Join Our WhatsApp Group

NAZLAH Complete Hausa Novel Document by NAZLAH


NAZLAH

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 29808



NAZLAH

Reading Time: 2 Hours

Added On: 27, Nov 2023

Author: Salmaji Yar Lelen Royal Star ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION

Author Phone : 07033371851

Book License : Paid

Category: Love Novels

File Size: 167.25 kb

File Type: txt

Views: 613+

Download: 334+

Last download: 2 hours ago

Description/Story: [11/27, 7:15 PM] Masoyiya💖💖💖💖: ☘️☘️NAZLAH☘️☘️



*DAGA ALƘALAMIN*


SALMAJI / ƳAR LELEN ROYAL STAR CE🧚‍♀️🧚‍♀️🧚‍♀️






*WANNAN LITTAFIN TUN DAGA FARKINSA HAR KARSHENSHI SADAUKARWA NE GA YAYATAH (MARYAM YUSUF) WANNAN LITTAFIN WAKE NA RUBUTASHI , ALLAH YA RAYA MIKI ZURI'ARKI, YA KUMA KARA RUFA MIKI ASIRI DUNIYA DA LAHEERA..........*




*WANNAN LITTAFIN NA KUƊI NE #200 NE KUƊINSA KI DAURE HAJIYA KI BIYA NAKI, DOMIN SHAN KARATUNKI CIKIN KWANCIYAR HANKALI......*




*🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟*
{R.S.W.A}

https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad’akarwa, ilimantarwa da kuma nishad’antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad’ai ke maganin k’ishi_

*Alk’alaminmu ‘yancinmu*



*BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*( DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN KAI, YAH RAB YARDA NA FARA LITTAFIN NAN LAFIYA KASA NA KARESHI LAFIYA, ALFARMAR ANNABI DA AL-QUR'ANI)




3-4.





"""""""""""""""""Ba sai kin kara fada min komai ba, ai dama bakyason laifinsa duk ranar da baƙin cikinsa ko muguntarsa suka kasheki zaki gane mugun halayarsa",,ta fada tana taimaka mata, shi kuwa jin hayaniya ta kara yawa a kansa yasa yace "Wai ha haka ne, ke meyasa jaka ce, duk yarda na fada miko magana bakyaji, ko kullum kinfi son nayi ta dukanki sai kace jaka, kina cikin wannan halin ma ba zaki tausayawa kanki ba Mutswwww" ya ƙarasa fada yana jaan tsaki.........






Haushi kamar zai kashe Iya,, cikin fusata tace "Uwar kace Jaka, kai dama ashe har yanzu halinka bai chanja ba, ina ga bayan shaye-shayen da kakeyi har da ciwon hauka ya kamaka", ta fada tana ɗankara mishi dakuwa...........





sosa kanshi ya yi, tare da cewa, "Au wai da Iya ce", banza tayi dashi, ganin ya yi zaune yasa tace "Malam ka bamu guri dan Allah", sumi-sumi ya wuce daga ɗakin yana wani haɗa hanya, yanayin tafiyarsi kawai zaka kalla kasan shi din Dan shaye-shaye ne ma bugawa a jarida................





mayar da hankali Iya tayi akan Maryama da take ta uban nishi, ruwan rubutun da tazo dashi ta fasa ledar tare da sanya mata a baki, sha ta fara yi cikin fita hayyaci, bayan ta gama sha , ta shafe mata tun daga saman cikinta har ƙasan mararta da ruwab rubutun, cikin ƙanƙanin lokaci Naƙuda ta tahau gadan-,gadan cikin mintuna da bazasu wuce 20 ba Allah ya sauketa lafiya, tana haihuwa ta matsa daga kusa da Yarinyar da take tsanyara kuka ta kwanta tana sauke numfashi, wani bacci mai mugun nauyi ne ya yi Awan gaba da ita.............






