Join Our WhatsApp Group

MIJIN KWAILA Complete Hausa Novel Document by MIJIN KWAILA


MIJIN KWAILA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 45316



MIJIN KWAILA

Reading Time: 3 Hours

Added On: 20, Oct 2023

Author: Zahra Ishaq Adam ,

Ebook Compiler : ESHAAT SMILER

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 273.06 kb

File Type: txt

Views: 1217+

Download: 554+

Last download: 16 minutes ago

Description/Story: HADA DOCUMENTS DAGA
ESHAAT SMILER HOM OF HAUSA AND ENGLISH DOCUMNTS WHASTAPP 08066360176 FOR MORE







*MIJIN 'KWAILA* ����‍♀

sabon salo daga labarin *zahra adam ishaq*


"-chapter one-"

Ahankali yake tafiya da motar sakamakon yanda ya iske saitin bakin makarantar yaran yacika yakuma batse da dandazon yaran da'aka riga aka taso daga makaranta,ya d'anja gajeren tsoki lokaci guda yana kallon tsadadden agogon dake hannunshi ya taka burki kamar yanda sauran masu ababen hawa y'an uwanshi sukaja nasu burkin sakamakon dakatar dasu da yellow piper yayi.
Ranshi 'kwarai yana a dagulene koda yake ba abin mamaki bane ganin fuskar tashi babu walwala kusan dukkan na tare dashi sunsan dahakan duk da yake mutum mayen barkwanci lokaci kankane yakoma kamar wani horror abin tsoro ga kowa saboda yanda yakecin magani kullum idanunshi suna manne da farin gilashi saboda yanda ya matsama idanun nashi da kuka wanda har yazuwa yau d'innan yakasa dena kukan,
Baya zato ko tunanin zaidena kukan rasa jigon rayuwarshi dayayi a cikin watanni shidda dasuka gabata.
Yazuwa wannan lokacin yazama abin tausayi ga kowa to ai dolene dukkan mai imani ya tausayama d'an sangirin saurayin maicike fal da 'kuruciya akan fuskarshi da dukkan sassa na jikinshi,
Rashi yayi babba rashin dayake ganin bazai ta'ba samun tamka ko madadin taba.ZAHRA ADAM ISHAQ cikakkiyar budurwar dasuka sha'ku tun yarinta shine yaci kashinta da fitsarinta ya goyata a gadon bayanshi yamata soyayya dabai ta'ba yima wani mahalu'ki a duniya irintaba rana guda ciwon mara yayi fatali da rayuwar zahara yazuwa barzahu,
Adai dai lokacin da yarage saura kwana uku rak!
Daurin aurensu,
Yashiga rud'u mara misaltuwa dayawa yawa anzata ya haukace,amma dayake allah gafurune kuma rahimu saiya tashi kafad'unshi yakuma saka mashi dangana duk da ikirarinshi na dena kallon kowacce y'a mace da gashi tunda yarasa zahra.
Y'amma dayawa sunsha kawo kansu gareshi wasu iyayensu zasu kawo talla wasu text zasumai amma haryau baiga mai maye gurbin zahra ba,
Yashafi gefen fuskarshi daya tuna aneesa wacce tanace mashi kamar chewing gum saboda so,
D'iyar 'kawar mummy ce,
Ya girgiza kai batare daya ankare ba.
