Join Our WhatsApp Group

JAMILA Complete Hausa Novel Document by JAMILA


JAMILA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 23622



JAMILA

Reading Time: 1 Hours

Added On: 16, Feb 2024

Author: Ummu Maher ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : 07068606171

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 129.24 kb

File Type: txt

Views: 397+

Download: 110+

Last download: 1 hour ago

Description/Story: 🤍 _JÁMÉÉLÉR_ 🤍🍇*

💎Labarin Jamila🖌️

_📖Labari mai ban tausayi tare da tsantsar cin amana_ 🖊️



Na📘✍🏼

*RABI'ATU BASHIR ABDULLAHI*
(Ummu Maher)Miss green💚☘️

*MATAR BASH💎*



✍🏼Marubuciyar📘📘📘


*1_UWAR GIDANA💖*
*2_AUREN DOLE👰🏻‍♀*
*3_FAROUK🍋*
*4_INAYATULLAH🌐💠*
*5RUHI D'AYA💙🤍*
*6_K'ADDARAR RAYUWA Ce⛲*
*7_ASANADIN ABAYAR SALLAH👘*
*8 LOADING.... AKAN AIKINA👩🏻‍💼💚*

*AND KNOW*
*9_JAMEELA🍇🤍*

___________📖🖌️
Ina gaida sarakan surutu na Mk palace😂musamman Rafi'at/Dikko


بسم الله الرحمن الرحيم

💫💫
*🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️*


https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl

_*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_

*Dedicated to My Real Nimcy Luv kina wuta🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥*

Ina gaida Masoyana kamar haka🖌️

Na'ima Sulaiman
(Nimcy Luv❤️)
Momin Shukura
Momin Minal
Nabila Dikko
Hajara L Sadiq
Queen nersmer
Dr Maryam
Hajiya Maryam
Bintu Umar Abbale
Rukayya(Gawata)
Rukayya Adam marubuciyar Dr Muhseen.


Sannan INA gaida Masoyana aduk inda wadand'a ban ambato sunansu ba.





*TSOKACI;*
Wannan labarin mallakin Ummu Maher ne ban yarda a canza min labarina ta kowacce hanya ba sai da izinina.






*💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫*




Shãfî nã🟨1


Wasu shuke shuke ne masu kyau da k'awarta wa awajan da muke tare da kukan tsuntsaye suna sauti a hankali.




"Jamila kinji irin farin cikin da na ke ji kuwa idan nazo wajen nan kuwa?" Ina manta dukkanin rayuwar da na yi matuk'ar nazo wajen nan "Jamila mutum baya zab'awa kansa rayuwar da zaiyi a gaba saboda abubuwa da yawa suna faruwa acikin rayuwarmu Wanda bamu shirya musu ba,Amman wannan yana cikin k'addarar ko wani d'an adam alokacin saka shirya da kuma lokacin da baka shirya ba."



Wacce a ke kira da Jamila ta yi shiru kwalla na zuba a idonta ta kalli k'awar ta mai irin sunanta wato Jamila cikin sheshshek'ar kuka ta ce"My namesake kenan tabbas bamu ne muke zab'awa kanmu rayuwar da zamuyi ba rayuwa ce ta ke zab'a mana hak'ik'a kamar yadda bakya son tuna rayuwarki ta da nima haka ya ke a waje na."kuma na tabbata namesake labarina ya fi na ki muni nesa ba kusa ba,bana son tuna labarina ko kad'an saboda duk farin cikin dana ke ciki idan na tuno yakan sakani cikin mawuyacin hali".





"Jamila inason ki bani labarinki saboda a kullum haka ki ke Ce wa labarinki yafi nawa muni yana da kyau ki bani labarinki duk da nima har yanzu baki ji labarina ba?".



"Yanzu kuwa zan baki labarina idan nagama sai ki bani naki namesake sai inji na wanene yafi muni don nasan labarina yafi naki.





