Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

IGIYAR ZATO Complete Hausa Novel Document by IGIYAR ZATO


IGIYAR ZATO

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 155608



IGIYAR ZATO

Reading Time: 12 Hours

Added On: 06, Feb 2025

Author: Miss Xoxo ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Zafafa Biyar

Author Phone : 08095215215, +234 903 234 5899

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 865.48 kb

File Type: txt

Views: 153+

Download: 601+

Last download: less than 1 second ago

Description/Story: *_IGIYAR ZATO_..........💕_*


_*NA_***


_*NANA HAFSAT_*
_*(MISS XOXO🧕🏼)_*


_®️ZAFAFA2020_*
_(SABON TAKU)_


[1:1] بسم الله الرحمن الرحيم


In the name of Allah, the Gracious, the Merciful.💕


SADAUKAR WA GA: BITTI HABIBTY💚(FEEDHOM)💋❤️

TUKWICI GA: DAUGHTER❤️(BILLY S FARI)💕

ALKALAMI TV;
(A shiga domin sauraron shrye-shiryen mu)
https://youtu.be/Zyl7_eSgXuo


_*SHAFI NA DAYA_*


*ZARIA*


*2004*

Zaune nake a ‘dan tsukukun gefan kofar dakin mu. Gaba na kuwa wani tsohon kwano ne dake ‘dauke da sandararren tuwon dawa da miyar kuka koriya shar da ita, ina ci ina korawa da ruwan bunu marar sukari, can gefe na kuwa su Alawiyya ne da Hinde sun barbaje suna afka lomar taliya yar mirji data sha manja sun yayyan ka tumatir da albasa a akai. Kuka na na hadiye ina ko’karin ‘karasa cin tuwon gaba na don sauri nake yi zan kai wa yayan mu abinci dake can tsallaken gaban gidan mu can yake bakanikan ci. Fitowar babar su Alawiyya ne yasanya ni hanzarin mikewa, Na dauke kwanon gaba na, Ai kuwa muna hada idanu ta zabga min harara wadda tazame mata jiki kullum sai ta min.

“Mayya! Aniyar ki ta biki. Kurwar mu kur wallahi, anyi gado awajen uwa. Da shegen idanu kamar na ungulu..”

Nai shigewa ta d’aki, Na baro Babar su Alawiyya wacce ake kira da Bintalo tana zuba min kwandon zagi. Na danne bacin rai na na dubi Innar mu dake tsintar hatsi a tire nace,

“Innaar mu bari naje na kai wa yaya abincin sa..”

Na karasa magana, hade da d’aukar wata fashasshiyar kular abincin mu wadda itace me kyau acikin kwanukan mu da ake zubawa yayanmu abinci. Innar mu tayi murmushi tana gyarawa autar mu kwanciya dake baccin ta hankali kwance, gefan zaninta ta sunce ta ciro naira hamsin wadda itace dama a kullin zanin duk ta kanannade ta mikomin,

“Ungo ki taho da man gyadan ashirin sai yajin goma, ki biya ta gurin ladiyo mai koko ki sayo koko da kosai na ashirin.”

Rissinawa nayi hannu biyu na karb’i kudin, idanuwa na suka kawo ruwa cikin tsantsar tausayi nace,

“Innar mu to ke mezaki ci? Kinbar mana tuwon ni da yaya Najib, koko da kosan kuma na Aminatu ne.”

“Banasan sakarci sanda naci abincin idanuwan ki biyu?”

Girgiza kai nayi alamun a’a. Kafin na janyo kodadden koren hijabi na daya zama tamkar na gado na zura shi cike da tausayin innar mu, Uwa kenan gwara muci ita ta zauna da yunwa har sai mun gama sanwar rana. Sallama nayi mata na fito kai na a kasa na wuce ta gaban bintalo ai kuwa ban gama maganar ta a zuci ba ta zubamin rankwashi ji kake .’kwas’.

Su Alawiyya da Hindatu suka tuntsire da dariya suna gasamin magana, share hawaye na nayi, domin inda sabo na saba da irin rayuwar gidan mu. Dakyar na karasa sauka daga benen gidan mu mune a saman karshe mu dasu Bintalo da Usaiba maman su Larai, wato dakuna na uku acikin d’akuna tara dake gidan. Domin kaf layinmu da unguwoyin gaban mu babu wanda bai san gidan mu ba, wanda akewa laqabi da ‘Gidan Mata Tara’.

*HAYIN RIGASA MECHANICS*

Ina tafe a hanya ina bitar haddar Suratul Yasin da za’a karba anjima a islamiyyar mu. Sauri nake yi na ‘karasa na kai wa yaya abincin sa. Cikin nutsuwa na ‘karasa wurin aikin su. Na gaggayshe da abokanan aikin su kafin na wuce wajen daya ke zama. Can ‘karkashin wata mota na hango shi yana gyara notinan taya. Yayi dumu dumu da bakin man fetur. Cike da murmushi na ‘karasa wajen sa. Cikin nutsuwa da girmamawa na dan durkusar da kaina yadda zai iya jiwo murya ta nace,

“Yayan mu! Sannu da aiki. Ga abincin ka.”

“Na’am Batoul! Sannun mu! Ya innar mu da auta?”

“Lapia lou Yayan mu. Bari naje nayo cefane.”

Ina gama fada na mike daga tsugunnan da nake, Yaya ya zura hannu a aljihu yana lalibo kudi. Nera sittin ya ciro duk sun dunkule da junan ya miko min naira arba’in ya maida ashirin din cikin aljihun sa. Na danne kukan daya tahomin ina kokarin mayar da kai na gefe dan kada Yayanmu ya gano yanayi na.

