Join Our WhatsApp Group

TARKO Complete Hausa Novel Document by TARKO


TARKO

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 166740



TARKO

Reading Time: 13 Hours

Added On: 29, Sep 2023

Author: Zainab Idris Makawa ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 876.16 kb

File Type: txt

Views: 1757+

Download: 2146+

Last download: 13 minutes ago

Description/Story: 🕸🕸TARKO🕸🕸
🕸🕸🕸🕸🕸🕸
1⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAURI


Da sunan Allah mai,rahama mai jin kyai, duk kan godiya da yabo ya tabbata a gare shi, wanda ya yi mu ya wadata mu da ni,imomin sa,
Wanda ya shari,anta yin addu,a zuwa gare sa, ,kuma yai muna ni,ima da baiwan shi, akan mu roke shi duk bukatocin mu,,
Ubangijin,mu wanda ya ce idan su ka tambaya a gamay da ni,
To ka basu labarin cewa ni din makusancin ne a gare su,
Ina karba adduan mai addu,ar mai, addu,a idan ya roke ni,
Ya Allah tsira da amincin ka su tabbata ga fiyayyen talikai,
Annabi rahama Muhammad S A W, da halaiyen sa da sahabban sa da ma duk wani musulmi wanda yabi tafarkin gaskiya har izuwa ranan Alkiyama,,,,,,,
Ya Allah ina rokon ka da da gode maka da ka bani wanan daman na rubuta wanan dan gajeren labari,
Ya Allah yadda ka nufeni da farawa lafiya Allah ka bani ikon kammalashi lafiya,
Ya Allah dani da na rubuta da wanda duk kabawa ikon karantawa, Allah ka yafe muna kurakuren mu,
Allah ka sada mu da rahamomin ka da ni,imomin ka ,
Ya Allah kasa Aljannan fiddausi tazamo makomar mu,,,,,,,,,

BARKAN MU DA SALLAH YAN UWA,,,,,,

A hankali ya sa hannun shi saman kan shi ya cire farin rawanin dake saye a kan shi,
Farin rawanin da a kasar hausawa sai wani mai, sarauta ko malami ko wani babban mutum ke sawa kan su shi,
Gefen guda daga inda yake zaune saman shimfidar dake a cikin rufan da ke kofar gidan shi,
Rumfar wanda ya a kayi manne da ginar zauren gidan, a ta gefe guda,
Sai shimfidar da akayi wa wani gadon kara dake a cikin rufar,
Shimfidar ya sha kayan laushi irin daddumar nan na da ja,jayen kala,
Daga gefe guda littatafan addini ne kala kala tare a guri guda,
Sai kuma wasu allunan katako, dake tare a guri guda,
Wanan abubuwan zai nuna wa mutum cewa runfar na wani malamin irin kasar hausa ne,
A hankali dan tsohon ya dan jawo jikin shi daga saman shimfidar da yake a zaune,
Gurin da wata butar silver mai ruwan gold yake a je da ruwa ya nufa, a hankali ya fara gabatar da alwala a tsanake, kamar yadda addini ya umur ta,
Bayan ya gama alwal ne ya kara gunda ruwa ga baki yayin da yake mikewa tsaye ya zubar a saman bangon shiga cikin gidan shi
A hankali ya ke dan takawa zuwa kofar fita cikin rumfar tashi,
Jama,a ne a,waje da alamar shi suke jira, daman yafito gaba dayan su , suka mike tsaye,
Bata lokaci aka fara gabatar da sallah azahar na ranan,
Bayan idar da sallah tsohon yadan kai wani lokaci a gurin zaune yana tasbihi,
Duk wanan jimawan da yayi a zaune bai hana mutane zanan jiran fitowar shi ba,
Ya fito fuskan shi dauke da annuri mai kama da murmushi a koda yaushe,
Yara ne daga gefe guda suna ta taruwa da alama karatu zasu yi a gurin,
Saboda irin yadda suke ta tururuwan fitowa daga cikin gidan,
Hakan ya nuna cewa gidan na malam Manya, babba gida ne mai tarin jama,a acikin sa,,