*JIHAR KANO*

Aiki muke sosai a gidan namu,nida ummana muna kitchen muna girke girke kala kala na tarar Yayanmu wato Yaya Deen,Shi d'an Yayan Mahaifina ne tun yana k'arami Mahaifinsa ya rasu shida Mahaifiyarsa a saka makon had'arin mota da ya ritsa dasu a hanyarsu ta zuwa Jigawa.

Mahaifinsa ya barmasa dukiya sosai saboda yafi mahaifina kud'i,koda suka mutu sai Baba na ya d'auki Yaya Deen ya rik'esa tun yana k'arami harya girma a yanzu kuma yana England karatu.


Shekararsa shida a England sai dai ayi waya dashi Amman bai tab'a zuwa ba sai a yanzun da ya gama makarantar,ni da Yaya Deen mun shak'u sosai kafin ya tafi England yadda ya ke sona nima haka nake sonshi.




" Aunty Jamila ga Yaya Deen nan ya dawo".

Da Sauri na fito daga kitchen d'in ina gudu don inje in shirya don ko kwalliya ban yi ba duk da na yi wanka don in rage Aiki,Umma kuwa dariya ta yi tana k'ara sa girkin don tasan yadda Y'arta ta tashak'u da Deen.



Kwalliya na yi sosai da wasu English wearer's masu kyau Riga ce T_sheet da wandon jeans Wanda yasha ado da flowers masu kyau na tamke yalwataccen gashi na da Ribom daman gani y'ar kyakkyawa sai na yi kamar y'ar Baby banyi amfani da d'an kwali ba kawai na feshe jikinta da tsadadden Turare mai matuk'ar dad'i,sannan na d'auki High Hill d'ina mai matuk'ar tudu na saka koda na duba madubi ba k'ara min kyau naga na yi ba sannan Na fita.



Shi kuwa Yaya Deen tunda ya shigo ya baza idanuwansa don ganin ta inda kyakkyawar k'anwar tashi zata fito,Cikin takuna mai d'aukar hankali kamar bana son taka k'asa na iso Farlon.


K'amshin turare na ne ya iso tun kafin in iso,Yaya Deen ya ware min hannyensa alamun in shiga ciki,Kunya ce ta kamani don gani na ke yi da da yanzu ba d'aya bane sanda Yaya Deen ya yi tafiya shekara ta 10 yanzu 16.



"Come on my lovely sister I miss u".

Kawai sai na tsinci kaina a mai cemai" I miss u to Yaya Deen" cikin shagwab'a na fad'i hakan.


Kawai sai na fad'a jikinsa gaba ki d'aya na zauna kan cinyarsa,Wani irin Abu yaji Wanda bai tab'a jinsa ba sai akan k'anwar tashi,ya rufe idonshi ya bud'e ya d'orashi akaina tun daga k'asa har sama ya shiga k'aremin kallo.






Notice
Iyaye kudinga kula da tarbiyyar y'ay'anku Ku kula da irin tufafin da zasu saka kada mu d'orawa kanmu Rayuwar Yahudawa da nasara.




*Kuyi hakuri nayi tyiping kad'an*

Na yi muku alk'awarin matuk'ar naga yawan Comments ya k'aru zan k'ara yawan tyiping.
*_🍇🤍JÁMÉÉLÉR🤍🍇_*


💎Labarin Jamila🖌️



*Na💖*
*RABI'ATU BASHIR ABDULLAHI*
(Ummu Maher)Miss green💚☘️

*MATAR BASH💎*


📲MINAL MULTIMEDIA
https://youtu.be/NCrdsZmuh6E

Dan Allah kushiga ku danna Mana subscribe




*_Dedicated to Real Nimcy Luv&Hadiza Barau gidan Iko_.*
_

_*📚JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION*_



*Shãfî nã🟨2&3*


Ganin irin kallon da ya ke min yasa na tashi daga zaunen da na ke ina k'ara yi mai sannu da zuwa,Har yanzu kallon mamaki ya ke bina dashi yarinyar da ya tafi ya barta tana y'ar k'arama Amman yanzu jibi yadda halittun ta suka koma.


