Join Our WhatsApp Group

A GIDAN HAYA Complete Hausa Novel Document by A GIDAN HAYA


A GIDAN HAYA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 50417



A GIDAN HAYA

Reading Time: 4 Hours

Added On: 19, Aug 2023

Author: Jameela Jameey ƴar mutan Kankia ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : MANAZARTA* *WRITERS ASSOCIATION

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Horror novels

File Size: 280.73 kb

File Type: txt

Views: 1215+

Download: 492+

Last download: 2 days ago

Description/Story: 🏭🏭🏭🏭🏭🏭🏭🏭
   A GIDAN HAYA
🏭🏭🏭🏭🏭🏭🏭🏭

_STORY AND WRITING_ _BY_
    _Jameelah jameey_
*Yar'mutan kankia ce ❣️*

*🌍MANAZARTA*
*WRITERS ASSOCIATION📚🖊*
      *M. W. A*

'''Kungiya d'aya tamkar da dubu.Masu Nazari da Aiki da Ilimi, Burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma Nishad'antar da masoyan ta.🤙🏻'''
https://www.facebook.com/107980080946102?referrer=whatsa
____________________________________

    
            

*BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM DASUNAN ALLAH ME RAHMA ME JINKAI INAFATAN ALLAH YA TEMAKENI YABANI IKON RUBUTA WANNAN LABARI DANA DAKKO BA AKAN WANI KO WATABA KAGAGGEN LABARINE INAFATAN ALLAH UBANGIJI YABANI IKON YINSA CIKIN AMINCI KUBIYONI DAN KUGA IRIN SALON DAYAZO DASHI*


'''NASADAUKAR DA WANNAN LITTAFIN GA NAMTARY UMMYN ABBA ALLAH YA JiKANKI YASA MUTUWA TAZAMO HUTU A GAREKI, ALLAH YABA8 MIJINKI DA YARANKI DA DUK WANNI MAKUSANTANKI HAKURI DA JURINYAR RASHINKI😭🙏🏻'''


Page 1-2



Yanzun ta samu ta gama azakar tana son ta koma baccin safe koda na minti goma ne, amman ina hayaniya mutanan gidan su ba zasu barta tayi wanann bacci ba gashi tana jin kanta nayi mata ciwo rabon ta da bacci tun jiya karfe ukun dare da ta tashi sallahr dare..

"Ohni Rumaisa, har sai yaushe mutanan gidan nan zasu san ba kyau shiga hakin mutum, mtsssss ina anfani ace gida baya yin shiru har sai in kowa ya kwanta sannan zaka ji gidan shiru, sai ka Aku haba, ni dai abun ya fara damuna wallahi."

"Aaha Rumaisa ke da wa Kuma,  naji kina ta maganganun? "Mama nida mutanan gidan nan mana, "To Rumaisa in ba hakuri mai za muyi, ai matsalar *GIDAN HAYA* kenan, yanzun fa fada ake da Lami da Halimai, wai Lami taga Halimai tana dibar mata abinci, Kuma ita abincin mijinta ta ajiye ma nashi,  kinji asalin fadan."

"Kai gaskiya Halimai bata da hali Mama,daga ita har mijinta, ni shiyasa bani son zaman tsakar  gidan nan, duk wata gulma daga jikinsu take fitowa, daga Halimain har ita Lami din, yau dai tasu ta hada su shiyasa aka jisu a cikin gidan nan."

"To ya zamu yi Rumaisa ai sai hakuri, shiyasa Babanki shima baya san yaga muna zama cikinsu, yace halinsu bai ye mashi ba."....cewa Rumaisa tayi."ai Mama basu da hali ko daya, sun sama kowa ido a gidan nan, bayan gidan nan gidan mutane ne, daki goma ne a cikin gidan Kuma kowane daki akwai Wanda suke zaune cikin su, ai dole ko wace gulma a unguwar nan ta fito daga gidan nan."