Tarin wanke wanke ne a gefe guda kuda na bin su,
Daidai lokacin da wata mata yar kimanin shekaru, hamsin da tafi daga dakin ta, tana kokarin gyara daurin zanin ta,
Gani kwanonin da ba,a wanke ba har izuwa yanzu yasa matar sake wani irin wawan tsuki, a lokaci guda ,,,
Takalman silifas din ta dake a kofan dakin ta take kokari zurawa kafan ta sai faman mita takeyi, tana cewa ace izuwa yanzu ba,a wanke kwanonin da akaci abinci a cikin sa ba,,,
Amma yau idan na kama wanan Yarinyan sai rayuwar ta ya baci,

Cikin gidan babbane mai sassa guda dai,dai har goma sha, biyar, duk sassan gidan na 'ya'yan malam Manya ne, sai mutum uku ne kawai diyan yan uwan shi da ya karantar kuma yai masu aure suna zaune a tare dashi,
Duk diyan malam suna da aure sai mutum guda wanda shine autan malam wanda ake cewa Isah,
Amma Abdullahi ya bace wada suke kiran shi, da shi saboda acewar mahaifiyar shi tun haihuwar shi da tasamu kudin suna ta, sai dabbobi tana kiwo shine suke ta kawo mata kudi,
Mahaifiyar Audi, itace matar malam na karshe wacce daga ita bai kara wani aure ba,,

Dan malam na farko shine baba Buhari, sai na biyu Sha,ibu, sai Musa, sai Gwago, Laira, gwago Lanto, sai Hamza,, Yahaya, duk diyan mace guda ne,
Ismail, shi da Habiba uwar daya amma ta rasu dadewa, tun gurin wani haihuwa,
Asiya, Rabi, da Audi su kuma diyan mama Rukaiyya ce Amaryam malam, ta yanzu,
Wanan babban gidan na malam manya, yana nan a cikin uguwar da ake kira da Shiyan Sarakuna, dake a cikin garin Birnin Kebbi,
Wanan shiyan kowa yasan cewa shiya ce ta haifaffun gari da kuma baki masu asali, ke zama gurin,
Yanzu haka, zaka samu mazauna unguwar duk kowa yasan kowane gasu da yawan ilimin addini tare da na zamani,
A tsakiyar unguwan zaka samu gidan malam Manya, wanda shi da daukacin iyalin shi suke a ciki,,
Babban diyarn Buhari mariya, sai, Abubakar wanda ya ke bi matan sai mata ne har su biyu, su ke bi mashi, sai daga baya mahaifiyar tasu ta samu maza,biyu da mata biyu,,,
Don haka yaranta sune manya a gidan gaba dayan, saboda, a kusan jere tai ta haihuwan ta,
Ba karamin kokari malam Manya keyi ba gurin ganin cewa hankalin iyalin shi, ya zamo guri guda,
Amma duk da haka akwai, baraka a tsakanin matan wanan babban gidan don sun kashi kashi dakashi a tsakanin su,,,,,
Yanzu haka ita matar malam wace a,ke,cewa maman Audi,
Kansu a hade yake da Amaryan malam watau maman Audi,
Wanda hakan ya samu asaline don kusan a lokacin da malam ya auro ta ita mahaifiyar su Audi,,,,
A tare suke hurda da mama Ladi, wace da ma bata kaunar zama da mahaifiyar mijin ta,
Hakan yasa da malam ya auro maman Audi, sai Ladi ta jata a jiki,
Shiko Ismail da kaunar shi wace da mahaifiyar su bata da rai, a gidan sai aka ware su,
Hakan ya sa Shi Ismail yake da kwazo da neman na kan shi,
A can cikin dangin mahaifiyar su gwandu ya auro matar shi,
Wace take zaman hakkuri a gidan tare da yaran ta,
Sai dai sauran matan yan uwan Buhari sam basu yarda, da wulakancin mama Ladi ba sam, saboda suna ganin cewa bata fisu ba,
Ya sa sam ba su yarda da da wanan cin fuskan da,takewa sauran matan gidan,

