Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

WACE CE NI Book 3 Complete Hausa Novel Document by WACE CE NI Book 3


WACE CE NI Book 3

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 30631



WACE CE NI Book 3

Reading Time: 2 Hours

Added On: 22, Sep 2024

Author: Hafsat Sodangi ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 152.56 kb

File Type: txt

Views: 488+

Download: 454+

Last download: less than 1 second ago

Description/Story: WACECE NI? -3


Umma ta mike ta dauko rigar baccin
dake ajiye can gefenta ta miko min.
"Karbi ki suturta jikinki." Tayi maganar ba taree
da ta kalle ni ba.
Hannu biyu nasa na karbi rigar nayi yanda
tace din, tana ganin nayi hakan ta nemi wuri ta
zauna tana kallona cikin natsuwa ta ce "menene
masalar da ta hanaki zama wurin mijinki ku
more darenku na farko?"
Nayi maza na sunkuyar da kaina kasa saboda
jin nauyin maganar tata, gaba daya mukayi shiru
na dan wani lokaci zuwa can sai na kawar da
shirun namu ta hanyar yi mata tambayar
taimake ni mana Umma yau kam ki gaya mun
gaskiyar al'amarina taimake ni ki gaya mun don
in san ni wacece?" Kallon da naga tayi min shi
ne ya firgita ni, nan da nan naji cikina ya bada
sautin kululululu.... cikin rawar jiki na tambaye
ta "Da gaske ne Umma ni din shegiya ce?" Ta
dan girgiza kai a hankali tare da fadin cewa "ko
kadan ke ba shegiya ba ce Adawiyya." Na dan
samu 'yar natsuwa kadan saboda jin abin da ta
fadi, don haka sai na dan kara mats awa jikinta
na ce, "Gaskiya Umma ke din ke kika haife ni?"
Na zuba mata ido ina kallonta tare da sauraron

7


irin amsar da zata bani, sai na sake ganin ta
motsa kanta.
Da hannu biyu na bugi kirjina cikin tsananin
kuka na ce mata "Na shiga uku Umma, tunda ba
ke kika haife ni ba?" Na kama kuka mai
tsananin yawa ina fadin "Shi kenan Umma ta
rasa ku dukanku na rasa Baba kema kuma a yau
na rasa ki bani da kowa kenan a duniya?"
Umma ta jawo ni jikinta ta rungume itama
taya ni kukan take yi tana fadin "Ba ki rasa
kowa ba Adawiyya, ni da Alhaji mune iyayenki
da kika sani mune kuma iyayenki na har abada
ban taba tunanin hali zai yi da zan bayyana
wannan sirrin ba in banda tsananin son da nake
yiwa Babangida, da ban bari akayi aurenku ba,
don nasan yin auren naku yana nufin bayyanar
asirin da na dade ina boye miki.
Na sake kallon Umma a kidime na ce mata
"umma amma ai dake nake takama, gashi kuma
a baya kin taba ce min kin haifi Rabi'atu kin
kuma gaya min cewar Umma amarya tazo gidan
nan da yaro a goye to ina ce shine yaya Almu?"
Cikin natsuwa Umma ta kalle ni ta ce min,
wancan yaro da na baki labari tuni dangin
Ubanshi suka kar ba, duk da Alhaji yayi iyakar
kokarinshi wajen ganin an bar mishi rikon shi
amma basu yarda ba bisa uzurin da suka bayar
8

na cewar shi kadai ne dan uwan nasu ya rasu ya
bari maganar haihuwar Rabi'atu kuwa biyo ni
kawai kisha labari, a baya na tsaya ne a inda na
gama baki labarin isowar Maryam gidan nan to
yanzu ma daga nan zan tashi.
"Isowar Maryam gidan ya saman min da
saukin fitina ne, amma ba fita hanyata karama
tayi ba, domin duk da amaryar da akayi mata
kishinta yafi tsanani a kaina, don ita da bakinta
sai da ta rinka gayawa mutane cewar da ta zauna
dani a matsayin kishiyarta gara ta zauna da
kishiyoyi guda uku duk da ita su zama hudu."
Umma ta dan saki wani lallausan murmushi
bayan fadin hakan da tayi. Sai kuma ta ci gaba
da fadin "Baba abin da karama ta ki irin taga
Alhaji a dakina koda kuwa nice dashi sai ta rasa
kwanciyar hankali ta rasa inda zata tsoma ranta
taji dadi muna cikin wannan zama ne mutancen
gida suka gane ai Amarya ciki ne da ita, shi
kenan ana gance hakan sai kuma kishin Karama
ya kema can zaman lafiya ya gagara a
tsakaninsu fadan safe daban na yamma daban
bayan kafin ta gane Maryam na da juna biyu
duk kokarinta bai wuce na ace su biyun sun
hade mun kai ba, ita Maryam din ce bata yarda
ba rikici tsakaninsu yayi tsanani 'yar magana ba

