Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

A JINI TAKE (IZZATA) CHAPTER 2 Complete Hausa Novel Document by A JINI TAKE (IZZATA) CHAPTER 2


A JINI TAKE (IZZATA) CHAPTER 2

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 206022



A JINI TAKE (IZZATA) CHAPTER 2

Reading Time: 17 Hours

Added On: 30, Jun 2024

Author: Mhiz Innocent ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : 08124818273

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 1004.97 kb

File Type: txt

Views: 960+

Download: 3680+

Last download: 11 hours ago

Description/Story: ✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO23*


.. Cakk Abba ya ɗauketa a hannunsa, ya soma takawa zuwa cikin ɗakin Ammi. Be ajjeta ba, se da ya ƙarasa kan gadon ya ajjeta. Juyawa ya yi zuwa side fridge ɗin Ammin dake gefe, ya saka hannu ya buɗe ya ɗauko ruwa me ɗan sanyi sannan ya matsa kusa da Lulun. Ɗan zubawa ya yi a hannunsa kafin ya kai kan fuskarta a hankali ya shafa, ba ta motsa ba, kamar wadda ba a shafawa komai ba. Ƙirjin Ammi ya sake bugawa, se ta ƙarasa hawa kan gadon, ta ɗauki kan Lulu ta ɗora a kan cinyarta, daidai lokacin da Abba ya sake kai ruwan fuskarta a karo na biyu. Ƙatuwar ajiyar zuciya ta sauke sannan ta soma buɗe jiƙaƙƙun idanunta. A kan Abba idanunta suka fara sauka, Abba ya lumshe idanu yana sauke ajiyar zuciya lokaci ɗaya yana furta

"Alhamdulillah.." Daga haka se kawai ya miƙe ya fice daga ɗakin, dan tun yanzu zuciyarsa na neman karyewa a kan 'ya'yan nasa, ba kuma ya so ya cigaba da zama anan ɗin har hakan ya janyo ya fara tunanin ya aikata ba daidai ba. Tsam Ammi ta rungumeta cikin jikinta cikin matuƙar farin ciki mara misaltuwa. Didi ma kasa sukuni ta yi se da ta ƙarasa ta rungume su. Ammi ta haɗa 'ya'yan nata waje ɗaya ta rungume. Se a lokacin Lulu ta sake tuna abin da ya faru ɗazun, zuciyarta ta buga da ƙarfin gaske, se ta ɗago da sauri muryarta na sake yin rawa fiye da yadda take, wata ƙwalla kwance a cikin kyakykyawar ƙwayar idanunta. Hannunta na wani irin rawa tace bayan ta tashi daga jikin Ammi

"Ammi mafarki na yi koh? Ammi wani mummunan mafarki na yi koh? Ammi don Allah ki ce min mafarki ne wannan ɗin ba gaske ba. Don Allah Ammi kin ji.." ta ƙarashe tana girgiza kai, gami da fashewa da wani sabon kuka. Janta Ammi ta sake yi cikin jikinta, itama tana jin wata sabuwar ƙwalla na taho mata.

"Ki yi haƙuri Afaaf.. ki dena wannan kukan, babu abin da ze ja miki se ciwon kai.."

"Ammi ba ki ce min ehh ba. Ammi ba ki faɗa min ba gaskiya bane. Wannan wane irin mafarki ne? Wannan wane irin mummunan mafarki ne? Ta yaya ma wannan abin ze yiwu? Ammi sake ni na je wajen Abba ya tabbatar min da wasa yake mana. Ammi wallahi har abada ba zan sake wani laifi a makaranta ba. Ammi na dena wallahi. Na dena bazan sake ba. Na san abin da Abba ke buƙatar ji kenan daga bakina, kuma gashi na faɗa. Don Allah Ammi ki sanar da shi na dena, wallahi na tuba na bi Allah.." yanzun ma ƙarasawa ta yi tana sakin kuka. Gaba ɗaya Didi se ta ji kamar ita ba a faɗa mata an ɗaura mata aure da wani ba, gaba ɗaya se ta ji kamar bata da wata damuwa idan banda ta er uwarta. Yanayin da take ganinta a ciki a yanzun ya danne komai. Wannan kukan da take ta yi ita kanta shi ke ɗaga mata hankali, gashi se magana take kamar wadda bata a hayyacinta.