Kamar ance dashi ya kalli gefen damarshi ya hangota cikin dandazon yara sa'anninta kamar sauran yara akwai uniform bulu da farin hijabi jikinta sai y'ar jakar makaranta saqale a hammatarta,
Wata mummunar fad'uwar gaba ta riskeshi lokaci guda ya cire gilashin fuskarshi yasake murza idanu gabanshi na bugun goma goma,
Dai dai lokacin data tsallako gefen dayake yara sun ragu sosai,
Tana tafe tana tsokanr yaran dake gefe da ita.
Caraf idanunta suka sar'ke cikin na ishaq wanda tuni anbasu hannu amma tsabar kallonta baimasan anbasu hannunba.
Tarin ababen hawa dasuke bayanshi suka addabeshi da horn hakan yasakashi waigawa da sauri, lokacin wani har yayi mashi overtaken yana fad'in "amma kai wawane,idan kallon mata kazoyi toka bamu hanya mu wucewa zamuyi "
Ishaq bai tankaba yagyara parking mota zuciyarshi kamar zata tsage saboda tashin hankali.
Ganin ita yaketa kallo yasata cewa da 'kawayenta"ummilolo kukalli d'an 'kauye yanata kallona kutsaya kuga yanda zanmashi gobe bazai sake kallonaba,ummana tace mai kallon mutane mayene."
Saita lalla'ba kamar zata wuceshi sai dai tana zuwa saitinshi inda ya sauke glassa d'in motar ta tofa yawu, cikin sa'a kuwa ya sauka akan fuskarshi.
Sauran students y'an uwanta suka saki baki suna kallonta duk sun kasa tafiya,
Yayinda su ummilolo suka hau tsalke suna kyalkyala dariya.
Itama dariyar take don asukwane tabar wajen da gudu,
Tana zuwa tami'kama su ummilolo hannu suka tafa, kafin tacigaba dayima ishaq gwalo tanasaka hannayenta saitin kunnuwanta almar eho...ya numshe idanu yana tunano zahranshi a irin wannan lokacin tayi makamancin hakan gareshi, lallai batada maraba da zahra, hannu yasaka ya lakace miyon,ya sumbata zahra daban take, komai nata so yakeyi.
Bai ankareba ya hango zahra can kusa dawani matashi irin masu tallar agwaluma d'innan,
Ta mararaice fuska tace dame agwaluma "kai don Allah bani d'aya?
Me agwaluma cikin mamaki ya kalleta yace"kibada kud'i sai abaki agwaluma yammata."
Sudai su ummilolo sun 'kunshe baki sunason dariya suna tsoron bala'in zahra don sunsan akwai daru.
Ta murgud'a wa mai agwaluma baki,"nace kabani d'aya kawai."
Me agwaluma ya fusata yace"tunda ubanki yabani jari meze hana inbaki d'aya."
Tazaro idanu"la la la..kazagi ubana?
Me agwaluma yayi tsaki,
Aikafin ya ankare tuni ta duma wawa uku ta sura ta fece aguje da fad'in "pdp!!!"
Sauran yara dasuke tsaye sukace "wawaaaa!!!"
Tuni sun duma hannaye suna dumbuzar agwaluma,
Ganin yara sun kwashe agwaluma yasaka me agwaluma binta aguje bayan ya jefar da tiren dayazama empty.
Shegen gudu gareta ko barewa ta shafa mata lafiya,
Sauran yara sukad'au ihu "sai zahra !!sai zahra!!!!
Gaban ishaq dake kallon duk abinda yafaru yabuga da karfi.
Ya maimaita sunan ZAHRA???


