya nisa yace" wlhy kamal bandashi nima ",shiru yayi sai kuma yace, "babu damuwa karka damu wlhy", daga haka ya miƙe yana faɗin "to sai mun haɗu anjima da daddare", Abdul ma ya miƙe yace "ba damuwa nagode kamal ".


Daga haka ya juya yana ta tunane tunane har ya iso a tsakar gidan ya samu umma tana ƙoƙarin shiga kitchen kusa da ita yaje yace," umma dama naje wajen Abdul ne ko zan samu kuɗin wajensa amma bansamu ba ",umma ta nisa tace ," to Allah ya kyauta amma dai yau yaza ayi kenan, yanzu babanka ma ya dawo bai samuba ,wlhy gashi muna da baƙuwa " .


D'an murmushi yayi yace "yanzu dai akwai wani ɗan canji a jikina idan na fita zan nemo mana abinda zamuci yau, amma dai gobe sai yadda Allah yayi da mu", duk juyawa sukayin jin motsin mutum a tsaye suka ganta tana kallonsu umma tace "ah ah Noor Kin fito ".


Girgiza mata kai tayi tace ,"umma inaso zan shiga bayi ne," da sauri umma tace "ayya gashi can bari na saka miki ruwa a buta ",da sauri ta karɓi butan hannun umma tana faɗin "laa umma karki damu dan Allah".


Ta wuce wajen randar ta ɗebi ruwan umma tace ."ga ruwan zafi idan zaki surka ,tace "toh" cup ta ɗauka ta ɗebi ruwan ta wuce bayi ,
Umma da kamal na nan zaune ta fito ta ajiye butan sannan ta nufi wajen tabarmar da taga sun shimfiɗa sun zauna.


Itama zama tayi sai kuma tace "umma dan Allah kuyi haƙuri da shiga rayuwarku da nayi, amma ina neman alfarma a wajenku dan Allah ina so in zauna da ku na wasu kwanaki, nasan ya dace na faɗamuku abinda ya raboni da gida , amma na muku alƙwari zan fada muku insha Allahu ".


Aai da ta ɗan yi shiru sai kuma ta sanya hannuta ta ciro ɗan kunnen gold ɗin dake kunnenta ta miƙama kamal tace "yaya kamal gashi ina so dan Allah ka siyarmin da wannan ɗan kunnen ".


Sai da ya kalleta ya kalli ɗan kunnen sai kuma yasa hannu ya karɓa yana kallo yace," tabb Gwal ne fa".


Tayi shiru tana kallonsa yace," sai dai bazan iya sayarwa a garinnan ba , sai dai gobe insha Allahu , tunda ranar kasuwan cikin garin kusa damu ne , su suna siya sai inje can na sayar miki ," ahankali tace "nagode sosai Allah ya saka muku da alkhairinsa ", duk suka amsa da ameen .

Washe gari kamar yadda sukayi haka ya shiga cikin gari ya sayar , duk da dai an masa an siya ba yadda kuɗin sa ya keba ganin cewa ɗan ƙauye ne, haka ya ɗaure kuɗin a mayafi ya dawo gida, a tsakar gida ya samesu suna hira da umma ya zauna shima yana warware wa ya miƙa mata.

"Yace gashi Noor ",ta karɓa tana murmushi ta ƙirga kuɗin sai kawai ta girgiza kai sannan ta kama hannun umma ta danƙa mata kuɗin.

Dubu biyar kaɗai ta ɗauka a kuɗin umma ta zare ido tana kallonta girgiza kai tayi tana kallon umma tace "umma dan Allah karkice komai kiyi haƙuri jiya naji hirarku da kamal dan Allah ku karɓi kuɗinnan ,na baku ne a matsayin yan uwana saboda kunyi min taimakon da bazan taɓa mancewa daku ba, kunyi min taimako alokacin da nake tsananin buƙatarsa".

Umma rungumeta kawai tayi tana sake jin son yarinyar har ranta, tana sake kwaɗaituwa da son jin dalilin ta na barin gida , a hankali ta share hawayen ta tace.


" Ni ban san me ya raboki da gida ba Noor, amma ke ɗin alkhairi ce a wajenmu, kuma mungode Allah ya saka miki da alkhairi kuma ya fitar da ke a cikin duk matsalolin da rayuwarki ke ciki".

Shidai Kamal kallonta kawai yakeyi sai kuma yace "Noor kuɗinnan", shhhh tace masa "yaya kamal pleaaaaase karkace komai".

Nurmushi kawai yayi yace "to shikenan nayi shiru Allah ya saka", daga haka suka ci gaba da hirarsu tana samusu baki jefi jefi, but hankalinta da tunaninta gabaɗaya suna wani wajen daban.

Wasu sabbin hawayene suka cika idanunta, she is sure baida buƙatarta a rayuwarsa, kuma bayida asara idan har bata tare dashi , he never loved her but tayima kanta alƙawari koda mai kama da ita bazai sake gani ba.

zatayi nisa dashi irin nisan da bazai taɓa cinmata ba, a hankali ta sanya hannu ta share hawayen tana ƙaƙalo murmushi, ganin umma tana kallonta sai kuma ta miƙe ta nufi ɗaki duk suka bita da kallo .

🥱🥱🥱🥱🥱🥱

#maimoon
💖 **ABNUR**💖

*By* *maimoon* 🤓

*Elegant* *online* *writers*

**Freebook**

*Page* *3*

Kwanci tashi asarar mai rai,yau kwanan Noor goma kenan a ƙauyen Marke dake jihar Kano.

duk da cewa har yau ba tayi musu cikakken bayanin abinda ya rabota da gida ba,amma sun fahimci ita ɗin mutum ce mai matuƙar daɗin zama, sannan bata da son magana sosai.

Hakan yasa suke zaune tare da ita, har zuwa sanda zata yanke shawarar sanar dasu ainihin abinda ya rabota da iyayenta ,

Umma tana matuƙar ji da ita, kuma hakan yasa basa ma ɗago maganar, saboda yadda daga an tambayeta, sai dai ta fara kuka, Sannan akoda yaushe maganar ta baya wuce"Umma kuyi haƙuri insha Allahu zan sanar daku ,har ma abinda baku tambaya ba".

A bangaren ZANNUR kam babu sauƙi, yayi iya ƙoƙarin sa ,ya haukace da neman ta har gidajen Radio,but...


Read / Download ABNUR

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album