"Ya isa haka.. Ki yi shiru nace koh?" Ammi ta faɗa tana goge idanunta. Ba dan taso ba haka ta haƙura ta cigaba da zama a jikin Ammin. Tun tana kukan a fili har tazo ta gaji ta koma sheshsheƙa har daga ƙarshe baccin wahala ya kwasheta. Se a lokacin Ammi ta sauke ajiyar zuciya, ta ɗaga kai ta kalli Didi dake zaune kusa da ita. Idanunta duk sun yi face_face da hawaye, gaba ɗaya kamar ba Didin ba, se ta miƙa mata hannu, babu ɓata lokaci ta ƙarasa Ammin ta haɗasu ta rungume. Se a lokacin ta samu damar fashewa da kuka gwanin ban tausayi.

"Kema karya min zuciyar za ki yi Afrah?" Ammi ta faɗa a sanyaye. Girgiza kai Didi ta yi se dai ta kasa tsaida hawayen, da ƙyar ta iya buɗe baki tace

"Ammi Abba...!" Se kuma ta yi shiru, sannan ta ɗora da

"Ammi ban san wanda Abba ya aura min ba.. Abba be faɗa min ba Ammi.." Ɗan runtse idanunta Ammi ta yi, kafin a hankali ta ɗora hannunta a kan Didi tace

"Ina saka ran samun sassauci daga gare ki Didi. Don Allah ko wane ne Abbanku ya aura miki ki yi haƙuri, ba ze taɓa zaɓa muku abin da ze ce cuceku ba. Idan har kika damu, toh shi kenan Afaaf kuma ta samu dama. Kin ga kenan ta duka ɓangarori biyun Abba ze yi nadamar abin da ya yi, bayan kuma hakan ba laifi bane. Idan kuwa kika haƙura, ke zaki ɗora er uwakki a kan hanya, kamar yanda kika saba. Dan haka ki dena kukan nan, kin san dai yanzun nan kanki ze soma ciwo.." Ammi ta ƙarasa maganar cikin rarrashi. Ba ta iya cewa komai ba, illa zuciyarta da ta cigaba da bugawa. Ta yi shiru tana tunanin yadda rayuwarsu ta gaba zata fara. Aure a ƙananun shekaru irin nasu, da kuma mijin da basu sani ba, baya sonsu basa son shi.

"Allah ze kawo mana mafita.." Ammi ta faɗa kamar ta san abin da Didin ke tunani.


... "Ina ɗana yake Yallaɓai? Me ya same shi haka? Ya ka yi aka kawo shi wannan asibitin?" Mom ta yi duka waɗannan tambayoyin a lokaci guda. Ajiyar zuciya Daddy ya sauke kafin yace

"Duka waɗannan tambayoyin a lokaci ɗaya?" Daddy ya faɗa yana kallanta.

"Don Allah so nake na ga ɗana, yana ina?"

"Mu je.." Daddy ya faɗa yana yin gaba. Babu ɓata lokaci Mom ta bi bayansa hankali tashe, burinta kawai ta ga shalelenta ta kuma san abin da ke damunsa.

"My boy.." ta faɗa tana kai hannunta kan fuskar Bad ɗin dake kwance har lokacin kamar matacce. Ganin da ta yi be motsa ba ya sanyata kallan Daddy tace

"Bacci yake yi ne? Wai me ya same shi?"

"Ki kwantar da hankalinki. Ze farka zuwa anjima In Sha Allah."