Yaya Deen Ya ce"Kai Babyn Dady gaskiya kin girma Sosai ina tunanin kayan Dana siyo miki ma baza suyi miki ba saboda na d'auka yadda ki ke Siririya yanzu ma haka ki ke Ashe ba haka ba ne.?"


Shagwab'a na fara yi mai shi kuwa ya shagala wajen kallona,nima shi d'in na ke kallo yadda naga ya k'ara kyau da wani kwarjini kamar ba shi ba.



Da daddare Ya kirawo mu ni da Yaya ta Safiyya sai K'anne na Twins,Raliya da Rayya,sai k'ara min k'aninmu Nasir,ko wa da tsarabarsa sai da ya gama bawa kowa sannan ya dawo kaina yana nuna min kusa dashi alamar in zauna.


Bank'i ta tashi ba na zauna a d'an d'arare don duk saka kaya matsatstsu da na ke yi ban tab'a koda rik'e hannun Namiji ba ballan tana ma har in zauna Kusa dashi.


Janyo wani k'aton akwati ya yi Wanda daga yadda ya janyo shi zaki tabbata ce wa akwai shi da nauyi,bud'e wa ya fara yi sannan ya turomun shi ya zuba min shanyayyun idanuwanshi.



Kallon kayan na fara yi Wanda a k'iyasce za su yi kala 20 kallon kayan na fara yi sannan na kalleshi ina matuk'ar mamakin kayan ina tuno da k'awata Fatima ita ko suturar arzik'i ma ba dashi ballan tana zuwa mkrnt rayuwar Fatima tana bata tausayi duk tana gaya wa iyayenta suna taima konsu don duk Wanda ba shi dashi ka tausaya mishi kaima sai Allah ya tausaya maka.



Gyaran murya ya yi ganin na yi zurfi acikin tunani na kawai sai na ji yana ce wa"My Jamy me ta faru ne naji kina tunani haba duka_duka just16 fa ba kisan rayuwa ba har yanzu shiyyasa.


Godiya na ringa yi mai abisa kyautar da ya yi min,sai da na sami d'an ta yi wato Yaya Aunty Safiyya muka fara Jan akwatin.



Kallona ta yi irin kallon ayar tambayar nan ta ke kallona?Amman bance da ita k'ala ba na fito daga d'akin don dama munyi nida Yaya Deen zan dawo Don ya ce min akwai maganar da ya ke son muyi.




"Jamcy kamar yadda na ce miki inason muyi magana to yanzu zan fad'i miki ce wa ina sonki Jamcy tun kina cikin zaninki na ke sonki na ke k'aunarki Amman ki yi hak'uri idan na sab'a miki."



Kunya ce ta kamani sosai ban iya na kalleshi ba na tashi zan fita,kawai sai naji ya janyo ni na fad'a gaba ki d'aya ajikinshi.




Aunty Safiyya da ke lab'e tana video wani hawaye ne ya fara zuba a idanunta yanzu a ce duk son da ta ke yi wa Yaya Deen Amman ya b'uge da son k'anwarta.


Ina baza ta tab'a yiyuwa ba Duk abinda za ta yi sai ta yi don ta raba wannan had'i,da Sauri ta juya ta shiga d'akin ta kwanta tare da Adana wayarta wata hassada ce ta ta sowa Safiyya lokaci d'aya tun suna k'anana duk inda suka shiga kafin kowa ya tanka ta sai an fara tan kani saboda halitta ta kuma gashi na fita fara'ah don ita bata da fara'ah ko d'aya.