"Gidan nan Mama kinga sana'a akeyi kala kala, da masu kitso da masu kunshi da masu wankau, harda dai basu yin abinci sai dawa ba dole ayi gulma ba a gidan nan."

Itada Mama bata ce komai ba, tana tunanin halin yan gidan nasu.

Niko nace ai *GIDAN HAYAR* kenan Mama, tana cikin tinanin taji Rumaisa na yi mata magana.

"Yauwa Mama yau da wuri zani tafi gidan aiki na, saboda ina son nadawo da wuri na wuce Isilamiya, bari ma na tashi kawai na shiga wanka, Mama zo ki duba man kar wani ya shigo man ina cikin wanka kinsan dabi'ar gidan nan ce, bayan mutun yasa ba shi daya ke da gida ba."... Cewa Mama tayi."Yo ko kai daya ke da gida ai kace akwai kowa in ba kowa sannan kashiga, balle wannan gida ba naka ba *GIDAN* *HAYA*, ai Rumaisa hakuri zamuyi da halin yan gidan nan, tashi mu tatafi ki samu ki shiga kina fitowa nima na shiga, daman Babanki Shi tunda asuba yake wankashi."..."To Mama."

Haka su Rumaisa suka tashi, suka fita tsakar gidan, suka ebi ruwa a rijiya sannan suka kama hanyar kewaye, amman kafin su ida shiga Lami ta taso wai ta rigasu niyar shiga zuwa tayi ta nemo buta, haka su Rumaisa suka kyaleta basu kulata ba, ita ko Lami taso su biye mata suyi fada tunda uwar safiya sai kace suma kalar tane..

Bayan Lami ta  fito, Rumaisa ta fara shiga sannan Mama ta shiga suna gama wa suka koma dakinsu Rumaisa ta shirya cikin wata yar atamfarta tasa hijab dinta ta kama hanyar zuwa gidan aikinta..

"Assalama Alaikum."

"Amin wa'alaikumus Sallama."... "Aunty ina kwana."! ?..."Lafiya lau Rumaisa, Antashi lafiya."!?..."Lafiya lau Alhmdulh.".."ya Mamarki take."!?.."Duk suna lafiya Aunty."..."To Alhmdulh, Amman yau Rumaisa kin zo da wuri.".... "eh Aunty inason nagama da wuri zanyi wanki sanann na wuce Isilamiya."..."ok Allah sarki, Allah ya taimaka."..."Amin Aunty."

Nan dai Rumaisa ta fara yin moping din main parlour, sannan tayi na dakin Hajiya Maryam, ta wuce ta gyara kitchen, sai tayi wanke wanke, tana gama wa, ta taya Hajiya Maryam sauwar abincin rana,suka jerashi a dining sannan Hajiya ta sawa Rumaisa nasa ta, tayi mata godia ta wuce gida, tana jin dadin aiki gidan Hajiya Maryam, dan ita Hajiya mutun ce mai mutunci bata da wulakanta Dan  Adam, duk dukiyar mijinta da yake da ita  haka baisa ta ji warin tallkaba...

"Sallama Alama Alaikum, Sannunku da hutawa mutanan gidan nan."... Cewar Rumaisa da dawowarta kenan daga gidan aiki.

Ai Lami cewa tayi."ahaiye mun de mungode Allah bamu zuwa gidajen mutane zalamar Abinci, ko Hindatu."?.... Itaam Hindatu cikin wulakanci ta fara dariya tana cewa"aiko dai Lami, yo Allah ya bamu wadatar zuci,  mai zamuyi gidan wasu kwakwa, Halimai."?.... Ta jefa ma Halimai tambayar taba dariya raini, itama Halimai cewa tayi."Uhmmm kedai tayani gani Hindatu wai shine aka kira da *ANKI CIN BIRI* , *ANCI DILA* , hahahaha, yo ni  Halimai Allah ya sawaka man da zuwa kwakwa gidan mutane, ai na gwanma ce na kwana banci komai ba."... Ta karasa maganar itama tana kallon Rumaisa tana dariya.