9
magana ba kumą sai ta rarumeta da danbe sai da
Baba ya gaji da hakan yasa baki yayı kashedi
akan danben shine aka dan samu sauki.
Ni kam ina gefe kallonsu kawai nake yi ina
kuma iya kokarina wajen boye halin na nake
ciki saboda ban son a gane amma duk da yake
sai da Alhaji da Baba suka gane ina zaune a kan
tabarma a dakina rannam ina dama wa Alhaji
furar da zai sha bayan dawowarshi daga kasuwa,
sai ya kalle ni ya ce min "iko sai Allah, watakila
kuma bana yan tagwaye zan samu a gidannan
da kuma shekara da shekaru babu ko daya." Na
yi kamar ban ji shi ba, na mika mishi furarshi ya
kama sha.
'Yan kwanaki kadan bayan bayan nan kuwa
ina tare da Baba muna hira sai ya ce min "to wai
ni Zuwaira da kike ta faman wannan 6oye-
boyen kin mance ne uwarki mai yi min lissafin
cikinku yau bata nan? Na sunkuyar da kaina
kasa cikin hawaye saboda na kasa daina kukan
mutuwar Baba Rabi kullum cikin kewarta nake
anyi wannan zancen babu wani dadewa sai
kawai na haifi 'ya mace abin da ya baiwa Kowa
mamaki har Alhaji da Baban da suka gane
akwai cikin balle kuma wadanda basu gane ba a
wannan lokacin yaya Balki ce ta tsaya akan
hidimar jegona don gaba dayan matan gida sun
10

Ce babu hannunsu tunda dai na 6oye musu cikin
don ina tsoron kar suyi amfani da maitarsu su
Cinye abin da yake ciki to yanzu ma da ya fito
ba za su taba shi ba don haka ita ce mai samun
ruwa ta kwashe ta wanke yarinya ta gasa mata
cibiya ita kuma Maryam tana yi mun wankin
kayana da na yarinya dama duk wani aiki da ya
dangance ni.
Ranar suna Baba ya sanyawa yarinya suna
Rabratu a wannan loka cin ba karamin karamci
yaya Balki tayi min ba don kuwa har nayi
arba'in 1ta ke sanya mun ruwan wanka ta kwashe
tayiwa yarinya wanka safe da yamma bata yarda
ta bari ba kamar yanda Alhaji ya ce ta huta da ji
da hidimar yaran dake dakin ta wajen su bakwai
ga guda biyu da ta haifa a kurkusa wadanda
basa yarda su rabu da jikinta ko ina take suna
manne da ita uwa da kuma Jumaindu.
Ba zai yiwu in tsaya kwatanta miki irin son
da Alhaji da Baba suke wa yarinyar nan ba illa
dai kawai in ce miki ba al'adar mazan gidan ba
ne daukar ya'yansu amma shi kam daukarta
yake yi ya fita da ita ya kaita wurinta Baba suyi
hira in kuwa ya ganta a bayana tana kuka ko ya
ji ta zai ce min ban ita nan, ko da kuwa a cikin
mutane ne nayi-nayi ya daina don ina jiye mishi
kunyar hakan da yake yi,amma ya ki dainawa
11

sai ya ce "ke kyale ni kin hi shekara nawa nayi
ban same ta ba?"
Mun samun wajen watanni uku a lokacin nan
tafi wani jaririn mai wata biyar girma da kuzari
gata da idanuwa dara-dara gashi ba na jin
kunyar gyarata kullum cikin tsabtace ta nake sai.
kawai ta kamu da mura mai tsanani na wuni
daya kawai sai kuma ta ce ga garinku nan.
Baba ya yi ta kuka ina bashi hakuri shima
Alhaji ya shiga cikin damuwa mai tsanani
kowane loka ci sai yayi ta fadin "oh ashe
yarinyar nan ba zama tazo yi ba?" In dan yi
murmushi in ce mishi "I, ba mai zama ba ce sai
kayi hakuri ya ce to yaya zanyi? Ni kaina boye
damuwa kawai nayi amma zuciyata takai
matukaa wajen zafi, don kuwa ina son da a
wannan lokacin ban sani ba ko Baba ya gane
hakanne sai ya ce min dakin nan naki zaiyi
mikifili mai yawa na rasghin Rabi, koda take
yar karama kin riga kin sa rai da ita. Don haka
ki dauki Uwa itama wata Rabin ce sai ta rufa
miki gurbin da ta bar miki." Nayi nurmushi na.
ce "To Baba daga wannan ranar kuwa sai na
kar6i rikon Uwa daga wurin Yaya Balki hakan
kuma sai ya kara karfafa kauna mai yawa a
tsakaninmu har muka zama tamfar 'yan uwa

12

Sati uku cif da rasuwar Rabi'atu sai Maryam
ta haifi da namiji na kai wa Baba shi, bayan
nayi mishi wanka ya kare mjshi kallo ya ce
"kamarshi, daya da 'yar uwarshi da mace ne da
sunanta na mayar mishi sai ki sa hannu biyu ki
rike shi naki ne ki dauka shi da 'yar uwarshi da
ta tafi duk daya ne tunda 'ya'yan Bello ne na ce
"mishi to Baba na karbe shi na tafi na bar shi
yana share hawaye da gefen rigarshi ni Baba ya
tantaya in fadi sunan da nake so a sanyawa jariri
na ce' yasa mishi sunaishi don haka ranar suna
sar aka rada mishi Muhammadu Mustapha ni
nake kiranshi Babangida shi kuwa Baba yake ce
mishi Lamido.
Hannu biyu na saka na karbi al'amarinshi tun
yana dan jariri na kai kai shi gun Maryam ne
kawai don yasha nono tunda Junaidu yaga jariri
a dakina kullum zai zo ya zauna kusa dashi
dama kuma ga Uwa ta dawo dakin don haka sai
ya zama dare ne kawai ke raba shi da dakin
daren ma kuma sai an bari yayi bacci nake kai
shi ko kuma ita ta turo a dauke shi. Rannan ma
dai da Alhaji ya gaji da ganın hakan sai ya ce
min to wai ke me zai sa ba za ki bar yaron nan a
dakin nan ba ne kawai ki hada su ki rike? Ina
amfanin kullum sai an sako shi a dauke shi?" Na
ce mishi to.
13

Shi kenan sai gani da 'ya'ya uku a
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download WACE CE NI Book 3

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album