Cikin kunya na tashi daga jikinsa da Sauri na gudo daga d'akin ina cikin tafiya naji wayata ta yi k'ara number Fatima ce na gani da Sauri na yi pick d'in call d'in nata.




"Fatima ganinan zuwa bari in gaya wa Mama sai Aunty Safiyya ta rakoni gidan naku".


A d'aya b'an garen Fatima ta amsa da to tana sharar kwallah.




Mama na samu a d'akinta tana lazimi na tsaya Ina jiran Mama ta idar da sallar,sallama ta yi sannan ta jiyo ta kalleni.


" Mama yanzu Fatima ta kirawo ni tana fad'amin abin babu dad'i,wai Yanzu Aka cullo musu kayan su waje wai kud'in hayarsu ya k'are."


Sallalami Mama ta yi sannan ta ce"to muje tare Harda Alhaji mu gano sannan ayi solving d'in matsalar tun yanzu."


Shi kuwa Deen dariya ya yi sannan ya ce aransa Tunda na ke ban tab'a jin sha'awar wani Abu ba,koda na yi karatu a turai ban tab'a had'a jikina da wata ba Allah dai ya mallakamin k'anwata Amin.






*********
Sun fito musu da kayansu waje Alokacin da Fatima ta hangomu da gudu ta rungume ni tana kuka tana nuna min su da hannu yadda suke fito musu da kayan su hakuri na fara bata,Mama kuma taje wajen Inna wato Mahaifiyar Fatima tana rarrashinta.


Abbanmu ne ya je ya fara magana dasu tare da basu kud'in su, kawai muna tsaye sai muka ga suna zubawa Abbanmu kayansu Fatima a bayan Boot.



Kallon su kawai na farayi ina rik'e bakina ganin yadda kullum Nigeria ta ke k'ara zuwa sahon farko wajen son kud'i da Ha'inci.




Koda muka shiga mota ma hak'uri na dinga bata ina bata baki har muka je gida,Abbanmu ya yanke shawarar zasu zauna agidanmu kafin a samo musu wani gidan don ya yi Alk'awari ba zasu k'ara zama a gidan haya ba zai siya musu wani gidan.



*Wacece Fatima*
Fatima dai shine asalin sunanta y'an asalin k'asar Cameron ne,buzaye ne Mahaifinta da Mahaifiyarta duk buzaye ne Mijinta mai suna Suraja ya shigo Nigeria ne neman aiki koda gadi ne to shine Allah ya taimakeshi ya fara Aiki a gidan su Yaya Deen har Mahaifin Yaya Deen yarasu sannan ya koma gida anan zaman k'asar tasa wato Cameron yafi k'arfinsa,ganin haka ne ya d'ebo matarsa alokacin ba'ah haifi Fatima ba.

Sun dawo Nigeria inda ya k'ara samun Aiki na gadi to da wannan ne rayuwar ta fara yimai dad'i,ana cikin haka matarsa Wacce a ke cewa Imilli ta haihu y'an biyu duk mata Amman d'ayar tazo babu rai aka saka d'ayar suna Fatima.



Fatima Mahaifinta ya saka ta makrntar boko da ta islamiyya,tun Fatima tana k'arama suka had'u da Jamila a Mkrntr Islamiya sun shak'u da juna sosai har suka girma suna tare,Mahaifin Jamila yana taimakonsu sosai,har zuwa lokacin da aka nemi mahaifin Fatima aka rasa daga lolacinne kuma rayuwa ta juya musu.



*Cigaban Labari*
********
Muna zuwa gida Abba ya kirawo mai gadi ya fara shiga da kayansu,Yaya Deen ne ya fito daga sashensa yasha manyan kaya ya yi kyau na kalleshi ta gefe ya nufo inda muke.



"Subhana Lillahi Inna Lillahi Wa'inna Ilaihi Raji'un".


Fatima ce ta fara fad'in haka bakinta yana kakkarwa tana nuna Yaya Deen,Ai sai gani mukayi ta sume Mana gaba ki d'aya.








