Join Our WhatsApp Group

KATANGA Complete Hausa Novel Document by KATANGA


KATANGA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 72928



KATANGA

Reading Time: 6 Hours

Added On: 28, Jun 2023

Author: Rabe'ah Shuaib Na baba ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : 09037093702

Book License : Paid

Category: Love Novels

File Size: 390.3 kb

File Type: txt

Views: 1551+

Download: 979+

Last download: 5 days ago

Description/Story: "[10/8, 3:42 PM] Binta Lawan: *BEBE'ARTH*


28/8/2020


Wattpad@Rashuna


*KATANGA*


_Ina matuk'ar godiya ga Allah (S.W.T) da zai ba ni ikon kawo muku wannan littafi mai suna KTG, ina fatan yadda zan fara cikin yalwatacciyar lafiya na kammalashi haka, Amin summa Amin_

_Sak'on gaisuwa ga 'yan uwa da abokan arzik'i, da kuma dukkanin masoyana na kusa da nesa, ina kuma fatan za ku bani had'in kai cikin wannan littafin, kalma d'aya kawai zan gaya muku, alk'alamin ya fi mashi tsini, kuyi k'ok'ari kui nitso ku ninkaya cikin wannan sabon alk'alamin mai suna *KATANGA*_

_Hak'k'in mallaka:_
*RABEE'AH SHU'AYB NABABA*
(RASHUNA)


____________
*ONE*

_Bismillahir rahamanir rahim._

*SHIMFID'A*
Malam Ahmadu an haifeshi a garin Zaria, asalin malantarsa ya gadota ne a gurin mahaifinsa Malam Buba, kasancewar kuma tun ya na yaro mahaifiyarsa ta rasu, tare ya rayu da mahaifinsa har sai da ya yi aure da matarsa Asabe sannan Allah ya karb'i ran malam Buba, daga nan Malam Ahmadu ya ci gaba da jan ragamar mahaifinsa ta malamta.
'Ya'ya uku Allah ya azurtasa da shi, Abdullahi, Maryam sai autansa Shamsu, Abdullahi shine ya gado mahaifinsa amman kuma ba a iya malamtar ya tsaya ba ya na da shago a kasuwa da yake sayar da kayan awo.
Malam Ahmadu shine ya zab'awa Abdullahi mata, 'yar amininsa ce k'ud da k'ud da Allah ya karb'i ransu shi da matarsa shekarun baya da suka wuce, kasancewar gidan nasu gidan yawane, kuma auran zumunci akayi tsakanin mahaifan nata, haka take ta watan gari riya a cikin gidan sai uwar bauta da take musu, tausayinta da duba maraicinta da amuntakar da ke tsakaninsa da mahaifinta hakanne yasa ya nemawa Abdullahi auranta, Abdullahi baiyi musu ba kasancewar ya yaba da d'abiunta kuma ta na yawan burgeshi a duk sailin da zasu had'u hakan yasa ya karb'i tayin auranta da hannu bibbiyu.

A gurin Asabe wacce yanzu suke kira da Iya aka fara samun k'alubale, inda ta yi tsalle ta dire akan d'anta ba zai auri 'yar makafi ba, kasancewar mahaifanta duk makafi ne, shikuwa Malam Ahmadu yace ta yi kad'an ta hana wannan auran, idan har taga ba'ayi sa ba to tabbas babu ransa a Duniya.
Abdullahi da Maimuna sun aminta da juna sosai ya yin da suka fad'a zazzafar soyayya nan da nan magabata suka shiga lamuran nasu, a lokacin ne kuma wanda yake neman auran Maryam me suna Yusuf ya fito, a kano yake a zaune aiki ne ya kawosa zaria, tun ganin farko da yaiwa Maryam ya aminta da ita, bai fara zuwa zance ba sai da Malam ya yi masa izini, daga bisani kuma yace ya turo magabatansa.
An tsayar da ranar auran Abdullahi da Maryam lokaci guda .
Anan cikin gidan, Malam Ahmadu ya yanki gefe ya yiwa Abdullahi gini, d'akuna uku ne maka² abinsa a wadace, ya yi musu kuma k'ofar gurinsu da ban, sannan kuma ya had'a masa lefe dai-dai da zamanin da suke ciki.
Ansha shagalin biki kafin a kawo amarya sashinta, ita kuma Maryam aka kaita unguwar Sabon gari.