Gyara Yarinyar da take tsala kuka Iya tayi tare da ajiyeta gefe, kayan jinin ta fita dasu, sai da ta daura ruwan zafi akan katon murhun da yake tsakar gidan kafin ta ci gaba da wanke kayan da aka ɓata, lokacin da ta gama wankewa ruwan zafin ya yi zafi sosai, ɗiba tayi tare da shiga dashi ciki, kyakyawar jaririyar da take kwance idanunta kyarrr tana kallon sama ta dauka, tare da yin bissimillah ta fara dan shafo ruwa da hannunta ta goga mata, wani jalar kuka mai firgitarwa ta tsanyara, wanda yasa ita kanta Iyar sai da taji tsoro.............




ganin babu abin da ya sameta, yasa taci gaba da mata wankan, tana dan murmushi, gani Yaringar Sak Uwata ta biyo komai, sai dai har tafi Uwarta fari, dan ita wannan fara ce mai sirkin jaa-jaa kalar dai fatar turawa.............




bayan ta gama mata komai, ta Ajiyeta domin zuwa ta dauko wani kwalli da ta daka domin ringawa Jaririyar Amfani dashi, tana ajiyeta ta sanya kuka, ficewa tayi da sauri domin zuwa ɗakkowa, tana fita Lawan na shigowa, direct dakin ya nufa, in da yake jin kukan Yarinyar yake kallo sai dai bai ga Yarinyar ba, hakan yasa ya yi kan Maryama da take kwance tana baccin wahala, ƙafarshi yasa ya fara shurin hannunta tare da cewa "Ke! ke!! ke!!! ke ki tashi ki dauke wannan Aljanar Yar taki ", ya fada yana zama, dakyar ta mike ta nufi inda takejin kukan yarinyar ..............





laluɓawa ta farayi har ta samu inda take, raɓata jikinta tayi, tuni tayi tsiit kamar wadda akace wa Mamarta ce ta dauketa, ba'a dau lokaci ba Iya ta dawo da tandun kwallin sanya mata tayi, tare da mikawa Lawan ita tace "kar ɓeta ka riketa zamu shiga wanka", tana daurata kan hannun Lawan ta fasa kara da kuka sosai, kallon Iyar ya yi tare da cewa "Iya kuka take,kuma ni wlh banason kukan Yara", harara ta dalla mishi tare da cewa "Nima ai haka nasha wahalar kukanka dan haka ka ɗana", ta fada tana jaan hannun Maryam , tsakar gidansu dake kwal-kwal a shere suka fito, kama hannunta Iya tayi suka shiga bandakin da yake fes shima yasha shara.............






Wankan Runhu Iya tawa Maryama , ai kuwa kafih su fito har ruwan nono ya sauka sosai, har tana ji yana dan zubar mata, har kuma suka fito daga wankan Yarinyar nata tsala ihu iya karfinta..................






da kanta ta taka ta nufi cikin ɗakin, Tabar Iya waje, tana shiga yace "Ungo wannan Yar mai masifar kuka", jikinta har rawa yake takarɓeta, ɗiwawunta ta fara neman inda zata ɗosana, zama tayi kusa dashi kaɗan dan ba duka tama zauna ba, tsawa ya daka mata tare da cewa "sauka! sauka salon ki zubamin ƙazanta a saman gado, to wallahi har ki yaye na haramta miki hawanshi", da sauri ta zauna ƙasa, Iya ce ta shigo, ɗakin hannunta dauke da kaskon wuta rushi ringis a cikinshi jaajir, akiyewa tayi tare da komawa ta ɗauko faranti, ajiyewa tayi tare da cewa "ke baki da hsnkali ne kike zama ƙasa, daga haihuwarki yau, salon kije ki janyo mana wata matsalar", ta fada tana kallonta, dan murmushi tayi tare da cewa "ba komai a ƙasan fa Iya", shiru Iya tayi dan tasan ba kowa zai hanata hawa gadon ba sai Lawan..........




"to taho Maryama kici Abin ci", matsawa tayi gurin Iyar tayi, bde mata kwanon tuwan dawo da miyar kuka tayi, miyar taji haɗi ga ƙanshin man shanu na tashi sosai,kallon Iya Lawan Ya yi tare da cewa "Iya ni ina nawa ?" sakin baki tayi tana kallonshi, sai kuma tace " ni nace kaje ka buga chacha da kuɗin da zaka ci abin ci dan haka sai ka nema", shiru ya yi yana kallon tuwon da ba ƙaramin bi dashi ya yi ga..........






