Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

'DAN GARGAJIYA Complete Hausa Novel Document by 'DAN GARGAJIYA


'DAN GARGAJIYA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 8964



'DAN GARGAJIYA

Reading Time: 0 Hours

Added On: 24, Feb 2025

Author: Ummu Rahma ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : ‪+234 803 509 6818‬

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 50.3 kb

File Type: txt

Views: 14+

Download: 14+

Last download: less than 1 second ago

Description/Story: [4/10, 7:57 PM] ‪+234 803 509 6818‬: *👳🏼👳🏼'DAN GARGAJIYA👳🏼👳🏼*
*(gargajiya ba addini bane)*



*Na*
*Ummu Rahma* ✍🏻




*Gajeren labari mai dauke da nishadi, gidadanci da rashin wayewa ta addini*



*1⚜5*



*BIRNIN KAHUTU*



Kwance bahijja take cikin tsananin ciwo na nak'uda gashi babu kowa a tare ita, sai addu'o'i takeyi ga mahaliccinta na samun sassauci, can wani kuxari yazo mata ta ja jiki ixuwa kan mudubin ta ta dauko wayar ta ta danna lambar mahaifiyarta, bugu biyu ta dauka tare da karawa a kunnen ta, nan taji muryar 'diyar tata tasan ba kalau ba.

"Umma ki yafe ni mutuwa zanyi ki rokar min Baba ya yafe min shima" Bahijja ke fadin haka inda hankalin mahaifiyar yayi mutuqar tashi domin tasan diyar tata na tare da tsohon ciki ga ta kuma a gidan gargajiya, tana tsaka da tunani saiga Alhaji Mahmud ya fito daga wanka.

Nan ta sanar dashi abinda me faruwa aikuwa ya zura kayan sa yace suje su ga halin da take cinki. Ya dauko motar sa suka tafi, da Isar su yace Umma ta shiga ta gano halin da take ciki, shigar ta da kamar minti biyu sai ga ta dawo a guje tana fadin Alhaji shigo mu kamo ta zuwa asibiti kan 'da ya fito gashi ko motsin kirki bata iyawa.

Tun kan ta karasa Alhaji Mahmud yayi ciki a guje ya dauko ta suka nufi asibiti, isar su ke da wuya nurses suka kawo musu agajin gaggawa inda aka dauke ta zuwa dakin haihuwa Dan ceto ranta dana yaron.




A bangaren Badaru (mijin bahijja) kuma yana dawowa gida ya kutsa kai cikin gida yana muzurai shi a dole baya son raini, yana shiga yaga bata nan, nan ya fito ya shiga wurin mahaifiyar shi yake tambayarta ko ta shigo gidan, kada baki tayi tace yoo ni ina na ganta.


Suna cikin haka saiga k'anwar Badaru nan ta dawo daga aiken da aka mata, nan ta Sanar dasu cewa ai taga Umman ta sunzo sun dauketa zuwa asibiti, nan ya mulmulo wani uban zagi yace "mu za ai wa birnanci a karya mana tsarin iyaye da kakanni alhalin ni *'Dan Gargajiya* ne gaba da baya" fuuuu ya fice sai asibitin da yake tunanin nan zai samesu, aikuwa yayi Sa'a nan din sukaje danya hango surukar tasa a zaune, nanfa ya shiga cikin inda nurses suke da masu kawo yan haihuwa, nan fa Badaru ya fara tijara yana bubbuga kirji yana fadin "mu 'yan gargajiya ne ba'a mana iskanci, kawai an dauko min mata ba tare da an sanar da ko mahaifiyata ba an kawo ta nan, wannan ai reni ace mahaifiyata tana raye ace ba'a sanar da itaba saidai taji daga baya".



Umman bahijja tace kayi hakuri mun same ta ne cikin wani hal... bata qarasa ya katse ta yana zuba rashin arxikin sa son ransa, duk abinnan dake wakana kowa ya kasa cewa Badaru komai har ma'aikatan jinyar, nan wata jajirtacciya ta taso adaidai lokacin dayake cewa uban wa yasa a kawo mishi mata asibiti, a zuciye ta dira gabansa tace ubanka ne......



Wai shin wacece wannan, kuma ya zasu kare da badaru?


Amsoshinku na shafi na gaba.



Kuyi hakuri bana iya yin dogon shafi.




*Ummu Rahma ce*✍🏻
[4/10, 7:57 PM] ‪+234 803 509 6818‬: *👳🏼👳🏼'DAN GARGAJIYA👳🏼👳🏼*


*(gargajiya ba addini bane)*



*Na*


*Ummu Rahma* ✍🏻



*Gajeren labari mai dauke da nishadi, gidadanci da rashin wayewa ta addini*


*5⚜10*


Kai wane irin mara tausayi ne, wane irin mutum ne kai mai butulcewa rahamar mahalicci, ka ko san a halin da aka kawo ta nan zaka zo kana wa mutane rashin arziki.


Badaru yace mata " ba ruwanki hajiya" yana muzurai kamar ya tik'i gudu a filin tsare.

Malama Ramatu tace da ruwa na mana saboda 'ya mace ka tab'a, kai zakaso ayiwa k'anwar ka haka ko 'yarka ko mahaifiyar ka.


A a hajiya banda Babata wlh. Mal Ramatu tace harda ita, ita wannan da make ciwa mutunci ba uwar wata bace, duk wannan maganganun suna yin shine a hasale, Mal Ramatu kuwa kamar ta rufe shi da duka.