Lafiya lau zaman Abdullahi da Maimuna yake babu wata matsala ko d'aya, Malam ya d'ebo soyayyar duniya ya d'orawa surukar tasa, kullum in zai shigo gida da abinda zai aika mata da shi, ya yin da Iya kuwa ta bi ta tsaneta, ko kad'an ba ta sakar mata fuska kyara da tsangwama shine tsakaninsu.
Wata d'aya da bikinsu Allah ya azurtata da samun juna biyu, tattali da kulawa fiye da wacce take samu ada Malam yake mata, idan ya fita duk abinda ya san me ciki na sha'awa shi yake siyo mata, Iya kuwa tayi ta sababi a tsakar gida ta na masifar ga d'iyarsa can ta na da juna biyun amma ba ya ta tata ya tare a bayan sirika, ya taka k'afa ma yaje ya gano d'akinta baije ba don tsabar tab'ewa da lalacewa, ci kanki kuwa Malam ba yace mata sai dai yai ta murmushi idan ta na yi ya nai mata uzurin k'wak'walwarta ta goce.

Cikin Maimuna na shiga wata tara cif, ta haifi kyakkyawar yarinyarta sankace ciya, da hak'oranta guda biyu na k'asa, tsakanin Abdullahi da Malam ban san wanda ya fi wani farin ciki ba, Malam fad'i yake an haifar masa jika 'Yar baiwa, mutane kuwa da wanda Maimuna ta sani da wanda ba ta sani ba sai tururuwar zuwa barka suke, wasu ma don suga hak'oran ne kawai yake kawo su, don duk wanda yazo sai ya d'aga bakin ya gani, sai dai kawai Maimuna ta yi murmushi.

Iya kuwa ko lek'owa taga jikarta ba ta yi ba, illa ma bak'in ciki da take kamar ranta zai fita, saboda yadda taga malam ya na rawar k'afa ya samu jika 'Yar baiwa, don har ya siyo raguna biyu tik'a² ya tirkesu bakin nan yak'i rufuwa, Iya kuwa tace.
"Inma za ka daina farin ciki ka daina, shawara nake baku ku d'auki 'yar nan ku kaita bakin ruwa don wallahi 'yar aljanu ce ba 'yar baiwa ba. “
Murmushi kawai Malam ya yi baice da ita komai ba don ya san bak'in ciki ne ya taru yai mata yawa.
Ansha shagalin suna yadda ba kwa zato, yarinya taci sunan babar Malam AYSHA, Maimuna tace a dinga kiranta da NUSRAT, yayin da Malam ya d'ebo soyayya,tattali gami da kulawa ya aza akan 'Yar baiwa.
Wata d'aya tsira Maryam ma ta haifi 'yarta mace taci sunan babar Yusuf RABEE'AH suke kiranta da HIDAYA.

Watan Nusrat uku a duniya Iya ta matsawa Ahmadu number sai ya k'ara aure, wata bazawara ce nan mak'otansu da take shigo mata, mijinta mutuwa ya yi kuma mai bala'in kud'i ne, siyayya take yowa Iya sosai da haka ta siyeta, don dama burinta kenan ta tirsasa d'an nata ya aureta, don ta tareshi da buk'atarta ya yi mata kaca² hakanne yasa ta biyo ta gurin Iya.
Don a samu zaman lafiya Malam yacewa Abdullahi ya aureta, itama ya bi zab'inta,ko a samu k'iyayyar da takewa Maimuna ta ragu, don fad'i take yaiwa mahaifinsa biyayya amman ita saboda bai d'auketa a bakin komai ba ya watsa mata k'asa a ido ta ya ya kwa za ta k'aunaci Maimuna?

Tun sanda aka saka ranar tarewar Bulki Malam da Abdullahi suke kwantarwa da Maimuna hankali ita kuma ta nuna musu hakan ba komai bane dama ai namiji mijin mace hud'u ne.
D'aki d'aya shi ya zama na Maimuna, d'aya na Abdullahi d'ayan kuma na Bulki.
Ranar juma'a aka d'aura auransu kuma a ranar ta tare, farin ciki gurin Iya ba'a magana kamar ta zuba ruwa a k'asa ta sha, tunda take ba ta tab'a taka gurinsu ba sai a ranar da aka kawo Bulki.
To zamansu dai ga shinan da dad'i babu dad'i a haka rayuwar take juyawa.
Shekarar Nusrat d'aya Maimuna ta sake haihuwar mace wacce taci sunan mahaifiyar Maimuna SAFIYYA suke kiranta SHUKHURA, wata uku tsira Bulki ma ta haifi 'yarta mace wacce taci sunan Iya na gaskiya ZAINAB suke kiranta da NIMHA, anan fa Iya ta baje kolin gata da soyayya, fad'i take yanzu ne aka haifa mata jika.
Tun haihuwar Shukhura sai da Maimuna ta shekara biyar kafin ta haifi wata macen aka saka mata NA'IMA suke kiranta da YUSRA, ita kuwa Bulki ba ta sake haihuwa ba tun daga kan Nimha.

