Join Our WhatsApp Group

ABULLE TA MAI UNGUWA Complete Hausa Novel Document by ABULLE TA MAI UNGUWA


ABULLE TA MAI UNGUWA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 48288



ABULLE TA MAI UNGUWA

Reading Time: 4 Hours

Added On: 06, Apr 2023

Author: Ummyn Yusra ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Paid

Category: Love Novels

File Size: 246.24 kb

File Type: txt

Views: 2025+

Download: 680+

Last download: 3 hours ago

Description/Story: https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
[9/5, 10:15 AM] Ummyn Yusrah🧕🏻: *ABULLE TA MAI UNGUWA*

_Rubutawa_
_Ummyn Yusrah_


_Gajeren labari domin nishaɗi_


*Garin Jinjin*

_Ƙaramar hukumar Mai Ludaya_

_Yammaci lis!_

_Fadar mai unguwa_

1

Mai unguwa ne zaune kan kujerarsa, yayin da sauran jama ar fada ke kewaye da shi kan wata ƙatuwar tabarmar ana ta hira da mai da zance.

Tunda suka doso fadar idon mai unguwa ke kanta.

Kanta ɗauke da tiren talla, kunkumin nan an ɗaureshi tamau da gyale, ga fuskarka ta sha kwalliya da fauda buda jaka.

Masifa kawai ta ke ta zubawa har bakinta na kumfa.

"Karime Wallah gobe sai na ci uwar Indo, hegiya kucaka ta rasa wa za ta yi zance da shi sai Hamusu rabun raina! Ke alƙur an ji nake kamar na kifar da kayan tallar nan na je na ragargaji tsinanniya."

"Yo ke Abuwa tun yaushe na ke gaya miki ki rabu da tsinanniya? Shegen kwashe-kwashe irin naki yasa ki ka kwaso mai ƙwatar miki masoyi. Yo ni ban isheki ƙawance ba ne?"

Kallon sama da ƙasa ta yi mata ta keɓe baki

"Taɓ! Kin manta ita ɗin ƴar waye? Ƴar gidan mai unguwa ce fa! Duk sati ranar juma'a sai mun je cin hinkafa gidansu. Ke ko sau ɗaya aka taɓa dafata gidanku. Shima albarkacin yayanku ya bi doguwar mota ya yi kabo-kabo zuwa burni ya auno muku ita."

Cikin yanayin jin haushi ta ce
"Shegiya kwaɗayayya, ai ke wallahi kin ji jiki. Dama tunda naga kin liƙe mata nasan da biyu ne, shiyasa duk ranar juma a kike korata idan na biyo miki yawon juma a. Har kike wani cewa sau ɗaya kika taɓa ci a gidan mu. Ke sau nawa na ci a gidanku?"

"Ko sau ɗaya. Amma ai kina zuwa kwaɗayin tuwan biski da miyar ja."

"Aikin banza! Abunda sai a share mako uku ko hudu ma ba ai ba, duk ranar ko da a ka yi ƴar hali ki ke yi mun, kin yi ta haɗe fuska kenan kuna kumbura kamar Fanken Dudu na bakin kasuwa."

"Kam bala i! Nice Fanken Dudun Yasin sai na hau kan gandar bakinki na yi luguden leɓe, yar jakar ub..." Ta sauƙe tiren tallan dafaffiyar gyaɗar ta ta nufota gadan-gadan za ta cafko ta, da sauri ta matsa can gefe tana faɗin

"Idan na tsaya kenan za ki yi luguden ko? Ai wallahi ke da Indo ne sai na faɗa mata kwaɗayi ki ke zuwa yi gidansu."


