Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

ABINDA AKE GUDU Complete Hausa Novel Document by ABINDA AKE GUDU


ABINDA AKE GUDU

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 101765



ABINDA AKE GUDU

Reading Time: 8 Hours

Added On: 02, Sep 2023

Author: Batul Mamman ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 541.71 kb

File Type: txt

Views: 2019+

Download: 1430+

Last download: 4 days ago

Description/Story: ABIN DA AKE GUDU
Na Batul Mamman
Ebook creat by Shuraih Usman
Ebook publish by www.hausaebooks.cf
Ebook din nan yazo maku ne daga shafin www.hausaebooks.cf
Kuna ziyartar shafinmu don samun sababbin littatafai
Ga duk wanda ke bukatar ebooks nashi ya samu shiga cikin wepsite namu sai ya turo mana da littafin ta Email namu [email protected]

ABINDA AKE GUDU 🙆🏽 1
Batul Mamman💖
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
Daki ne cike da 'yan mata sai hayaniya suke yi. Wasu
suna saka kaya wanda ya kasance atampa ce ja mai adon
baki, wasu kuwa kwalliya suke yi a gaban madubi.
Wadanda basu sami wuri a gaban madubin ba da na
jikin hodarsu suke amfani ana ta fentin fuska cikin
nishadi.
Suna wannan hirar da shewa wata mace da bazata wuce
shekaru talatin ba ta shigo da katon cikinta ita ma irin
atampar jikinsu ta saka tayi kwalliya daidai gwargwado
cike da damuwa ta soma magana.
" don Allah kuyi sauri ku fito ku ake ta jira. Umma sai
fada take min babu amarya babu kawayenta. Kun dai
san tayi ta kashedi akan African time".
Wata cikinsu wadda da alama ta gama nata shirin tace
"kiyi hakuri Anti Shema'u yanzu zamu fito".
"Babu wani yanzu zaku fito. Ina Asma'un?" Ta fada tana
dube dube.
Can gefen gado ta hango kanwar tata ana rangada mata
kwalliya irin ta amare tayi kyau sosai. Kusa dasu Shemau
ta koma ta sake nanatawa mai kwalliyar tayi sauri ta
gama a fito da amarya. Ita dai Asma'u har yayarta ta
gama magana bata ce komai ba saboda kada ta bata
kwalliyarta. Wannan rana ce mai matukar mahimmanci
a rayuwarta. Ranar kamunta da mutumin da take ganin
tamkar babu irinsa a duniya.
Har Shema'u ta fara tafiya tayi saurin dawowa da sauri ta
sake kai idonta gaban rigar jikin amarya. Daure fuska
tayi " duk amaryar duniya idan ana bikinta rama takeyi
saboda zulumin barin gida da sabuwar rayuwa banda ke
Asmau. Dubi yadda rigar nan ta sake matse ki duk
kirjinki ya fito ta sama".
Hannu Asmau tasa ta rufe jikinta saboda yadda 'yan uwa
da kawayenta na dakin suka maido da kallonsu gareta.
Shemau ta cigaba da magana "ki tabbatar abinda zaki
yafa ya rufe miki kirji don bani da amsar bawa Umma
idan ta fara fada." Daga nan ta fice tana mamakin irin
wannan jiki na kanwarta. Dama can ita mai jikin kiba
ce....
******
Farfajiyar gidan ta gama cika da mata inda aka kawata
wani bangare da ado irin na gargajiya domin zaman
amarya. Ga kujeru da tebura wurin yayi kyau sosai
harda turaren wuta na tsinke da na garwashi aka kunna
sai kamshi ke tashi.
Mai gabatar da taron mace ce ta nemi kowa yayi shiru
saboda amarya zata fito. Mai kida ya canza salon kidansa
da wanda ya dace da amarya aka fara ita da kawayenta
suka fito suna taku daidai.
Sunyi matukar kyau da burge mutane da irin salon