Malam yadda kuka san bai da wata jika sai Nusrat, komai ya samu 'Yar baiwa, kayan ciye² kuwa sai ta rage ake samwa k'annenta, ta shak'u da kakan nata fiye da zatonku masu karatu, shima kuma ta shiga ransa sosai da sosai, ya na bata kulawa ne ba wai don fifici ko wani abuba, sai dai shi a ganinsa dole ne jikanka na fari ya banbanta da sauran, saboda gaba d'aya soyayyar da kakewa d'an naka kake 'yebowa ka aza a kansa.
Amman a gurin Iya da Bulki cin fuskane kawai, don a nuna ba'a son Nimha, hakan yasa suma suka d'auki dukkanin tsana suka d'ora akan Nusrat.


Nusrat Fara ce, amman farinta mai duhu ne, fuskarta siririya ce mai d'auke da siririn dogon hanci, idanuwanta suna da girma matsakaici masu shape d'in k'wan k'walati, cikin idonta fari ne tas ruwa ya kwanta a cikinsa mai maik'o, k'wayar idonta kuwa bak'a ce me silkin brown a ciki, bakinta d'an madai daici ne haka zalika lab'b'anta basu da wani tudu, ko ya ta motsa bakinta wani siririn dimple ne ke bayyana a gefen kumatunta na tsaye wanda yake k'ara fito da zallar kyahunta.
Shukhura kuwa fara ce k'al, suna yanayi da Nusrat, amman ta fi Nusrat kyau, kina ganinta kai tsaye za ki kirata kyakkyawa, saboda ita ko ba tai murmushi ba kumatunta a lotse yake, kuma nata irin na kwance ne.
Yusra ma fara ce kamar Shukhura, itama ta na yanayi da su, amman kuma ba ta da dimple.

A yanzu shekarun Nusrat goma sha biyar a duniya, ta na sss1, su Shukhura kuma shekarunsu goma sha hud'u suna jss 3
auta Yusra kuma shakarunta tara a duniya ta na aji hud'u a primary.
Allah ya yiwa Malam rasuwa shekaru hud'u da suka wuce bayan ya yi jinya kad'an, kowa ya ji babu dad'i domin anyi babban rashi mai girma, musamman Nusrat, bayan mutuwarsa ne kuma soyayyar da Abdullahi wanda yanzu suke kira da Baba yakewa Nusrat ta fara bayyana, don har ga Allah ya fi k'aunarta ya na b'oyewa ne saboda kada ya kuma janyo mata bak'in jini.
mutum ne me wadatar zuciya, ba wani k'arfi ne da shi ba sai dai rufin asiri na Ubangiji, don sun wuce cin yau da na gobe a gidansa, haka zalika bai bar iyalansa a wulak'ance ba, a ko da yaushe za ka samesu cikin kyakkyawar kamala.

Shamsu ya yi aure da matarsa Fiddausi da d'iyarsu Amima sa'ar yusra, sunanta na gaskiya Zainab, shima Iya ya yiwa takwara, a kaduna suke a zaune a saboda anan ne yake aiki, ya ninka yayan nasa sosai a fannin dukiya wanda k'arara Iya ke nuna banbanci tsakaninsu da Baba.
Aunty Maryam kuma mijinta ya koma kano da aiki don haka ya d'ebe su suka koma kano da zama, 'ya'yansu hud'u yanzu, Hidaya, Abdul, Hibba, Abbas, suma sosai Iya take ji da su saboda suma mahaifinsu na da kud'i, kuma anai mata aike akan kari.


*Wannan kenan*

300 za ku biya domin samunsa cikin sauk'i.
0567838462
NABABA FADILA SHU'AIB GTBANK
in kuma katin waya ne ki turo ta wannan layin, shaidarki ta biya ma ki turo cikinta.
09037093702
In katin wayane 400 zaku biya.