Haleeem da ya shigo dakin ta jawo jikinta tare sa fara bashi abincin yana ci yana shafa kan baby gal din da yake luluɓe da gashi baki siɗik mai yawa sosai, ganin komai normal yasa Iya mikewa ta tafi gida, tana fita ya diro daga kan gadon, anshe tuwon ya yi, tare da komawa gefe ya ci gaba da ci, ba tare da tunaniin sun koshi ba ko basu koshi ba ...............






ganin gari na walkiya yasa ta mike ta fara shiryawa cikin kodaɗɗun kayanta, wata tsohuwar rigar Haleeem ta dauka ta sanyawa babyn tare da luluɓeta, shimfiɗa ta shiga yi musu a ƙasan sumintin cikin ɗakin, kafin ta gama Haleeem ya yu bacci gyara mishi kwanciya tayi tare da kwanciya itama, tana kwanciya ruwan sama mai karfi ya tsuge, ruwan aka fara mai karfin kamar zai ɗaye rufin kwanukan mutane ya tafi da su..............





luluɓe Haleeem tayi da kyau, tare da daura baby'n akan kirjinta ta luluɓe sosai, kasantuwar kayan jikinta ba wani na kirki bane yasa sanyin da akeyi take busu mata, sanyi ne ya kamata kyarma ta soma yi, gashi ɗakin babu ko abun rufewa balle ta rude, labulen kuwa irin boka-bokan nan ne, ba wani na kirki ba , kyarma jikinta yakeyi, Addu'o'i ta fara yi, tana riƙe da yarinyar a kirjinta, an dade sosai ana ruwan kafin ya fara tsagaitawa.............

.





Har suka kawo wani gida mai kyau wanda yaso fin wanchan gidan da suka baro kyau, amma bai daga kanshi ba ya kalli ko hanya, a haka har suka ƙaraso gida, shima gidan sojoji ne suke tsare dashi, sai da suka dai-daita parking a tsakiyar gidan, ficewa duk sukayi motar suka bude mishi, kafin suka tsaya suna sarawa motar, ya jima kafin ya zuro kyawawan fararen ƙafafunshi waje,cikin izza da taƙama, ya fito tare da nufar wata ƙofar glass , yana tsayawa kofar ta bude, wani ƙayataccen palo mai kyau ne ya bayyana, shiga ya yi, da Sallama , wata hamshaƙiyar Mace ce da taci wani dan ubansu lass, mai kyau kallo daya zaka mishi kasan cewa ba ƙananan kuɗi aka kashe ba gurin sinyanshi.................





Amsa Sallamar tayi, tana murmushi, mikewa tayi tare da cewa "Sannu da zuwa Auta
", murmushi ya yi, tare da tsugunnawa har ƙasa ya gaisheta, amsawa tayi tare da cewa "nasan bakayi break ba kaje kayi kafin mu tafi", girgiza kanshi ya yi, tare da cewa "Na koshi", kallon tuhuma ta mishi, ganin ya ɗukar da kanshi alamar bayason ta kara mishi wata magana, yasa ta mike tare da daukar mayafinta da jakarta dake kusa da ita tare da cewa "Haleesa ki fito mu tafi, muje", mikewa ya yi, yana gaba tana bayanshi, har suka ƙarasa gurin mota, shi da kanshi ya bude mata mota ta shiga kafin shima ya zagaya, bude mishi akayi ya shiga driver yaja motar Escort dinau na bayansu da gabansu...........





tunda suka shiga motar babu wanda ya yi, magana dan shi lumshe idanunshi ma ya yi, yana saurarar karatun Al-qur'anin da yake tashi cikin motar, a haka suke tafiyar cikin kwanciyar hankali..............






kusan 3 hours suna tafiya kafin su karaso, wani gari mai suna Lambar Ƙunci, tafiya suka ci gaba dayi har suka karaso Shuwaki, shigarsu cikin garin yasa suka fara yin slow down da motar dan sun iso cikim garin da zasuzo, tafiyar five minutes ce ta ƙaraso dasu ƙofar wani gida mai matsakaicin kyau, shi ba na talakawa ba shi kuma bana masu kuɗi chan ba................