"Har yanzu ba ka faɗa min abin da ya same shi ba Yallaɓai.." Kafin Daddyn yace komai, likita ya shigo cikin ɗakin. Bayan sun gaisa da Daddy cikin girmamawa sannan ya ƙarasa inda Bad ke kwance, ya duba shi sosai sannan ya kalli Daddy har lau dai cike da girmamawa yace

"Har yanzu be motsa ba?"

"Ehh.." in ji Daddy.

"Ohk a cigaba da addu'a. Kamar dai yadda muka faɗa zuwa anjima In Sha Allah ze farka.."

"Allah ya yadda.."

"Likita me ke damun ɗana?" Mom ta faɗa tana kallan Doctor ɗin. Kallanta Daddy ya yi, kafin ya maida dubansa kan Doctor ɗin yace

"Za ka iya wucewa.."

"Ohk Sir.." Daga haka ya fice daga ɗakin.

"Abin da yafi dacewa ki zauna ki masa addu'a ya samu ya farka, ba tambaye tambaye ba.." Daddy ya faɗa yana kallan Mom.

"Wai abun har ya kai haka?" Mom ta faɗa a sanyaye.

"Kar ki ɗaga hankalinki.." Se ta sauke ajiyar zuciya tunda dai ta ga ba faɗa mata za a yi ba, se ta nemi waje ta zauna kawai tana kallan ɗan nata cike da tausayawa.


... "Sannu da zuwa.." Ummeey ta faɗa tana kallan Abeey.

"Yawwah.." ya yi maganar yana neman waje ya zauna. Murmushi Abeey ya yi kafin yace

"Na san kin ƙagu ne ki ji abin da zan faɗa.." Ɗan yaƙe ta yi tace

"Ƙwarai kuwa Malam.. Ka fita kai ba cikakkiyar lafiya ba.. ga kuma wannan zancen da yafi kama da almara.."

"Kwantar da hankalinki.. Ni kam garau nake jina musamman ma da yau ɗaya daga cikin burina ya cika. Wato na aurar da Affan.." Cike da mamakin dai Ummeey tace

"Wai Malam dama da gasken ne?" Girgiza kai Abeey ya yi kafin yace

"Ban da abinki, wannan ɗin ai ba maganar da za a yi wasa a kanta bace. Da gaske a yau ɗin na aurar da shi. Kin ga kema burinki ya cika, ko dama ba abin da kike so ba kenan?" Ya tambaya yana kallanta.

"Ikon Allah.." Ummeey ta faɗa cike da mamaki. Se kuma ta ɗora da

"Toh Alhamdulillah.. Allah ya sanya alkhairi.. ya basu zaman lafiya.. ya haɗa kansu. Ni kuma ina nan ina jiran zuwan sirikata.." ta ƙarashe tana murmushi. Murmushi Abeey ya yi yace

"Ameen Ameen.."

"Amma Malam.. kana ganin Affan ze iya riƙe mata kuwa? Duk uban hidindimun nan na aure da ake yi.. abubuwan kamar da yawa, kuma na san dai mutane ba zasu ɗauki ɗiyarsu su bamu ba tare da an gabatar da abubuwa na al'ada ba.."

"Haka ne.." Abeey ya faɗa bayan ya sauke ajiyar zuciya. Se kuma ya ɗora da

"Allah ze hore yadda za a yi In Sha Allah.."

"Toh Allah ya yadda.."

"Ameen.." Abeey ya amsa kafin yace

"Har yanzu be shigo ba?"

"Wallahi kuwa.. dama yace ze daɗe.." Ummeey ta bashi amsa.

"Ko yaushe ya dawo, ki faɗa masa ina son ganinsa ko da bana nan.."

"Toh Malam.."




... Kamar a mafarki ta ji tarinsa ƙasa_ƙasa. Da sauri ta
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download A JINI TAKE (IZZATA) CHAPTER 2

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album