��������

Aunty y'ar charas��
[12:03, 24/11/2017] hm: *MIJIN KWAILA* ����‍♀


chapter 2.





Gudu take kamar wacce zata tashi sama,
Ahaka tasha kwanar layinsu da yawa y'an unguwar sunsan halinta don haka suna ganinta suka fara dariya,
Wasu nafad'in "mai hali baya fasa halinsa zahra."
Saida ta kutsa d'an sirdad'en lungunsu kana ta dakata da gudun tana luliya agwalumar abango dafad'in"luliya-luliya danya awakin baba da dad'i."
Sai dai batayi auneba ta hango mai agwaluma a three thirty ya kutso lungun,
Hakan yasakata idasa fad'awa gidan kamar wacce aka cilla da kibiya .
Umma dake tsaye bakin band'aki da buta a hannu, zahra batamasan ta angije ummanba,ta danna d'akinta gami da gar'kama sakata.
Umma tabita da idanu,
Yayinda anty hafsat dake tsaye gefe tabita da tambayar lafiya zah....
Bata 'karasaba sukaga me agwaluma ya fad'o gidan,
Baikobi takansuba yarufama zahra baya zuwa d'akin datake ciki.
Anty hafsa cikin mamaki ta tareshi dafad'in"lafiya malam bakada hankali zaka fad'o cikin gidan matan aure bako sallama.?"
Yayimata kallon banza ranshi yana zafi kafin yace"aiba sallama ta kawoniba,wlh sai anbiyani kud'ina kokuma in karya yarinyarcen,
Yanuna d'akin da zahra take ciki.
Yayinda take lekowa ta window tana mashi gwalo,
Yakuma 'kufula,
Anty hafsat itama hararshi takeyi tana nuna mashi kofa"get out"
Ya kalleta da jan idanunshi"bansan wannan yaren ba."
Anty hafsa itama akwai masifa don haka tamike dafad'a,
"nizakama rashin kunya,wato kashigo gari ka waye haryanzu jahilcin kauye bai sakekaba,idan laifi akamaka kai ataka basirar da wannan cin maganin dakakeyi zaka kwatarma kanka y'ancine,?
Tajuya a fusace ganin yanda yake harararta,yana mata qunquni.
"bari inkira police idan yaso idan kaje bayan kanta zakayi bayanin abinda yashigo dakai gidan matan aure."
Umma tariketa tana fad'in"me yayi zafi hafsat,bansanki da hakaba,
Kifara tambayar abinda zahra tayimashi don bana raba d'aya biyu itace ta tsokanoshi.."
Umma tasake kwantar da murya tana tambayar me agwaluma abinda yafaru,
Idanunshi taf da hawaye, yake bama umma ba'asin yanda komai ya farun.
Umma tagyad'a kai tana fad'in"nasan za'a rina ai,
Nidai zahra bazan maki bakiba sai dai ince allah ya shiryeki,abinda kikeyi amma nagaji nagaji da halinki bari babanki yadawo a tattara amaidake can kauye inyaso kici gaba da halinki a can am.a nikam nagaji."
Tajuya afusace tanufi d'akin da zahra tuni ta danna mashi sakata.
Anty hafsa tazuge jakarta tafiddo da dubu d'aya tamikama mai agwalumar tana hararashi dafad'in"next time kasan yanda zakayi magana da nasama dakai ".
Shima hararta yayi,
Sai dai bai tankaba.
Anty hafsa tadafa kafad'ar umma wadda tazauna zugwui da damuwar da zahra ke sakata akoda yaushe,
Tace"umma pls banason ganin damuwarnan taki,kina sane da lalular dakike fama da ita,
Umma kamata yayi kinama zahra addu'a bawai yawan damuwaba."
Umma tasauke numfashi"toyaya zanyi kinasaje da halin yarinyar nan,khatta da sunan da yaran unguwa suke kiranta dashi wai *zahra'u mala'ikar yara inkin mutu ba ruwan Allah walakiri ya jibgi kayanshi*."
Umma taci gaba"sam idan kinga nasamu naji sa'ida to kuwa zahra tatafi makaranta toyanzu hatta da makarantar abin yaci tura iya shege kullum sabon salo take fiddowa,jiya Monday tafara zuwa makaranta js 1,take amma wai baifi wata biyu da shigartaba yara bakwai ta fasama kai da dutse,dacirema wata yarinya ha'kori,