fitowarsu. Aka dauki tafi, masu hoto kuwa na camera da
na waya suka fara aikinsu. Haka suka rinka tafiya har
suka karasa inda zata zauna. Autarsu ce Aina'u 'yar
kimanin shekaru sha uku a tsaye da mafici irin na kaba
yayarta na zama ta soma yi mata fifita a hankali. Hakan
ma ya kayatar da mutane.
Hajiya Bara'atu dake zaune cikin 'yan uwanta da kawaye
har 'yar kwalla sai da tayi. Gashi cikin ikon Allah karo na
biyu kenan da zata aurar da daya daga cikin 'ya'yanta. A
hankali tace " Allah Ka jikan Alhaji" bai rayu yaga auren
'ya'yansa ba bare yaga jikokin da suka fara tarawa.
Daga nan fa aka soma shagalin biki inda aka bukaci
dangin ango su fito domin kamun amarya. Suna tahowa
Asma'u ta bawa Walida aminiyarta wayarta ta rada mata
a kunne ta dauketa a hoto idan ana fesa mata turaren
kamun. Walida tace "uhmm su Asmau an iya soyayya.
Nasan sarai Abubakar zaki turawa".
Asmau ta juya ido tana fari "ke kuwa an hana bawan
Allah ganin iyalinsa dole na taimaka masa da hoto".
Dariya duk suka yi sannan aka cigaba da biki.
******
Ana soma kiran sallar magriba aka gama taron shiyasa
dama Haj Bara'atu ta rinka nanata musu banda African
time. Sallah aka tafi a gabatar harda amarya wadda ta
gaji sosai. Dakinta suka nufa ita da kawayenta suka yi
tasu sallar. Tana idarwa aka fara yi mata tayin abinci,
kafin a kawo ta dauki wayarta ta turawa Abubakar
hotunan kamu.
A lokacin yana tare da abokinsa Qasim. Shi dai Qasim
gani yayi Abubukar ya dan matsa ya fara waya.
Murmushi yayi don yasan da wa ake wayar. Hira suke yi
sosai yana fada mata yadda tayi kyau da kuma rashin
jindadinsa da aka hana shi zuwa wurin kamun.
Karshen gado ta koma ta rungume waya suna ta hira.
Tun ana cewa ta sauko ga abinci har suka gaji suka dena.
Ba su suka gama wayar ba sai da ya fara jin kiran sallar
isha daga masallacin gidansu wanda suma su Asma'u shi
din suke ji. Sallama suka yi tare da alkawarin zai kirata
anjima.
Tana saukowa daga kan gadon ta dafe cikinta "yunwa
nake ji kamar na kwana ban ci abinci ba"
Walida ta dan harareta "abincin ai ba jiranki zaiyi Juliet.
Ni nayi tsammanin a irin soyayyarki da Romeo din naki
baku san yunwa ko kishiruwa ba idan kuna tare".
"Nasan ba wani abu ke damunki ba sai tafiyar da rabin
ranki Babangida yayi gashi ba kya samunsa a waya sosai"
Asmau ta fada cikin tsokana ai kuwa Walida ta jefeta da
pillow tana fada. Babangida yaron gidansu Walida ne irin
almajiran nan marasa kunya gashi ya kware wurin kaiwa
matar babansu gulmar duk abinda take yi shiyasa ta
tsane shi. Har kusan daya na dare 'yan matan suka kai
suna hira sannan bacci ya dauke su. Wasu akan gado
wasu a katifun da aka shinfida a kasa.
Cikin bacci Asma'u taji wayarta na kara ta dauka cikin
magagi. Tana ganin sunan mai kiran ta wartsake.
Cikin taushin murya yace " Asmy na tasheki daga bacci
ko?"
Sai a lokacin ta kula karfe hudu da kwata na dare sunfi
wata daya yana tashinta a irin wannan lokacin dama.
Ta dan shafa idanu "babu komai Yayana yau mun so mu
makara ma".
"To a tashi ayi a nemi kusanci da Allah. I love you Asmy."
Murmushin da yake so a gareta tayi sannan tace "me too
Yayana".
Bayan ta ajiye wayar tashi tayi ta fita ta tafi bandaki ta
dauro alwala. Nafila tazo ta fara yi sannan ta dukufa