“Yayanmu ALLAH ya kara bud’i. Me zan siyo aciki?”

“Jia kin tambayeni kudin Omo ko? To kiciri goma ki sayo omon. Naira talatin din sai ki sayo abunda babu a gidan.”

Gyad’a kai nayi, Ina tunanin abunda babu,

“Shikenan zan sayo maggi mai tauraro na goma sai albasa da tumatir na sauran ashirin din. Nagode Allah ya saka da alkhairi ya ‘kara bud’i. Na tafi Yaya sai ka dawo.”

Sallama mukai dashi alokacin yana kokarin bude kular ‘dumamen tuwon jia dana kawo masa. Allah sarki Yayan mu bai ci komai ba ya fita daga gida tun asubah. Hanyar ‘karamar kasuwar sayar da kayan masarufin unguwar mu na nufa. Nan na hadu da Fadila babbar ‘kawata tana sauri itama da alama cefanon zata yo. Dan ‘daga murya nai yadda zata iya jiyo ni na shiga rafka mata kira ina hadawa da sassarfa don cinmata,

“Fadilah! Fadila!..!”

Juyowa tayi da sauri tana kallo na, fuskar ta dauke da murmushi. K’arasawa nayi ina haki. Ta dan dafa ni tana bubbuga bayana,

“Sannu tawaje na, daga ina kike?”

“Wallahi daga gida amman na biya na kaiwa Yayan mu abincin sa.”

Murmushi tayi hade da sakalo hannuwan ta ta wuyana muka ci gaba da tafiya a haka, Har muka karasa wajen Falalu mai kayan miya. Mutum hudu ne a gaban mu. Dan haka muka koma daga gefe muna hira. Fadila ta sauke nannauyar ajiyar zucia tana yar carafke da duwatsun hannun ta,

“Tawaje na nakasa cire Yaya Najib a rai na”

Na muskuta kusa da ita ina mai kallon kwayar idanun ta dake fitar da hawaye, Na kasa gane wane irin so takeyiwa Yayan mu, gashi a gidan su an hanata kula shi ko nace Umman su ta hane ta da kula Yayan mu saboda su sunada rufin asiri mu kuma talakawa ne wanda bamuda tabbacin cin yau ko na gobe. Mahaifiyar ta irin iyayen nanne masu son ‘yayan su su shiga babban gidah. Gashi Yayan namu a babban ajin sakandire na biyu yake ko ‘karewa bai yi ba, ya dena zuwa ya koma sana’ar kanikanci (mechanics) ta haka yake d’auke mana wasu hidindimun na gidah dana makaranta duk kuwa da ta gwamnati muke yi. Ajiyar zuciar nima na sauke, cikin bata baki da kwantar mata da hankali nace,

“K’awata kenan, dan Allah ki ‘kara hak’uri ki fawwalawa ALLAH lamurran ki, na rantse maki da ALLAH idan har Yayan mu mijin ki ne to babu shakka sai anyi auren ku. Sannan ki sani Yayan mu fa har yanzu kinga ba gama makaranta yayi ba ko ince ya dakatar da zuwa makaranta saboda muna cikin halin rashi. Muma kuma duka duka yanzu muke a karamin aji na biyu. Kinga kuwa akwai sauran lokaci, Saura aji hudu mu gama makaranta muma. Kuma ma ai shekarun mu bana zamu cika sha hurhudu fa (14). Dan dai ma kece kawai kina son sa ne amman naga shekaru hudu fa ya bamu...”

Nagama fada Ina murmushi, Fadila ta rafka min hararar wasa tana tsuke baki hade da sakin tsaki,

“Wai an gaya miki kowa irin ak’idarsa ce da ke? Ke wannan yadama amman ni gaskia inason Yaya Najib kuma zan iya salwantar da komai don zama mallakin sa.”

Tabe baki nayi ina sake cuno shi gaba, narasa meyasa take son Yaya Najib, ko yaushe tasan so oho? Kuma ma dai ni abokan Yayan mu wallahi kallon yara nake musu. Ina cikin zancen zuci ashe har layi yazo kanmu. Fadila ta mike ta sayo kayan miyan sai gani nai ta miko min bakar leda cike da kayan miya, Na bita da kallon ‘karin bayani. Duk kuwa da nasan hakan ba farau bane awajen mu. Amman gaskia ni kunya nake ji duk sanda tayi haka duk kuwa da nasan tasan mu ba masu hali bane.

“Dalla tashi mu tafi, kin ‘kuramin idanuwan ki irin na Ashwariyya rai!”

Daria nayi, domin duk sanda ta tanka idona da irin na Ashwariyya abun daria yake bani. Domin nasan ni dai ba jinsin indiyawa bace amman sosai mutane kemin kallon ruwa biyu ce ni. Saboda kyau da tsarin halitta da ALLAH yayoni dashi, wanda kwata kwata nafi yan gidan mu da yan d’akin mu kyau. A takai ce dai kamanni na daban. Na kan sha kuka na a duk sanda Bintalo ko sauran matan gidan mu suka tasani a gaba suna zagi na da aibata ni, koda yake wasunsu a gurin mazajen su suke jin cewar wai ni ba ‘yar baban mu bace, Ni shegiya ce. Nima nakan zauna wani sa’in na tambayi kai na ya akai na fita zakka a gidan mu? Amma kuma me? Ai ALLAH shine mamallakin kowa da komai, a haka ya yoni badan ya tsane ni ba. Cikin
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download IGIYAR ZATO

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album