Principal ta bugeta shine tatara yara bayan antashi makaranta sukayima motar principal ature,da 'kasa har suka fasamata glass din mota.shine fa akazo hargida dakorarta sukayi dakyar babanku yasamu ya mayar da ita suka amsheta ,amna saida yabiya kudin duka asarar dasukayimata kinga ayau har ta dakko wata maganar.
[9/20, 1:16 PM] mum meenat: Anty hafsa ta sauke ajiyar zuciya,
"nidai umma sainake ganin kamar lamarin zahra fa akwai sa hannu wannan abin datakeyi bafa normal abu bane,gaskiya is abnormal ne umma yakamata mutashi tsaye,yarinya saikace ana kad'ata da ruwan hanji sam zahra bata d'auko halayyarmuba."
Umma tace "kema kya fad'a ai,nida ace ba'a gida na haifi zahraba tozan iya rantsewa da Allah anyiman musayar tane batawa bace ba.gata sam bata d'auko kamanni dakuba,hakanan bata dauko halayyarkuba.
Ku shidda na gaifa allah ya dauki ran maza biyun dasuke cikinku sai kumata guda hud'u da allah yabarmun,duk na aurar daku ku ukku akan matakin karatun zamani dana addini dai dai gwargwado bamu tauyekuba,gakunan duka cikin rufin asiri amma zahra sam tazamo zakka acikinku,itabaga karatuba baga natsuwar ba,itakenan kamar tunkiya duk inda ta gifta sai ance kayya."
Umma ta'kare maganarta kamar zata fashe da kuka.
Da'kyar anty hafsa ta shawo kan umma,ta lalla'bi zahra ta bud'e dakin tanufi kitchen tadauko abincinta wanda tuni ya sandare saboda hucewa,
Tazauna kamar wata saliha tanacin abincin anty hafsa namata fad'a akan rashin jinta.
Itadai bata tankaba,
Har lokacin sallar la'asar yayi tatashi tayi wanka akaja wata kwasheshiyar jagira wadda tasamu matsugunni a gefen kunne,
Tad'auko janbaki jajawur ta dafsa bayan ta zagaye bakin nata da tarin ba'kin kwalli.
Tajuya da fuska tanama madubi murmushi tana tsuke d'an matsakaicin bakinta aganinta ba nabiyunta wajen kyau.
Duk da tana cikin 'kunci baihanata ganin kyawon nata ba
Sai dai aranta kullum tanajin haushin meyasa anty hafsa da anty salma kai harma da anty lubna duka suke farare tas,
Amma ita saitayo duhun fata,
Taja tsoki ita d'aya dafad'in"nadaisan dama ummanmu ba sona takeyiba shiyasa ta haifoni ba'ka.
Tasaka uniform na islamiyya check blue dasuka d'au guga sukayi luf dasu,
Tafito har lokacin umma bata dena fushi da itaba,
Takalli umman cikin kukawa tace"umma natafi,"
Umma tace"adawo lafiya sauran yauma akawomun 'kararki kinyi fad'a dawani mutum zaki bani labari."
Ta turo baki gaba,batare da tatankaba,
Umma tayi tsaki dafadin"shashasha kawai shekaru shabiyu amma fitinarki tafi ta masu shekaru ashirin."
Itadai gaba tayi abinta kamar yanda tasaba,
Tafito lungunsu tana gunaguni,charaf idanunta suka sauka akan na ishaq wanda ya sar'ke hannayenshi a kan kirjinshi yakafe kofar lungun nasu da idanu,
Duk da rashin tsoro irinna zahra saida gabanta yafad'i,amma dayake tsiwa gareta saita murgud'a mashi baki dafad'in''kurwa
ta kur namana d'aci,me d'a yaci d'anshi mara d'a yaci 'ko'kon tsuliyarshi."
Ishaq duk da baya jiyo abinda take fad'i shidai komai takecewa ahakan burgeshi tayi,
Yanason d'an murgudennan nata,
Ya numshe idanu daya tuno da zahra gaf da bikinsu yakafeta da idanu tayimashi murgud'e dafad'in "kallonfa,
Alokacin murmushi yasaki yanace da ita"nanda wata biyu saina tsotse bakin murgud'enanna naki."
Alokacin dariya tasaki dacewa"kai yaya ishaq,bakajin kunyata nifa kanwarkace".
Ya runtse idanu,kamar zai fashe da kuka afili yafurta "i really luv yhu zahra,inason koda mace mai sunankine bare kuma mai kammani dake."
Post everyday nsha Allah
September 20, 2017 at 7:31pm ·