Cewa Rumaisa tayi cikin ɓacin rai."Eh ai shiyasa naji ku yau da safe kuna fada a kan abinci, nagode ma Allah ni *Rumaisa* da nike zuwa kwakwa gidan mutane, Alhmdulh tunda bani satar abun wani, kin ga ko da *MUGUWAR RAWA,* *GWAMMA KIN* *TASHI* "

"Kam ubancan, ubawa kike gayama magana haka"? Cikin kukuwa da ɓacin rai tace."Wanda ya tsargu da kashi baki ji masu karin magana na cewa *IYA GANI, IYA KYALEWA,BA* dan haka in dan zaku yi abun ku karda ku sake ku sanyo ni, domin ni ba kyaleku zanyi ba kunji nagayama maku, baku iya komai ba sai *ZAMAN* *BANZA* da *SA* *IDO* aikin kenan an dai ji kunya wallahi."

"Ke Rumaisa, wai maiye haka?  bana ce maki karda na sake jin kin biye ma su ba?  kuna cece kace, sai kace wasu abokanki?  baki san dai kiga bakina yayi shiru ko."!?... Cikin firgici tace."Aah Mama ba haka bane, amman dan Allah kiyi hakuri ba zan Kuma ba."... Cewa Mama tayi."bani zaki ba hakuri ba su zaki ba hakuri, su da kika dage kina ta gaya masu magana san rainki sai kace wasu kawayenki, ai ko ba komai sun girmaiki, maza basu hakuri kafin raina ya baci."

"Su Lami dan Allah kuyi hakuri ba zan Kuma ba.".... Cikin fada Lami tace."da hakurin ya mutu sarakar nawa kika bada? fitsaraira marar kunya kawai."... ita dai Rumaisa bata ce komai ba ta shiga warta daki ta barsu tsakar gida sunata aikin jaraba..

"Rumaisa."... "naam Mama."... "daga yau itace rana ta karshe da zan maki magana a kan fadan da kike da su Halimai, taya zaki tsaya kina biye masu? Kuma kin san sarai mutanan nan ba wani tunani ga resu ba?  dan da kowa ma fada suke tunda suke yi da mazajensu dan haka daga yau kar na sake ji.".. "insha Allah Mama bazaki sake ji ba, bari na tashi nayi Wannnan wanki kafin lokacin Isilamiya yayi."

"To shikenan Allah yayi maki albarka, ya baki miji na gari."... "Amin Mama."

Bayan Rumaisa ta gama yin wanki, ta shirya ta wucewarta Isilamiya tana dawo wa ta tadda Mama tana aikin Tuwan dare, nan ta cire hijab taje ta kama ma Mama aiki, suna gama tuwo da miya, suka diba suka bama mutanan gidan sannan suka kwashe tuwansu suka ajiye a daki, suna jiran Baban Rumaisa ya dawo suci abincin, da yake tare suke cin abinci dare, bayan ya dawo suka ci abinci sukayi sallah kowa ya kwanta yayi bacci....




*Yar'mutan kankia ce❣️*

Share
Comment
Vote
And
Like
Pls


🏭🏭🏭🏭🏭🏭🏭🏭
   A GIDAN HAYA
🏭🏭🏭🏭🏭🏭🏭🏭

_STORY AND WRITING_ _BY_
           _Jameelah jameey_
*Yar'mutan kankia ce ❣️*

            

*🌍MANAZARTA*
*WRITERS ASSOCIATION📚🖊*
      *M. W. A*

'''Kungiya d'aya tamkar da dubu.Masu Nazari da Aiki da Ilimi, Burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma Nishad'antar
da masoyan ta.🤙🏻'''
https://www.facebook.com/107980080946102?referrer=whatsa
____________________________________

      

*BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*

'''NASADAUKAR DA WANNAN LITTAFIN GA NAMTARY UMMYN ABBA ALLAH YA JiKANKI YASA MUTUWA TAZAMO HUTU A GAREKI, ALLAH YABA MIJINKI DA YARANKI DA DUK WANNI MAKUSANTANKI HAKURI DA JURINYAR RASHINKI😭🙏🏻'''