Sashin mata daban a makarantan sashin maza da ban
Matan suna zaune kusa da kakan su inda suke daukan karatu,
Malam baya yarda yarinya ta girma batare da ta sauke alkur,ani maigirma ba,
Don duk wace zaiwa aure a gidan dole sai ya kasan ce ta sauke littafi mai tsarki,
Don haka komai kankantar yarinya dole tana zama da zaran lokacin karatu yayi don gudun makara saboda bulalan da malam ke dan shada masu a hannun su idan sunzo a lati,,,
Sauri takeyi don gudun makara don tasan cewa malam yanzu ya fito daga cikin massalaci,
Saboda agogon bango dake sagale dakin mahaifiyar ta ya nuna mata cewa, biyu da minti talatin daidai,
A cikin saurin da ta keyi ne suka hade hanya da mama Ladi wace ta zo sa shen nasu don neman Meenat din
Meena wace ganin mama ladi yasa gaban ta faduwa don tasan cewa ko banza sai kunuwar ta yasha murda gurin mama,
Da sauri Meena ta ja baya daidai inda mama ta kai mata bugu ta gwauce,
Gaba ta sata da masifa inda dole ta aje Alon ta zuwa sashen mama ladin,
Sai da ta wanke kwanonin tas sanan ta, dauki allon ta zuwa kofan gida,
Tun fitowar ta hankalin malam Manya, yake a kan yariyar wace, ke ta dan sharan kwalla, da habar hijabin ta,
Malam,Yasan duk abinda ke gudana agidan
Amma hali irin na manya yasa shi, kawar da kai tankar bai san may ke gudana ba,
Azaton Meena malam zai mata bulala yau sosai saboda irin makaran da tayi, ga kuma sauran yan uwan ta duk sun zuro mata ido suga yaya zasu kwashe ita, da malam,
Sai dai tana zuwa sai malam ya nuna mata, gurin, da zata zauna a hankali ta zauna a tsorace don gudun kada ya fyedo mata bulala daga inda yake zaune a gefen su,
Da guda guda su kai ta zuwa gaban shi suna biya allon su,
Meenat tana isowa agaban malam, maimakon ya fara biya mata sai yace mata cikin tausa murya Amina ki dinga kula daga yau da duk wani aikin da za,a saki, a gida bana son kina makara haka don gudun kar a barki a baya,,,
Kai kawai ta gyada mai don a zaton ta har yanzu zai mata bulala da ta makara,
Amma har aka tashi, bai mata bulalan ba, hakan yasa ta sakin jikin ta,
Ba komai asa Meena take tsoron bulalan malam don ganin irin yadda bai kaunar dukan ta duk cikin su,,,
Hakan yasa Meena ke jin nauyin ace, tana cikin masu makara,
Dawowan ta sashen su, ta yi dakin mahaifiyar ta inda ta samu mahaiyar ta na gyara dakin ta don ganin yamma ya gabato,
Hijabin ta ta cire tana kokarin karban tsintsiyar dake a hannun mahaifiyar ta,
Jeki ki duba kigani idan da, sauran aikin da zakiyi, wa maman ku ki karasa mata, kafin dare yayi,
Cikin sanyi jiki Meena ta bar sashen nasu zuwa,,, gurin ina ladi don ta share mata guri,
Kamar yadda ta saba yi mata akoda yaushe, don dama takamar maman ladi shine taita bautar da yar mutane saboda mugun kiyayyan da takewa Meena din haushin uwar ta take ji,,,,,,,


A yi hakkuri da wanan yan uwa barkan mu da sallah,
Allah yasa wanan novel din ya samu karbu gurin fadakar da ku kamar kullun,
Taku ZAINAB MAKAWA,,,,,,,,,,,,,,,,,,,
🕸🕸TARKO🕸🕸
🕸🕸🕸🕸🕸🕸
2⃣


ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAURI

SADAUKARWA
Na, Sadaukar da wanan littafin ga Anty na yayana kuma masoyiyata Antyna Nafisa Harzami tare da duk sauran yan uwan mu maza da mata yan Harzami Family,,,,,,

