Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

IN DA RAI DA RABO Complete Hausa Novel Document by IN DA RAI DA RABO


IN DA RAI DA RABO

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 337860



IN DA RAI DA RABO

Reading Time: 28 Hours

Added On: 05, Sep 2024

Author: Sameena Aliyu ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : +234 703 745 3539

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 1.82 mb

File Type: txt

Views: 804+

Download: 3283+

Last download: 47 minutes ago

Description/Story: [25/11, 16:42] +234 703 745 3539: *INDA RAI*
_.............DA RABO_



*01*



*©Sameena Aleeyou...✍🏽*



BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM


*Dedicated to my Trio*♥


Cikeda risinawa matashi mai kimanin shekaru 30 a duniya ya d’ago yana duban Dattijon mutumin mai kimanin shekaru 58 zuwa da tara kana yace “But Daddy.....”

Katsesa yayi da fad’in “No SAMEER I don’t want to hear anything, what’s gotten into you Son.... Haba Sameer ni nasan ba haka na tayar dakai ba... Abinda nakeso da kai ka tashi ka tafi gidan Uncle d’inka ka basa hak’uri sannan ka d’auki matarka ku tafi magana ya k’are....”

Jinjina kai yayi kana yace “Ok Daddy I’ll do as you say....”

Murmushi Dattijon yayi kana yace “That’s my boy Allah ya maka albarka....”

“Ameen Daddy...” Ya fad’i yana k’ok’arin mik’ewa had’ida fidda wayar salulansa daga aljihu....

Satan kallon sashen da Mummynsa ke zaune yayi aiko banda uwar harara babu abinda take aika masa.... K’arasawa ya d’anyi had’ida risinawa kana yace “I’m sorry Mummy... I promise this will never happen again in shaa Allah.....”

Jinjina kai tayi kana tace “I hope so, Ace aure ko wata biyar mai kyau bakuyi ba an soma samun sab’ani irin haka ai babu dad’i... Dama naji batu mai dad’i kaji koh...”

A hankali ya jinjina kai kafin ya fice daga parlorn....

Motarsa ya nufa ba tareda ya kula da Malam Sallau dake gaidashi ba...

Ya jima k’ofar gidansu Siyama yana tunanin ta yanda zai soma bada hak’uri don sam hakan ba d’abi’arsa bace idandai ba ma iyayensa bane, a hankali ya rintse idanunsa had’ida furta “Goodness! Where do I start....”

K’aran da wayarsa tayi ne ya sanyasa zaro wayar daga aljihun gaban rigarsa daga d’aya b’angaren Sultan yace “Doc we’ve an emergency here at the hospital, Sameer we need you right away....”

Shafe goshinsa ya d’anyi kana yace “Is my presence really necessary, just do what you can, I’m dealing with another problem here...Please...” ya k’arashe yana lumshe dogayen idanunsa masu yalwan suma....

Fuzar da iska Sultan yayi kana yace “Sameer it’s a boy.... He suffered a multiple deep burns... I’m afraid he’s dying...” Ta cikin wayar yake jiyo sautin kukan yaron wanda k’unan wuta ya masa babu dad’i, cikin sauri Sameer ya juya kan motarsa yana fad’in “I’ll be on my way....” Cikin sauri ya karya kan motar had’ida ficewa daga gidan mai gadi na faman d’aga masa hannu alamun a sauk’a lafiya....

****

*Kano*


Cikin sanyin jiki suka shigo parlorn ko wacce tayi jigum jigum, budurwa mai kimanin shekaru 23 a duniya ne ta soma yab’e baki tace “Wllhi Allah Abbah shi yake biye Mamani take abinda taga dama, haka kurum mata ta tayar da bori wai zata tafi tabi MA’ARUF ni so nake wata rana a barta ta gwada fita nemansa ace yau shekaru 26 babu mutum babu labarinsa toh ta ina zaka soma nemansa, sai anyi magana ace tsufa ke d’awainiya da ita, mtsww...” Ta k’arashe tana jan tsaki....