Page_3-4

"Rumaisa.".. "Naam Baba, ina kwana."?  "lafiya lau, kin tashi lafiya"? "Lafiya lau Baba, "yauwa da man magana nike so nayi dake, jiya Mamanki ta gaya man yanda ki kayi fada da mutanan gidan, to daga yau karki yarda na sake ji, Kuma ba tarbiyar da muka baki ba kenan, bani son naga karami Yana raina na gaba da shi kinji."?cewa tayi. "Eh Baba, naji." cewa yayi."To Allah yayi maki albarka." "Amin Baba."
"To Maman Rumaisa ni zan wuce neman kudi, da akwai abunda kuke bukata."?  Cewa tayi."Eh ba sauran magi ya kare yau."murmushi Baban Rumaisa yayi sannan yace."Shi Kadai ya kare babu komai."? Cewa itama tayi tana murmushi. "Eh Shi kadai ya kare gaskiya."cewa yayi."To ga wata Naira dari biyu nan kun sawo magin, ni na wuce sai na dawo."ansa tayi tana cewa. "To angode, adawo lfy."cikin jindadi yace."Allah yasa, Amin."
"Mama bari nasamu na dan kwanta kafin gari ya ida yin haske."cewa Mama tayi. "Aah tashi dai mutashi mu shiga wanka, kafin mutanan gidan su tashi bacci."cewa tayi. "To shikenan Mama, na tashi mu wuce ko."?.. "to daman Babanki ya jawo mana ruwan wankan har dafa mana Shi yayi mu tafi kar ma ya huce."
Rumaisa ta fara shiga wankan tana fitowa ta tsarema Mama itama ta shiga, suna fitowa suka yi wanke wankensu duk abunda suka san nasune sai da suka kaudashi, suka kai shi daki, suka kulle dakinsu suka yi kwanciyarsu suna basu tashi ba sai karfe 9 na safe, Rumaisa ta shirya ta tafi gidan aiki...
Sallama Alaikum, Aunty ina kwna? Kin gani yau Kuma sai yanzun."cewa Hajiya Maryam tayi."aiko dai yanzun Fadila ta gama tambayar ki, zaki raka ta wai kunshi, ta gaji da jiranki, sai Yayansu yayi dropping din ta ya wuce wajen aiki."cewa tayi."ayya banji dadi ba, ai da na raka ko mike kafafu nayi tunda yau babu Isilamiya yau, ai shiyasa ban zo da wuri ba."
"Nikom nace Rumaisa yaushe zan baki waka kiyi man awara, kinsan Fadil yana bala'in san awara, gashi yau na ida soya mashi ta cikin freeze, nasan gobe dan Ubanshi sai munyi fada da Shi in yaji babu awarar.".. Murmushi tayi sannan tace."Shi dai Yaya Fadil yana son awara naga Alama, bakomai Aunty bari na ida aiki yanzun naje nayi maki ita zuwa anjima nagama insha Allah."
"Bani takura maki ba dai ko Rumaisa."?...cewa tayi."haba Aunty wata kallar takura, ai kifi karfin komai a guna.".. "To nagode Rumaisa, bari na tashi ya dibo wankan kafin ki gama."cewa tayi."To Aunty a fito lafiya."..  "Allah yasa."
Bayan Rumaisa ta gama yin aikin gida, ta ansa waken ta wuce gida, tana mamakin yanda Fadil yake da halinshi, shide haka Allah yayo Shi cewa tayi."ni Rumaisa ai tunda nike ban taba ganin dariyarshi ba, gaskiya Fadila tana hakuri da Allah ya hada ta da Yaya mai halin Fadil ace mutum baya dariya kullum fuskar shi tamau sai kace an aiko mashi da sakon mutuwa."haka ta kama maganar ta cikin zuciya har ta isa gida, dan tayi alkwarin baza ta sake yi masu sallama ba, in ba dai su Maman A'i ta iske ba a tsakar gidan wannan zata yi mata sallama har ta gaidata domin Maman A'i mace mai hankali da wayau...