JINJINA
Jin,jina gare ki MAMAN FARIDA

TUKUICI
Wanan littafin tukuici gareki Anty SAFEENA MAMUD, MAIDUGURI,,,,,

FATAN ALHERI GAREKU DUK KA MASOYANA MASOYA NOVEL DIN ZEE MAKAWA,,,

YA ALLAH Kabani ikon gama wanan littafin lafiya kare ni, da ga rubuta duk wani abin da bai dace aciki ba,,,,



A karkashin babban itaciyar cediyar da ke a tsakan gidan gurin da matan gidan ke taruwa suyi hira, daka da sauran yan aikace, aikacen su,
Yau ma zaune akasarin matan gidan suke a guri itacen
Wasu na yan aiyukan su wasu kuma suna hira ne kawai saboda basu da aikin yi a lokacin,
Mama ladi ce tafi don rakiyar kawar ta aminiyar ta kuma uwar matar da ta zabawa Abubakar din ta,
Kusan matan gidan dake guri alokacin duk sun, wa hajja, sallama,
Sai dai kusan duk idon matan akansu yake tun dai irin yadda suka ga mama ladi na washe baki don ganin Aminiyar nata,
Daga cikin mata ukun dake zaune, suna hira duk suka bisu da kallo a lokacin da suka bada baya,
Matar shaibu ce tace ni dai sam wanan matar bata kwanta min a zuciya na ba, wallahi,
Sai dayar matar da suke a zaune tace ,"ke ki iya bakin ki da wanan zancen,
Guda tace ke ina ruwan ki da zancen da bai shafe ki ba kina zaman ,zamanki ki jawa an kifitina,
Hakan bai sa Maimuna shiru ba har sai da takara cewa
Mata da wani iren fuska babu fara,a, walle, duk sanda nigga wagga mace hankali na tashi shi,kai,,,
Daga haka zancen nasu ya tsaya don ganin mama Ladi da sukayi ta juyo zuwa cikin gida,,,,

Abubakar ne zaune tare da malam a turakar shi suna hira, a washe garin da ya dawo daga karatun shi ,
Dama Abubakar sunan malam ne yaci don haka malam manya ke kiran shi da mai suna,,,
Mai suna inji malam
Yanzu kan Alhamdullahi ko?
Tunda guri ya cika ankamala wagga karatu gashi har ankai ga aiki yau,
Murmushi Abubakar yayi yadan sadan da kan shi kasa cikin girmamawa,
A cikin taushin murya yace wa malam din malam da taimakon Allah da naku ai wanan gurin nawa ya cika,
Nagode ma Allah da yanufe ni yau kana raye malam saboda irin yadda kai min tarbiya da kokari a cikin rayuwana,
Kudi ya ciro masu yawa daga cikin aljihun shi, ya a je su a,gaban malam din,
Ido malam ya dan tsurawa kudin da Abubakar ya aje a gaban shi,
Cikin tambaya yace kudin maye wanan kuma mai suna,
Abubakar yace kudin da akafara bani na albashina ne, shine nace barin kawo ma don asan yadda za,ayi da su,
Shiru malam yayi yana nazarin wani abu a cikin zuciyar shi,
Gyaran murya malam yayi da farko tare da gyara zaman shi kadan,
Mai suna inji malam Abubakar din yadan dago da kan shi kadan yana mai kallon malam,
Wanan kudin ka kasa shi kashi hudu,
Kashi biyu ka kwasa nakane,da sauri ya dago kai ya kalli malam don shi a ganin shi ai kudin sun mai yawa duka don ba wani abu yake saye ba ai,
Malam ya gyada kai yace kwarai kashi biyu kai zaka a je a gurin ka,
Kashi guda kabawa...


Read / Download TARKO

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

2 Comments On TARKO
avatar
maryam-2-4-2

7 months ago

Reply

Ya zanyi in karanta duka

avatar
maryam-2-4-2

7 months ago

Reply

Ya zanyi in karanta duka

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album