🤔🤫To fa me ya sumar da Fatima kuma?



Kubiyoni don jin yadda zata kaya.





*Ummu Maher ce*
*_🍇🤍JÁMÉÉLÉR🤍🍇_*


💎Labarin Jamila🖌️



*Na💖*
*RABI'ATU BASHIR ABDULLAHI*
(Ummu Maher)Miss green💚☘️

*MATAR BASH💎*


📲MINAL MULTIMEDIA
https://youtu.be/NCrdsZmuh6E

Dan Allah kushiga ku danna Mana subscribe




*_Dedicated to Real Nimcy Luv&Hadiza Barau gidan Iko_.*
_

_*📚JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION*_


*Shãfî nã🟨4&5*


Salati kowa ya fara yi sannan muka nufi Fatima ni ce na fara ruk'ota tun kafin ta je k'asa ina kuka na fara girgiza Fatima.



Shima Yaya Deen ya kid'ime yana mamakin sumanta kuma tana nuna sa to me ye had'insa da wannan yarinyar shi dai yasan bai tab'a ganinta ba to meye kuma na tsorata don ta ganshi?.


Ruwa aka dinga yayyafawa Fatima har sai da ta tashi,Umma ta kalli Mahaifiyar Fatima ta ce"da man Tana haka ne ko kuwa yanzu ta fara?".
Eh to gaskiya tana haka wani lokacin Amman sai an b'ata mata rai ina ganin ko abinda ya faru d'azu ne ya janyo wannan matsalar."



D'akin mu na kai Fatima muka zauna muna hira kamar ba ita ce ta suma d'azun ba,muna cikin hirar ne Aunty Safiyya ta shigo ta ce"ke Waye ya kawo mana wannan kucakar cikin d'akinmu Salan suzo su shafa mana tsiya....."


Tun kafin ta k'ara sa maganar na yi saurin ce wa"haba Aunty Safiyya me yasa ki ke haka ne?"kuma maganar talauci da ki ke yi ai Allah ne yaso ya barsu haka,irin wannan abinda ki ke yi babu dad'i fa....."


Wani mari ta wanka min saida naga wucewar taurari na dafe kunci na ina kuka,Fatima ta rungume ni a k'irjin ta tana rarrashi na.

Tsaki ta yi ta fita daga cikin d'akin ta barmu daga ni sai Fatima,sharemin hawaye tayi sannan ta ce"Jamila idan har zuwa gidanku zai zama...."rufe mata baki na yi Ina kuka Na ce "kiyi hak'uri ai ba Aunty Safiyya ce ta kawoki gidannan ba ballanta na ma ace? don haka ki yi hak'uri.



Kafin kace me har mun cigaba da hirarmu cikin kulawa da junanmu,muna cikin hirar ne na ke tambayar ta me ya faru d'azu ta fad'i?

Dariya ta yi sannan ta ce" Jamila aduk sanda kika ga na yi irin wannan ki tabbatar na ga mutumin da ba shi da gaskiya ne to anan ne zaki ga na suma".


Dariya maganar ta ta bani sannan na ce yanzu Fatima yayan nawa Mara gaskiya? ki ce zamuyi fad'a da ke?".


Dariya ta yi sannan ta ce a yanzu ba zaki gane duk wani abinda zan fad'a miki ba sai nan gaba idan kika gani da idaniyarki.


Ban d'auki maganarta sa mahimmanci ba muka cigaba da hirarmu har muka yi bacci.




Haka rayuwa ta yi ta juya mana cikin annushuwa sai dai matsalar mu d'aya Aunty Safiyya don kullum cikin k'untata mun ta ke nida Fatima.


Mama har ta yi fad'an har ta gaji,a b'angaren Yaya Deen kuwa ya samu yadda ya keso ta fannin k'anwar tasa don...


Read / Download JAMILA

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album