Dawowar Rumaisa gida kenan tace."Mama ga aiki awara nan zamu sake yi ma Aunty Maryam." murmushi Mama tayi tace."A'a to bari na fito daman zaman banza nike yi bani da abun yi."nan fa Mama ta fito cikin some minute suka tsinke wankan, nan Rumaisa tasa hijab takai markade, tana dawowa suka daura sanwar awararsu, suna fira da Maman A'i, nan Hindatu ta fito tana yi masu wannan kallo sanann tace."Allah ka rabamu da matatsiyar zuciya, in ba rashin zuciya ba, mutane sai dan banzar kwakwa, in ba kwakwa ba ace duk sanda za'ayi awara kuke yinta dan ku samu na dare."
Maman A'i tace."Ai Hindatu kasan ance *NEMAN NA KAI,*  *HALAK NE,* dan haka ba ruwanki da lamarinsu, ya ka mata ku chanza hali, haba Hindatu mutanan nan basu tsarema ku komai ba amman duk kunbi ku sa masu ido, Kuma ku ke da abun da ido."ɗaga ma Maman A'i hannu Hindatu tayi tana cewa."dakata malama, au ashe yar iya Andawo?  yanzun za'a fara yin shigar sugula, inba shigar sugula ba wa ya saki cikin wannan maganar yar'nema."? Cewa Maman A'i tayi."Ban sani ba sai naji bugu sannan."Maman Rumaisa ce ta fara ba Maman A'i hakuri dan taga ranta ya fara ɓaci yanzun zata biye masu suyi fada cewa tayi."Dan Allah Maman A'i kiyi hakuri, karda ki biye mata, duka duka maiye duniyar, da za'abiye Anita bata lokaci gurin fada, kinga ma awarar ta kusa yi muna gama soyawa sai mu shiga daki ba shikenan ba." cikin raina da jin zafi da hassada Hindatu tace."da ya fi maku ma kwakwata banza da ku."Maman A'i tace."ke dai kije ji da shi, mundai yi gaba sai dai a bimu da ido."
"Maman A'i dan Allah kibar biye masu, mutanan nan ba hankali ne dasu ba." Cewa Maman A'i tayi."wallahi Maman Rumaisa, indai su kayi bisa idona sai na yi magana, yo ina dalili mutane ba ku hada miji ba, amman sunbi sun sa maka ido suna kishi dakai, ai wannan kishi ne da hassada, haka zasu kare a wulakance, mu Kuma insha Allah yanzun muka fara yin gaba, dan munyi masu nisa fidtinkau, dan ba yabon kai ba baki daya gidan nan mazajenmu sunfi sauran nasu, ai Alhmdulh ko nan aka tsaya."cewa Maman Rumaisa tayi."Allah yasa dai mu dace, "Amin Maman Rumaisa...
Bayan sun gama yin awarar, Rumaisa taje ta kaima Hajiya Maryam, nan suka dan yi hira sannan tayi mata sallama ta dawo gida direct dakinsu ta wuce, daman tsakar gidan su Lami ya iske suna zaman banza, zaman gulma...
"Rumaisa har kin dawo? "Eh Mama wallahi yau duk na gaji sosai, "ai dole, tashi kici abinci ba sai kin tsaya jiran Babanki ba, "To Mama." bayan ta gama cin abinci ta samu ta kwanta cikin bacci taji ana fada da mijin Halimai da na Lami, suna ta fada sai kace yara kanana,  wai abunda ya hada su, shi mijin Lami yace ma mijin Halimai yayi ma Halimai tsakani da matarshi dan ya lura ita take koya ma Lami zaman gulma da kirbibi, shi kuma mijin Halimai yace suna koya ma juna dai, dan matarshi ba ma gulmaciya bace, da kyal da jibin koshi su Baban Rumaisa suka raba wanann...


Read / Download A GIDAN HAYA

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album