_Ya a ci gaba?_😃
[9/5, 10:15 AM] Ummyn Yusrah🧕🏻: *ABULLE TA MAI UNGUWA*

_Rubutawa_
_Ummyn Yusrah_


_Godiya mai yawa da Addu'o'inku_

3

"Kai! Kun raba mana hankali, maganar wa za mu ɗauka cikinku?" Ɗaya daga cikin jama ar ya daka musu tsawa. "Cewa ta yi Inno Mai Ƙosai." "Ƙarya ta ke yi, ita ta fara cewa Talatuwa mai Tafasa." Sarkin fada ya ce "Yau naga shashanci gurin yara. To ai abun alfahari ne a san mutum asan sana a tasa, naga duk faɗin unguwar nan da Inno Mai Ƙosai ake ƙiranta, ita kuma Talatuwa mai Tafasa. Duk ai sana ar tasu ta gado ne, shine har kuke husuma a kai don an ƙira sunansa?" Liman da ke zaune gefen hannun damar mai gari ya zuba ma yaran ido, ya kaɗe idonshi guɗa ɗaya na dama, yana nunasu da yatsa ƴar manuniya da ke hannun dama ya ce "Wai wannan kam ba Abuwa bace ƴar gidan Ilu mai Amalanke?" Sarkin fada ya amsa yana mai jijjiga kai kamar riƙaƙen gadangare "Ita ce fa! Ai fitinaniyar yarinya ce. Waccar kuma Karime ce ƴar gidan Mudi mai jaki." "Ikon Allah! To, mai Ilun yake jira da bai sallamata ba? Duba fa, duk ta ƙere sa anninta a girma." "Man liman ai yariyar saurin girma ne da ita kamar wani kaji da na gani a can Binni, cikin garin Jinjin, wai kajin turawa, can garin yahudu da nasara a ke kawo su, haka nan suke gaɓa-gaɓa. Girma ba hankali." "To, ai kam gara ya miƙata, tun kafin a fara sata cikin waƙa. Wannan ai abun kunya ne ma a gareshi. Ƴa ta kai har wannan lokacin." "Ai kam! Sa ar fa Huwaila ce ta wajena. Yanzu suke shiga shekara na sha uku, amma kaga ita Huwaila ai bata kai ta ba, nan da mako biyu ne ma za a kai ta ɗaki." "Ikon Allah!" Duk ka-ce-na-ce ɗin da ake Mai Unguwa nashi ido, don ya ma rasa ta cewa. Hasalima tunanin shi daban ne. "Ke me ya haɗa ku da Indo ƴar gidan Mai Unguwar?" Ɗago kai ta yi sai hawaye sharrrr! "Ba komai." "Da gani ba ki da gaskiya, domin duk wani mai saurin kuka rashin gaskiya ne da shi." "A a, dama... Dam...!" "Dama me? Ke Karime, me ya haɗa su da Indon?" Gyara zama ta yi, kamar dama jira take. Nan ta ɗauko zance tun daga tushe har zuwa ƙarshe.

Salallami gurin ya ɗauka da. Sarkin fada ya ce "Ikon Allah! Ke kuma haka Allah ya yo ki da kwaɗayin hinkahwa? Yo in ba gidan Mai Unguwar ba, ina ake dafa ta? Shima dai albarkacin dangantakar da ke tsakaninsu da kansilan yankin Mai Auduga ne yake kawo mishi shi, wataran a turo ƴar Kwafarati wataran ƴar Hausa. Shine har za ki ɗarsa rayinki a kai? Ikon Allah." "Kwankwatsi ƙarya ta ke yi mini. Ba haka nan bane." "Rufe mana baki ja irar yarinya kawa..." Mai Unguwa ne ya katseshi yana faɗin "Ku barsu haka nan, ku kuma kada na kuma jin kun yi hayaniya a tsakaninku. Maza tashi ku tai." Jiki na rawa duk suka miƙe, kowa ta sunkuci kayan tallarta. Canza hanya su ka yi, sai da su ka daina hango fadar Mai Unguwa Abuwa ta ce "Yasin da an dokeni kanki zan rama." "Yo ko da ba a dokeki ɗin ba ai kin ɓare baki kamar ɓaure kina ta sharɓar kuka, Tuɓu luɓus kawai, mai kama da kazar masu jajayen kunnuwa." Tana kaiwa nan ta sa gudu. "Hegiya da ƙafa kamar Mazarin tsire. Za mu haɗu da dare a dandali."




_Ummyn Yusrah_
[9/5, 10:15 AM] Ummyn Yusrah🧕🏻: *ABULLE TA MAI UNGUWA*


_Rubutawa_
_Ummyn Yusrah_


_To, ga ci gaban._

2

"Idan kin fasa faɗa mata kin raina Talatuwa mai Tafasa!"

"Ko kuma Inno mai Ƙosai ba!"

"Kam bala in can! Innar tawa?" "Ita dai, ai uwa ba ta fi uwa ba."

Har zuƙowa ta yi, itama Karime ta dire kwanon tallarta . "Zo mana! Kada ki ganki haka gaɓa-gaɓa ki ɗauka tsoron ki na ke, Aradu idan ban kwasheki na laftaki a ƙar ba."

"Kai! Kai!! Kai!! Kai!!! Kunga ƴan nema, me ya haɗaku kuma?"

Abuwa da takaici ya gama cikata, na rashin luguɗen leɓen da ba ta samu ta yi a kan gadar Bakin Karime ba ta ce.

"Ƙiran sunan Inna ta ta yi." Tana faɗa tana hararar Karimen, kamar wacce idanunta zai zazzago ƙasa don harara. Ga wani ƙarin takaicin ma da ta ƙirata da sunan da ta fi tsana (Gaɓa-gaɓa.)

"Ƙarya ta ke yi Baban Lanti. Ita ta fara ƙiran sunan uwata."