Wani dan tsoho ne ya tashi yana cewa, "iyeee wa nake gani haka kamar mutanan Katsina", ya fada yana washe bakinshi, yar dariya suka yi Hajiya ce tace,"aikam dai Mune Kawu ya gidan", murmushi ya yi tare da cewa "lafiya lau kuwa, wa nake gani kamar Soja marmari daga nesa ", murmushi Hamid ya yi, dan shi bai fiye dariya ba sai dai murmushi," ah'ah wannan marmari ne daga kusa ", dariya duka sukayi, kafin su wuce ciki.................





Suna shiga cikim gidan akayo musu chaaaa, Yaran ne suka rungume Hajiya suna cewa "Ga Yayah Hauwa! ga Yayah Hauwa" dariya tayi tare da cewa "Eyyi Yara sun girma kalli yarda Amina da Maryam suka wani zanƙale sukayi girma, har sunfi Haleesa girma"ta fada tana shafa kansu, dariya duk sukayi, suna boye fuska, Hannu Haleesa wata Yarinya wadda ba zata wuce sa'annin Haleesar ba tayi, murmushi Haleesa tayi tare da cewa "Aminannure", harararta tayi tare da cewa, "kar fa ki manta ni Mamarki ce", dariya duka aka kwashe da ita tare da cewa, "Eyyi ai sai fa Mama", tura baki Amina tayi tare da cewa, "nan gaba mai sai kin tɗringa gaisheni Yarinya", ana dariya aka shimfaɗa musu taburma, zama sukayi sai da suka zauna kafin matan gidan su Ukku su haɗa baki gurin cewa "Wai Yau Mai gidan ne yazo, tab lallai yau akwai cefane kenan" suka fada suna dariya.........




"Ni ne fa Yau nazo naga Matana"Hamid ya fada yana murmushi, fira suka shiga yi, Haleesa kuwa tana chan ta shige cikin su Amina da Maryam suna ta fira...........




Basu jima da shiga cikin gidan ba, aka fara shigowa da kayayyakin abin ci lemuka kwalayen biscuits da dai sauransu, murna Yaran suka shiga yi suna tsalle, sun jima sosai, kafin Hajiyar tace "Zamuje gidan Bava Balki amma kafin mu tafi zamu dawo", har ƙofar gida haka suka rakasu, mota suka shiga suka wuce, basuyi wata tafiya sosai ba suka ƙaraso gidan Ya'u Tela, cikin farin ciki suma suka karɓesu Baba Balki Kanwar Baban Hajiya sai Tsokanar Haleesa da Hamid takeyi,Mijinta da kishiyarta kuwa sai nan nan sukeyi dasu, suma haka aka dire musu kayan arziki sosai kafin su ce zasu tafi , Kallon Hajiya Baaba Balki tayi tare da cewa "Ni kam Hauwa'u yaushe zakije gurin su Rafan Habu ?" murmushi tayi tare da cewa "ai ban ma jima da zuwa ba sai bikin Yarinyar Yayah Hadiza zan koma", "to shi kenan ki gaishesu in kinje", jinjina kanta kawai tayi............





mikewa sukayi zasu fita, suna fita suka haɗu da wani katon mutum mai jiki sosai , sai dai ya manyata sosai, yana kan mashin gabanshi rungume da bangajin tsire, cike da murna ya tsaya dan yasan yau kakarshi ta yanke saƙa, gaisawa suka shiga yi , cike da jin kunya Hajiya tace "yanzu dama zamuje gidan ai yan gidan nanan ko ?", ta fada tana kallonshi, "E muje Kudidi nan kuwa, " "to shi kenan muje" Sallama sukayi da Baba balki tare da bin bayanshi zuwa gidan................





...


Read / Download NAZLAH

START READING

OR

DOWNLOAD TXT NOW
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album