D’ayar mai kimanin shekaru 19 tace “Wllhi Adda Nabila ni bana ganin laifin Baffah Wali idan ya fice mata a giya, kiga dai duk jikokin gidan nan rankatataf d’inmu ban cire kowa ba harda ke mai sunanta bata damu da kowa ba kullum damuwarta Ma’aruf yaron da tun yana shekara 4 ya b’ace sai anyi magana itada Mamy suce INDA RAI DA RABO, Allah na tuba da ace yana raye tsawon shekarun nan ai da ya bayyana mana....”

K’aramar cikinsu mai kimanin shekaru 16 tace “Ahtoh sai anyi magana tace Babban Jika... Mu da yake Yayanmu uwa d’aya uba d’aya ma bamu kaita damuwa b.....” Had’iye kalaman nata tayi cikeda k’unk’uni tana duban wacce ke faman narka mata mugun kallo da alama bata jima da shigowa parlorn ba

“Aunty Zulfah ina yini....”

Gaba d’aya sauran biyun suka juyo suna duban sashen da k’anwarsu ke gaisuwa....

Ganin yanayin Addar tasu wacce ke sanye cikin kayan Bautar K’asa ya sanyasu shan jinin jikkunansu....

Ba tareda ta amsa gaisuwar tasu ba fuska a tsume tace “Mamy fah...?”

Nabila mai bi mata a haife ne tace “Suna can sashen Mamani suna bitan karatunsu na aikin lallashi...”

Girgiza kai kurum Zulfah tayi kana ta nufi k’ofa zata fice Mas’udah mai bin Nabila a haife tayi saurin katseta da fad’in “Allah Aunty Zulfah Mamani abinda take yayi yawa naga dai idan da akwai wanda b’acewar Yaya Ma’aruf zai damesa bayan Mamy da Abbah toh ya kamata ace sai kece tinda ranar da aka haifeki ranar Yaya ya b’ata....”

Nabila ta k’arada “Shiyasa Mamani tafi tsanar Addah sama da kowa a jikokinta a nata tunanin sanadiyar haihuwar Addah Yaya ya b’ata...”

“Ya isheku haka...!” Zulfa’u ta katsesu kafin taci gaba da fad’in “Ku bazakuyi hankali ba, ana cewa yaran Abbah sunfi kaf yaran gidan nan tarbiya amma kuna nema ku shafawa iyayenku bak’in fenti... Sai mai idan Mamani ta nuna damuwarta kan missing grandchild d’inta, badai jikanta bane toh ina ruwanku, idanku baku damu dashi ba sabida baku sanshi ba sai ku k’yaleta ita ta nuna damuwarta, wllhi kunji na rantse kar na sake zuwa gidan nan naji kuna k’anan maganganu kan wannan al’amari kunajina koh...”

Ciki ciki suka amsa kafin Marliya k’aramar cikinsu ta k’arada “Aunty Zulfah yau ina kika baro Kausar naga baki kawota nan gida ba yau....”

Harara kurum Zulfah ta watsa mata kafin ta fice ta nufi sashen Mamani....

****

*Kaduna*


Fitowarsa kenan daga surgery wayarsa dake bisa teburinsa ta d’au ruri.... Dafe kansa yayi ganin mai kiran ba kowa bace illa Mummynsa sannan ta kirasa yafi sau a k’irga, shaf ya mance bai kashe wayar salulansa ba sanda zai shiga aikin domin kuwa akasarin lokuta idan zai shiga aiki kashe wayarsa yake donma kar a nemesa....

A hankali ya d’aga wayar had’ida zama cikin kujeransa....

Kafin ya sami zarafin magana Mummy ta soma balbalesa....