istigfari kamar yadda suka sabarwa kansu ita da
Abubakar har aka kira assalatu. Sake kira yayi ya
tabbatar idonta biyu sannan ya tafi masallaci ita kuma ta
tashi 'yan matan dakin ta tayar da tata sallar.
*****
Yau ta kama alhamis babu wani taro da za'ayi a gidan sai
karfe bakwai da rabi da za'ayi dinner da daddare.
Qasim yazo har gida ya sami Abubakar tare da takardar
da aka bashi ta canjin wurin aiki da karin matsayi. Abin
takaici ana bukatar lallai yaje ya gabatar da kansa a
sabon ofishin da aka tura shi a Zamfara kafin litinin mai
zuwa. Abubakar ya taya shi murna sai dai sunyi
bakincikin bazai sami dinner da daurin auren abokin
nasa ba. Abubakar duk ya shiga damuwa Qasim ya rinka
kwantar masa da hankali.
Abubakar yace "yanzu tunda ka zama ACP Qasim to sai
ka nemo mana mata musha biki."
Dariya Qasim yayi "wace mata zan nemo bayan kasan
albashin dansanda har yanzu bai taka kara ya karya ba."
"A dai rinka godewa Allah" Abubakar ya fada yana saka
takalmi. Har bakin mota ya raka Qasim. Dukkaninsu
basu ji dadin zuwan canjin aikin a wannan lokacin ba.
******
Kwalliyar Asma'u ta yau har tafi ta jiya. Kawaye da 'yan
uwanta kowa yayi irin nasa adon. Anti Shema'u, 'yarta
Mimi da Aina'u kayansu iri daya. Mazan gidan su biyu
suma shadda suka saka iri daya.
Suna gama shiryawa motar ango tazo daukar amarya.
Shima kayansa ya dace da nata. Tun a gida ake daukarsu
hotuna haka a wurin dinner din. Abin ya kayatar saboda
komai anyi shi cikin nutsuwa irin na 'yan boko. Duk
motsin Asma'u idon Abubakar yana kanta suna hada ido
sai suyi murmushi. Soyayya ce da ta samo asali tun
farkon tarewarsu Asma'u a unguwar su Abubakar
shekaru tara da suka wuce.
Sai wurin shadaya da rabi aka tashi daga taro kowa ya
tafi gida. Wani abokin Abubakar ke tuka motar suka
ajiyeta a gida sannan suka wuce.
******
Washegari Juma'a gidan commissioner kamar yadda
duk 'yan unguwa suka sakawa gidansu Abubakar sun
tashi a makare saboda gajiyar da suka kwaso a wurin
dinner da kuma sanyin da aka tashi dashi.
Mahaifinsu Alh Adamu Matawalle tsohon dan sanda ne
har commissioner ya taba yi. Da taimakonsa Qasim ya
sami aiki ma. Matarsa daya Yalwa wadda suke kira
Mama. Su shida ta haifa. Babban danta sunansa
Abdulhalim yana da mata daya da 'ya'ya biyu sai mai
binsa Nasiba itama tana gidan nata mijin. Abubakar ne
na uku amma kannensa mata biyu Sadiya da Suwaiba
duk sunyi aure. Su biyu suka rage shi da autansu Umar.
A gaggauce suka tashi domin baifi awa daya da rabi ya
rage musu ba lokacin daurin auren ya yi. Mata suka tashi
aka shiga kitchen saboda abokan Baba kamar yadda
suke kiran mahaifinsu a gidan zasu ci abinci idan an taso
daga wurin daurin auren. Ga samari 'yan uwa da suka
kwana a gidan su ma shiyasa aka yi ta layin shiga wanka
a bandakuna biyun dake bangaren maza. Da gangan
suka ki barin Abubakar ya fara shiga a cewarsu shi ango
dole a jira shi.
Baifi minti talatin ya rage ba Umar ya fito daga bandaki
kumfar jikinsa bata gama fita ba Abubakar ya shiga ya
rufe kofar da mukulli.
Sauran samarin
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download ABINDA AKE GUDU

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album