"Ya isa, ku wuce mu je, tun ɗazu Mai unguwa ke hango hayaniyar da ku ke, da ya ke ku ba ku san zuru ba sai an tanka shine ku ka ci gaba ko? Za ku yi bayani ne."
Jin Mai unguwa ne ya turo ƙiransu duk hanjin cikinsu ya kaɗa, tsoronsu ɗaya kada ya ƙira musu tsabga, don wannan baƙin mugun idan ya riƙe mutum da dorinar nan tashi ba ƙaramin jibgar mutum ya ke ba.

Nan suka bar kayan tallar suka ranƙaya gaban mai unguwa.

Ɗan aiken ya gurfana gaban Mai Unguwa yana mai dunƙule yatsun hannunshi na dama, yayin da ya ɗaga babbar yatsarshi yana mai jinjina wa Mai Unguwar yana faɗin "Ranka shi daɗe! ga yaran nan na taho da su."
Ya ƙarashe maganar yana mai nuna su Abuwa da Karime da ke durƙushe can a ƙasa, duk sun yi tsuru-tsuru, kamar wanda su ka kar uwar Mai Unguwa.

Sai da ya ɗan ɗau lokaci kafi ya fara magana cikin isa da mulki "Menene ya faru ku ke ta sa insa a tsakaninku tun ɗazu?" Shiru su ka yi ba amsa

Tsawa mahukuncin fadar ya daka musu yana mai nuna su da miƙaƙƙiyar doninarshi ya ce,
"Ba Magana a ke yi maku ba ne? Ko nan ma rashin kunyar za ku yi mana? Ahir ku kula, fada ku ke."

"A...A...Ab!"
"Ta ce me? Kin bi kin ishemu da in ina." "Cewa ta yi wai Indon gidan Mai Unguwa ta..." "Ƙarya ta ke kwarankwatsa. Sunan Innata ta ƙira." "Ƙarya ta ke, ita fa fara ƙiran sunan tawa uwar."

Duk suka karaɗe wajen da hayaniya, da wannan ta ɗauko zance sai wannan ta katse, musamman ma Abuwa da ta ke tsoron tonon tonon asirinta.



_Mu haɗe a gaba_
[9/5, 10:15 AM] Ummyn Yusrah🧕🏻: *ABULLE TA MAI UNGUWA*

_Rubutawa_
   _Ummyn Yusrah_

_Tsangayar Marubuta da ke fuskar littafi ina miƙo jinjina da fatar alkairi gareku._

4

Da ɗai-ɗai mutanen da ke fadar Mai Unguwa suke tafiya, har ya rage saura Mai Unguwa da sarkin fada. Sunkuyowa yayi da kanshi saitin fuskarka Sarkin fadan.

"Kai! Wannan yarinyar ƴar gidan Ilu mai Amalanke nan fa kalar mu ce."  Zaro ido ya yi, cike mamaki ya ce "Ranka shi daɗe! Wannan ai ta yi ƙarama, duka-duka nawa take."  "Ka ji shashanci! Ita Abullen ba za ta zauna ba ne idan an kai ta ɗaki ko me ka ke nufi Kallamu?"  "Ahh! Zama kai, daram ma kuwa. Kawai dai gani na yi ta ƙawar Indo ce ta wajenka kuma ƴar autar gidan ka."  Ɗagowa ya yi, ya na ƙare ma Sarkin fada kallo  "Ahir ka iyar ma bakinka. Ka je ka sami Ilun ka gaya mishi idan bai bada ita Abuwar ba ina ciki." "An gama ranka shi daɗe!" Har ya fara tafiya sai kuma ya dawo ya durƙusa yana jinjina "Amma yallaɓai kana ga ita yarinyar za ta yarda?" Murmusawa ya yi har sai da jajayen haƙoranshi da suka gama rinewa da goro suka bayyana. "Yarda kam ai ta riga ta yi an gama. Kai dai je ka sanar ma Ilun. Ita da ke zuwa cin hinkahwa duk sati, ta samu a sati sau biyu ko uku ai kaga ta more, domin da zarar an yi auren nan za a dawo da girka ta sau biyu ko uku a sati don in samu ta zauna." Shima dariyar ya yi ya ce "Kuma fa haka ne yallaɓai! Na wuce ma, da zarar na yi sallar magariba zan wuce can ɗin." "To, madalla. A dawo lafiya."

"A ah! Yau kuma mutanen fadar Mai Unguwa ne a gidan namu?" Malam Ilu mai Amalanke ya faɗa lokacin da ya fito ƙofar gida bayan ɗan aike ya sanar ana nemanshi a ƙofar gida.