Garab'asa gareku masoyana, duk wacce ta sayi wannan littafin za ta sami wanda zan rubuta gaba kyauta, ban yadda ki sayi littafina ki dinga turawa gruop ba, in hakan za kiyi ki sameni a layina muyi magana.




Allah ka k'arawa mahaifanmu lafiya da nisan kwana.


#Team KTG
#N.W.A
[10/8, 3:42 PM] Binta Lawan: *BEBE'ARTH*


Wattpad@Rashuna


*KATANGA*


____________
*TWO*
Yau ta kama lahadi, duk da suna cikin hutun makarantar boko, su Nusrat duk sun tsefe kawunansu zasu kitso, sai da Nusrat ta fara wanka ta yiwa Yusra ma ta wanke mata kanta ta taje ta shafe mata shi da mai sannan suka shirya zasu tafi, kallon Shukhura Mama ta yi da ta saka hijabi zasu tafi tace.
"Ke yanzu ba za ki wankan ba haka za ki bisu?“
Sai da ta fara turo baki gaba kana tace.
"To Mama nan da nan d'in sai na yi wanka, abinda yanzun nan za'a mana mu dawo. “
"Allah ya shirya. “
Mama kawai tace ta na mik'awa Nusrat kud'in kitson nasu had'e da fad'in.
"Ta fara yi miki kitson, kuma tai miki manya don kinsan yadda yawan kanki yake, kuma ke zan barwa girkin dare don fita zan yi, saura kuma kice a fara yiwa Yusra don na san hali. “
Murmushi Nusrat ta yi, bayan ta saka hannu biyu ta anshi kud'in kana tace.
"Mun tafi.“
Maman tace.
"Allah ya tsare, ku dai yi addu'a kafin ku fita. “Tace.
"Amin, tom insha Allah.“ Tare da jan hannun Yusra suka bi bayan Shukhura da ta fita tun d'azu.

Har sun d'an gota gurin Iya ta hango giftawarsu da sauri ta k'walowa Nusrat kira.
"Ke ke A'i zo nan. “
Da yake haka take kiranta tun ma Malam na raye, juyowa Nusrat ta yi, Yusra ta turo baki gaba tace.
"Wallahi na san aiki za ta sakaki, kawai kizo mui tafiyarmu mu rabu da ita.“
Murmushi Nusrat ta yi tace.
"Bara dai naje na ji kiran da take mini.“
"Tak'i ta rabu da ni d'in, shegiya ifrituwa me zunb'utun baki. “
Suka jiyo muryar Iya daga ciki, kuma turo baki Yusra ta yi ta na hararar gurin kafin ta fice waje da sauri, Nusrat kuma ta nufi gurin Iyan ta na murmushi.
Gyaran d'aki tace tai mata da wankin band'aki sai 'yan tsunmokaranta ma da tace ta wanke mata.



Kallon Shukhura Nana me kitso ta yi tace.
"Ina su Yayar taku?“
"Ga sunan suna hanya. “
"To shiga ciki, gani nan bari na k'arasa sharar nan. “
Rufe bakinta kenan Yusra ta yi sallama, kallon ta Shukhura ta yi bayan ta amsa sallamar ta ta tace.
"Ina Yayarmun?“
"Ba Iya ce ta kirata ba, har ta na ce mini ifrituwa. “
Wani haushi ne ya kama Shukhura, ta zura takalminta ta fasa shiga d'akin ta fice a fusace Yusra ta biyo bayanta.

Kamar an jefota ta shigo ta na kallon Nusrat da ke zubar da shara.
"Sannu"
Tace mata, kafin ta shige zuwa gurin Iya, iya na ganinta ta d'aure b'arin goron da ta b'antara a gefen zaninta kana tace.
"To rasa kunya b'eran tanka, kinzo kimin rashin kunyar taki ne? “
Kar katar da kai Shukhura ta yi tace.
"Ashe 'Yar aljanu na da rana tun da har an iya sakata aiki, me yasa ba ki kirawo 'yar lelen taki tai miki ba sai ita za ki saka, amma in abu zaki bayar babu wanda ke gabanki sai Nimha, amman in aikine sai wacce kika raina, don kin san Nimha ko tsintsiya ba za ta iya d'aga miki...


Read / Download KATANGA

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album