��������

by
Anty yar charas ����
[12:03, 24/11/2017] hm: *MIJIN 'KWAILA*����‍♀

*to you maman Aliyu this page is for you*��



Chapter 3.


'karfe hudu na yamma dai dai lokacin da matashin ya cinna hancin motar tashi yazuwa cikin tanqamemen get d'in gidan,tare da matsa horn wanda yasaka megadin tashi da sassarfa yaxuwa bud'e katon get din.
Kamar almara ko mafarki haka baba yusha'u yake kallon fuskar ubangidan nashi dake cike da zallah nishad'i,
Yasake murza idanuwa aranshi yana ayyana'shin anma oga kyautar d'an mutum ne da kayanshi kome,?
Ganin yakasa aiwatar da aikinshi yasaka ishaq sake matsa horn da 'karfin gaske wanda yasaka baba yusha'u tale get din yana washe hakora dafad'in"barka ubangidana barka dazuwa isyaku na zahra baban zahra kaga angon zahra'u...
Isha'q ya numshe sexy idanunshi lokaci guda yanajin wani yanayi yana tsalga ainahin 'kasan zuciyarshi,
Ya'isada shigoda hancin motar lokacin daya saka hannu a aljihun jeans dinshi ya dumbuzo kud'in da bazai tantance adadinsuba ya dam'kasu ga baba yusha'u wanda tuni ya warcesu yana sake jinjinama isha'q d'in.
Yafito daga motar bayan ajiyeta a mahalinta,yana cilla key's din motarshi sama yana cafewa a tattare dashi akwai zallah nishad'in daya kwashe watanni shidda gam batare dayayi makamancin hakan ba.
Yakutsa kai acikin 'katon falon dayakai ma'kura wajen tsaruwa,dagani babu tambaya yasamu tagomashin dukiyarda tsayawa 'kididdigeta 'bata likacine.
Da sallama yashiga cikin falon idanunshi suka sauka akan 'katon kyakyawan hoton zahra wanda tayishi alokacin datake saukowa daga cikin jirgi,ajikinta akwai ba'kar suit saitayi roling white gyale akan wuyanta harzuwa kanta.
Fuskarta akwai full make'up don ita gwanar kwalliyace abinda yake karama isha'q kaunarta don yanason mace y'ar gayu.
Tasaki silent smile dake 'kayata fuskarta mai matsakaicin kyau.
Duk da ganin doctor ruqayya (wato mahaifiyarshi)
Baihanashi 'karasawa ga hotonba yasaka yatsanshi guda ya xagaye gefen kumatunta dake murmushin,lokaci guda idanunshi suka canja kala,
Yajuya kamar zaifashe da kuka,muddin zaidinga kallon hoton zahra bazai ta'ba kallon wata d'iya mace da gashiba,
Face zahra mai kamanni da zahransa.
Yadad'e tsaye jikin hoton yanason tabbatarma kanshi banbancin dake tsakanin waccen zahra 'karamar dakuma real zahramshi,amma yakasa gane koda abu d'aya dazai iya tabbatar mashi cewa bafa zahranshi ce takoma 'kan'kanuwaba.
Doctor ruqayya tatako a hankali zuwa kusa da d'an nata tadafa bayanshi cikin sanyin jiki da'alamar tausayawa kamar yanda tasaba.
Sa'banin da ayau fuskarshi fayau take babu tarin damuwarnan dake 'boye kyawon fuskar tashi.
Kama hannayenta yayi duka guda biyun idanunshi cikinnata duk da nata idanun suna manne da siririn farin glass din (medical).
Saida ya 'kawata fuskarshi da murmushi sannan yace"mummyna nasamu zahra..zahra tadawo gareni mummy awannan karon bazatayi nesa daniba,d'iyarki tadawo gareki mum....!
da hannu ta dakatar dashi"isha'q wai sai yaushene zakasan wanda yamutu baya dawowane,ayaushene zakasan cewar allah daya d'auki zahra yafimu 'kaunarta.saiyaushene zaka dena takura tunaninka da lafiyarka akan wadda babu ita a doron duniyane?
Zahra ta mutu, a gaban idanuna aka wanke gawar zahra.zahra d'iyar 'kanwatace nice na reneta tundaga ranar da mahaifiyarta ta haifeta batakoga fuskartaba takwanta tamutu,naso zahra na tausayama zahra nasani bayagani kaine mutum na biyu dayasha d'awainiya da zahra amma kasani zahra ba rayayya baceba.
Mutayata da addu'ar gafara dabeman dacewa don zahra mutumce guda harda 'kari
Ama yamuka iya'allah yafimu 'kaunar zahra ya amsheta a daidai lokacin damukafi bu'katarta,saimu bita da add'ua kaikuma kasaka dangana wa ranka ka rungumi 'kaddara matsayinka na musulmi nagari."
Bai katsetaba har saida ya tabbatar da takai aya,sannan yaaja hannayenta yaxuwa d'aya daga cikin kujerun falon yazauna yana fuskantarta,bayan yagama saita dukkan natsuwarshi gareta don ta yarda dashi takuma gane baizo da wasaba a wannan karon."mum wlh kiyarda dazancena mum,naga zahra ganin idanuna,zahra dai mum tana cikin students mum, a tattare da ita akwai yarinta nasani bawai ainahin zahrata baceba.amma inada tabbacin wannan itace zahran da zahrana take gayamun akoda yaushe,itace wacce zahra kefad'amun cewar _isha'q zaka samu zahra madadina koda bayan raina,zakasamu xahran da zata d'auke maka kewata.naro'keka da kobayan babu raina kajirayi xahra,kasota kamar yanda kake sona koma fiye da hakan._ _inamai tabbatarmaka itace alkairi a gareka._
Yaci gaba dafad'in"mum dani dake daduk wani ahali na gidannan yasan dahakan,mum kinatsu kituna maganganun zahra don allah kada kice wai bana cikin hayyacina."
Doctor ru'kayya tami'ke cike da tsantsar tashin hankali,tana zagaye katon falon hannunta goye a bayanta akan fuskarta akwai zallah damuwa dakuma rud'ani.
Sai dai kuma batasan tayaya zata'iya 'karyata isha'q a 'irina wannan lokacin dayazo mata da magana sahihiyaba.
A dukkan nazarinta dakuma hasashe irinnata tanada tabbacin isha'q yana cikin natsuwarshi ne.
Tasauke numfashi,itakam a dukkan tarihi ko'a mafarki kai a film's ko fili bata ta'ba ganin soyayya...


Read / Download MIJIN KWAILA

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album