Ta dora da cewa yanzu kai saboda Allah kayi daidai kenan wannan 'dabi'ar da kazo ka nuna har kana wani ikirarin kai Dan gargajiyane, to ka fada min inda ya samo asali a addini.



Shiru Badaru yayi yana tunanin k'arfin hali irin na wanna mata, bai gama tunanin sa ba yaji ta jefo masa wani tambaya da cewa, 'yayanka nawa, Badaru kamar bazai amsa ba yace 'yata daya na biyu za a Haifa.


Malama Ramatu tace Alhamdulillahi ka rubuta ka ajiye watarana zaizo kanka.



Badaru zaiyi magana kenan wata nurse ta fito daga dakin karbar haihuwa dan kiran Malama Ramatu domin patient dinta ta sauka, dama ita ma mai haihuwa ta kawo, har tayi gaba ta juyo tace kuma zan dawo gareka.....



**** **** ****


*'KAUYEN BANDAAS*




Hinde! Hinde! Hinde! Wai ina kika shiga ne ga awakai can zasu cinye ya'diyar dana zo da ita ki dafa min, jin shiru wacce aka kira da Hinde bata fito ba yasa shi 'dage labulan 'dakin nata Dan yaga ko tana ciki.



Turus yayi ganinta tana sallah, nanfa ya hau sababi ta inda yake shiga ba tanan yake fita ba.



Yanzu Hinde saboda taurin kai irin naki sallar ma baza ki bari ta nuna ba sai kinyi ta yanzu, dama nasan za a rina, shiyasa liman yana sallame wa na taho gida dan in ganewa idanuwa, ke kullum bakya bin abinda iyayen mu suka bari saboda kinje birni kin koyo rashin biyayya, ace Juma'ar ma bazaki bari sai an dade da dawowa ba sannan kiyi taki saboda taurin kai.



Duk wannan fadan da yake yi Hinde tana sauraran sa kuma tana jin takaicin halinsa da a komai saiya sako batun *Gargajiya*.



Malam Maude kenan mijin Hinde daya gaji al'adu tun iyaye da kakanninsa, dan kuwa da ana sayar da al'adu wurinsa za aje, mutum ne shi mai tsattsauran ra'ayi, gashi kuma ba shi da ilimin addini mai zurfi.



Bayan ya gama fadan sa yayi daidai da idar da addu'o'i da Hinde take yi nan ta fara bashi amsa cikin hikima da wayewa irin ta addini....




Haba Malam bai kamata ace har yanzu ka kasa sakin wannan ra'ayin naka ba na kimai kace iyaye da kakanni, shifa addinin Allah ba ruwan sa da wani gargajiya ko rashin ta, amma har yanzu ka kasa fahimta ta.



Ke rufa min baki, nawa kike da har kika San me duniyar ta 'kunsa, ku da baku riski al'adun mu ba masu daraja, yana fadi yana huci.



Hinde ce ta katse shi da cewa " yi hakuri Malam, ba wai ina nufin al'adun Ku basu da kyau ba a a kawai dai akwai inda ya dace ace basuyi tasiri ba musanman akan addini.


Ka Sani cewa acikin hadisan Manzon Allah akwai wanda yai mana nuni da zuwa masallaci amma mu suturce jikin mu kar muyi fita irin ta jahilci


Kuma ita sallah da kake fadin in barta ta nuna idan kuma na mutu kuma kafin lokacin fa.



Nan fa yay karaf yana fadin haba Hinde ke kullum baki da magana saita mutuwa, bari inje wurin ja'e in dawo kafin maraice, kiyi maza ki kwa'da min ya'diyar ina nan dawowa, ya shuri takalmansa yai gaba.


Dariya Hinde tasa Dan tasan cewa Malam Maude baya son zancen mutuwa.

Nan ta tashi ta fara kokarin hada masa ya'diyar sa kafin ya dawo.




Shin ya Malama Ramatu zasu k'are da Badaru a asibiti?



*Ummu Rahma ce ✍🏻*
[4/10, 7:57 PM] ‪+234 803 509 6818‬: *👳🏼👳🏼'DAN GARGAJIYA👳🏼👳🏼*


*(gargajiya ba addini bane)*



*Na*


*Ummu Rahma* ✍🏻



*Gajeren labari mai dauke da nishadi, gidadanci da rashin wayewa ta addini*



*10⚜15*




Tsaye Badaru yake yana nazarin kalaman Malama Ramatu tare da jiran ta ta fito dan su 'karkare.



Yana cikin tunanin yaji muryar ta ta dawo tana masa sallama, yayi mamakin haka duba da yanda suka rabu, abinda bai sani ba shine shi Malama Ramatu tana da saukin hali ga fahimta mai zurfi irin ta addini domin ya cancanci ayi masa sallama kasancewarsa musulmi.



Amma a wannan karon bata dawo a hasale ba, nan ta fara masa da nasiha tana cewa " baka kyauta ba bawan Allah, ya sunan naka" jikinsa ne yayi sanyi yace sunana Badaru.



Haba Badaru gaka a haka dai anga kamili mai nutsuwa amma kuma ka dauki wata dabi'a ka sawa kanka, duba ka gani nan duk mutane ne kowa da abinda yake fadi a kanka na
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download 'DAN GARGAJIYA

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album