“Sameer ya maka kyau, nace ya maka kyau... Da ka fice zaka gidan Hajiya Faridan gidan uwar wa ka tafi....? Shine sabida tsabagen wulak’anci zaka barsu suna jiranka, ko kasan cewa harta Alhaji Madi bai fice ba ya tsaya jiran zuwanka amma ka kama ka watsa mana k’asa a idanu.... Ya maka kyau Sameer nasan haka zakayi wllhi da ban bari an baka auren Siyama ba....”

Tinda ta soma magana bai katseta ba har saida takai aya, a hankali ya soma fad’in “Mummy calm down please, this isn’t good for your blood pressure.....”

A hasale ta kuma cewa “Don’t ask me to calm down, jininan ma ya hau mana duk ba kaine sila ba....”

A hankali ya shafi goshinsa can k’asan mak’oshinsa ya furta “Goodness..!” A fili kuwa cewa yayi “But Mummy cikinku babu wanda ya damu yaji daga gareni, babu wanda ya damu if I’m also suffering, Mummy this isn’t easy for me either.... Kin sani Mummy kinsan ina son Siyama kuma auren soyayya mukayi.... Kwana biyun nan bansan meke damunta ba... Amma koma meye na miki alk’awari I’ll save our marriage cos I still love my wife, l love her so much...” Ya k’arashe cikin sanyin murya....

Jinjina kai Mummy tayi cikeda jin dad’i kana tace “Yauwa D’an Albarka haka nakeson ji maza ka wuce gidan Uncle Madi d’in daga asibitin zanyi waya wa Hajiya Faridan na sanar da ita aiki ne ya rik’eka a asibiti amma gaka nan zuwa....”

Bai iya amsa Mummy ba har suka ida wayar, mik’ewa yayi had’ida d’aukar wayarsa da key ya nufi duba patient d’insa kafin ya fice...

Sam baisan Siyama nada kishi haka ba, ya kamata ta fahimci yanayin aikinsa da kuma za’a iya kiransa emergency ko wani lokaci.....

A farfajiyan gidan ya iske Alhaji Madi zaune saman kujeru na shak’awata jarida rik’e a hannunsa, don haka kai tsaye cikeda risinawa ya nufi sirkin nasa kuma amini ga Daddynsa...


Daga can d’an gefe ya durk’usa kana ya soma gaida sirkin nasa.... Fuska babu walwala ba kaman yanda ya saba masa d’inba ya amsa...

Sameer ya d’anyi gyaran murya kana yace “Uncle dan Allah ayi hak’uri bana gida Siyama ta fice kuma koda na kira layinta bata d’aga ba amma In sha Allah hakan bazai k’ara faruwa ba...”

Cikeda k’osawa Alhaji Madi ya amsa da “Allah sa kada hakan ya kuma faruwa, a dinga kulawa Sameer, kasan cewa muna tsananin k’aunar Siyama kuma bamu k’aunar ganin kukanta, sanin kanka ne Sameer my children are my life, I can do anything for them ko menene, Siyama da Khalid sune farin cikin rayuwata ka fahimta...”

A hankali Sameer ya jinjina kai kana yace “Ayi hak’uri Uncle za’a kiyaye In sha Allah....”

Alhaji Maina ya kuma jinjina kai had’i da bud’e shafi na gaba a jaridar tasa kana yace “Ka k’arasa ciki ka samu matar taka....”

Cikeda risinawa ya kuma mik’ewa had’ida godiyawa Alhaji Maina kafin ya nufi sashen Ammi mahaifiyar Siyama....

“You know what sis... I think you’re been too impulsive....”

Matashin Saurayi mai kimanin shekaru 26 ya fad’i yana mai duban Addar tasa wacce ratansu shekara guda ne tak....

Pillow dake gefenta ta d’auka ta jefi dashi kana tace “You stay out of this Khalid... Ni ba sa’arka bace...”

Fitoda manyan idanunsa masu
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download IN DA RAI DA RABO

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album