"Ranka shi daɗe nine da magaribar fari." Juyawa ya yi ya kalli gabas da yamma kudu da arewa "In ce dai Sarkin fada makuwa ya yi ko?" "Makuwa kuma? Mai ka gani?" "Ji na yi ka ƙirani da sunan manya." "Au! Wai da na ce Ranka ya daɗe? Ai ka dace da hakan ne. Ko za mu samu waje na musamman, domin muhimmin saƙo ne ke tafe da ni." "To! Allah dai yasa lafiya ba?" "Lafiya lau ma, sai alkairi." "To Madalla. Ina zuwa." Gida ya shiga ya ɗauko tabarma ya shimfiɗa a ƙarƙashin bishiyar darbejiyan da ke can gaba da gidan.

Bayan sun zauna, suka sake gaisawa gami da tambayar lafiyar iyalan da kuma harƙoƙinsu. Shiru ne ya gifta tsakani, kafin Sarkin fada ya katse shirun da faɗin.

"Mai Unguwa ne ya tasani ya ce in zo takanas ta kano, ƙafa da ƙafa in sameka in sanar kuma in yi maka albishir cewar idan ba a yi ma Abulle miji ba yana riƙo. Ya gani yana so." Ilu ya faɗaɗa fara arsa ya ce "Ikon Allah! Banda Mai Unguwa da abunshi ai Abulle ƴar shi ce, ko an bada ita ya ce ya mata miji ai da gudu za a ƙarɓo ta. Wa ma zai ƙi haɗa zuri a da jinin Mai Unguwa? Wanne ɗa ne ko jika za a ba Abullen daga ciki?" "A ah! Ɗa ko jika kuma? Ba ko ɗaya daga ciki." "To, wane ne daga cikin dangin nashi?" Yana maganar fuskarshi fal annuri. "Da alama dai ba ka fahimci maganar tawa ba. Shi Mai Unguwar ne ya gani ya ke so, ya kuma buƙaci a bashi auren ita Abullen." Cak! Numfashin shi da tunaninshi ya tsaya na wucin gadi.

Jin shirun da ya yi ba amsa yasa Sarkin fada gyaran murya ya ce "Malam Ilu na tare da ni kuwa?" "Ina tare da kai Sarkin fada." "To, me ka ce ne?" "Anya ko Abulle ta wajena ka ke magana kuwa?" "Ita ɗin ce dai, ai duk faɗin unguwar nan tamu ta Mai ludaya ita ake ƙira da Abulle ko Abuwa. Sai Zebu ƴar gidan Iro mai tumaki sai kuma Zinaru ƴar gidan Audu gurgu. Dukda sunayen nasu guda ne Zenabu amma ai da Inkiyar da ake ƙiran kowa." "To, amma ai ita Abuwar ba wata babba har can ba ne. Ina laifin Ma ƙaramin ɗan shi Mado da Indo ƙawar ita Abuwar ke bi ko dai wani daga cikin jikokinshi. Amma shi da kanshi ai ya girme mata nesa ba kusa ba." "To, shi aure ina ruwan hi da wani girma da tsufa ko shekaru? Zaman lafiya da kwanciyar hankali ake nema ai. Kada ka manta abunda ka ce, ba wanda zai ƙi haɗa zuri a da mai gari."

'Da ne da na fahimci maganar a baibai.'

"Haka ne. Yanzu a yi haƙuri aɗan bani lokaci in tuntuɓi ƴan uwana da uwar ƴar da ita ƴar, duk abunda muka yanke zan zo har fadar Mai Unguwar in sanar muku." "To, ba damuwa. Muna jira, fatan ba za a ɗau lokaci mai tsawo ba?" "Da ikon Allah." "To, Allah yasa mu ji alheri. Na barka lafiya. A gaida Iyalan da ita Abullen a ce mai unguwa yana miƙo gaisuwa."




_Ummyn Yusrah_
[9/5, 10:15 AM] Ummyn Yusrah🧕🏻: *ABULLE TA MAI UNGUWA*

_Ummyn yusrah_


_A ƙara yawan feji, a ƙara yawan feji. Duka-duka labarin fa bai wuce feji ɗaya ba idan na ƙara, ban son ya ƙare ne yasa na ke ta yi muku shi kaɗan-kaɗan domin nishaɗinku. Kawai a ci-gaba da gahi kawai._


5

Naɗe tabarmar ya yi ya nufi cikin gida ranshi ɓace, tunda ya shiga gidan ma bai iya zama ba. Jingina ya yi da zanar da aka zagayeshi da ɗakin. Inno da ta fito daga daki hannunta ɗauke da tire na kwano, an jere kwano tuwo da miya na ci ka duba da kofin ruwa shima na ci ka duban akai tana ƙoƙarin ƙiran ƙanin Abulle ya zo ya kai ma Babansu waje...


Read / Download ABULLE TA MAI UNGUWA

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album