Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

"[10/8, 3:42 PM] Binta Lawan: *BEBE'ARTH*


28/8/2020


Wattpad@Rashuna


*KATANGA*


_Ina matuk'ar godiya ga Allah (S.W.T) da zai ba ni ikon kawo muku wannan littafi mai suna KTG, ina fatan yadda zan fara cikin yalwatacciyar lafiya na kammalashi haka, Amin summa Amin_

_Sak'on gaisuwa ga 'yan uwa da abokan arzik'i, da kuma dukkanin masoyana na kusa da nesa, ina kuma fatan za ku bani had'in kai cikin wannan littafin, kalma d'aya kawai zan gaya muku, alk'alamin ya fi mashi tsini, kuyi k'ok'ari kui nitso ku ninkaya cikin wannan sabon alk'alamin mai suna *KATANGA*_

_Hak'k'in mallaka:_
*RABEE'AH SHU'AYB NABABA*
(RASHUNA)


____________
*ONE*

_Bismillahir rahamanir rahim._

*SHIMFID'A*
Malam Ahmadu an haifeshi a garin Zaria, asalin malantarsa ya gadota ne a gurin mahaifinsa Malam Buba, kasancewar kuma tun ya na yaro mahaifiyarsa ta rasu, tare ya rayu da mahaifinsa har sai da ya yi aure da matarsa Asabe sannan Allah ya karb'i ran malam Buba, daga nan Malam Ahmadu ya ci gaba da jan ragamar mahaifinsa ta malamta.
'Ya'ya uku Allah ya azurtasa da shi, Abdullahi, Maryam sai autansa Shamsu, Abdullahi shine ya gado mahaifinsa amman kuma ba a iya malamtar ya tsaya ba ya na da shago a kasuwa da yake sayar da kayan awo.
Malam Ahmadu shine ya zab'awa Abdullahi mata, 'yar amininsa ce k'ud da k'ud da Allah ya karb'i ransu shi da matarsa shekarun baya da suka wuce, kasancewar gidan nasu gidan yawane, kuma auran zumunci akayi tsakanin mahaifan nata, haka take ta watan gari riya a cikin gidan sai uwar bauta da take musu, tausayinta da duba maraicinta da amuntakar da ke tsakaninsa da mahaifinta hakanne yasa ya nemawa Abdullahi auranta, Abdullahi baiyi musu ba kasancewar ya yaba da d'abiunta kuma ta na yawan burgeshi a duk sailin da zasu had'u hakan yasa ya karb'i tayin auranta da hannu bibbiyu.

A gurin Asabe wacce yanzu suke kira da Iya aka fara samun k'alubale, inda ta yi tsalle ta dire akan d'anta ba zai auri 'yar makafi ba, kasancewar mahaifanta duk makafi ne, shikuwa Malam Ahmadu yace ta yi kad'an ta hana wannan auran, idan har taga ba'ayi sa ba to tabbas babu ransa a Duniya.
Abdullahi da Maimuna sun aminta da juna sosai ya yin da suka fad'a zazzafar soyayya nan da nan magabata suka shiga lamuran nasu, a lokacin ne kuma wanda yake neman auran Maryam me suna Yusuf ya fito, a kano yake a zaune aiki ne ya kawosa zaria, tun ganin farko da yaiwa Maryam ya aminta da ita, bai fara zuwa zance ba sai da Malam ya yi masa izini, daga bisani kuma yace ya turo magabatansa.
An tsayar da ranar auran Abdullahi da Maryam lokaci guda .
Anan cikin gidan, Malam Ahmadu ya yanki gefe ya yiwa Abdullahi gini, d'akuna uku ne maka² abinsa a wadace, ya yi musu kuma k'ofar gurinsu da ban, sannan kuma ya had'a masa lefe dai-dai da zamanin da suke ciki.
Ansha shagalin biki kafin a kawo amarya sashinta, ita kuma Maryam aka kaita unguwar Sabon gari.

Lafiya lau zaman Abdullahi da Maimuna yake babu wata matsala ko d'aya, Malam ya d'ebo soyayyar duniya ya d'orawa surukar tasa, kullum in zai shigo gida da abinda zai aika mata da shi, ya yin da Iya kuwa ta bi ta tsaneta, ko kad'an ba ta sakar mata fuska kyara da tsangwama shine tsakaninsu.
Wata d'aya da bikinsu Allah ya azurtata da samun juna biyu, tattali da kulawa fiye da wacce take samu ada Malam yake mata, idan ya fita duk abinda ya san me ciki na sha'awa shi yake siyo mata, Iya kuwa tayi ta sababi a tsakar gida ta na masifar ga d'iyarsa can ta na da juna biyun amma ba ya ta tata ya tare a bayan sirika, ya taka k'afa ma yaje ya gano d'akinta baije ba don tsabar tab'ewa da lalacewa, ci kanki kuwa Malam ba yace mata sai dai yai ta murmushi idan ta na yi ya nai mata uzurin k'wak'walwarta ta goce.

Cikin Maimuna na shiga wata tara cif, ta haifi kyakkyawar yarinyarta sankace ciya, da hak'oranta guda biyu na k'asa, tsakanin Abdullahi da Malam ban san wanda ya fi wani farin ciki ba, Malam fad'i yake an haifar masa jika 'Yar baiwa, mutane kuwa da wanda Maimuna ta sani da wanda ba ta sani ba sai tururuwar zuwa barka suke, wasu ma don suga hak'oran ne kawai yake kawo su, don duk wanda yazo sai ya d'aga bakin ya gani, sai dai kawai Maimuna ta yi murmushi.

Iya kuwa ko lek'owa taga jikarta ba ta yi ba, illa ma bak'in ciki da take kamar ranta zai fita, saboda yadda taga malam ya na rawar k'afa ya samu jika 'Yar baiwa, don har ya siyo raguna biyu tik'a² ya tirkesu bakin nan yak'i rufuwa, Iya kuwa tace.
"Inma za ka daina farin ciki ka daina, shawara nake baku ku d'auki 'yar nan ku kaita bakin ruwa don wallahi 'yar aljanu ce ba 'yar baiwa ba. “
Murmushi kawai Malam ya yi baice da ita komai ba don ya san bak'in ciki ne ya taru yai mata yawa.
Ansha shagalin suna yadda ba kwa zato, yarinya taci sunan babar Malam AYSHA, Maimuna tace a dinga kiranta da NUSRAT, yayin da Malam ya d'ebo soyayya,tattali gami da kulawa ya aza akan 'Yar baiwa.
Wata d'aya tsira Maryam ma ta haifi 'yarta mace taci sunan babar Yusuf RABEE'AH suke kiranta da HIDAYA.

Watan Nusrat uku a duniya Iya ta matsawa Ahmadu number sai ya k'ara aure, wata bazawara ce nan mak'otansu da take shigo mata, mijinta mutuwa ya yi kuma mai bala'in kud'i ne, siyayya take yowa Iya sosai da haka ta siyeta, don dama burinta kenan ta tirsasa d'an nata ya aureta, don ta tareshi da buk'atarta ya yi mata kaca² hakanne yasa ta biyo ta gurin Iya.
Don a samu zaman lafiya Malam yacewa Abdullahi ya aureta, itama ya bi zab'inta,ko a samu k'iyayyar da takewa Maimuna ta ragu, don fad'i take yaiwa mahaifinsa biyayya amman ita saboda bai d'auketa a bakin komai ba ya watsa mata k'asa a ido ta ya ya kwa za ta k'aunaci Maimuna?

Tun sanda aka saka ranar tarewar Bulki Malam da Abdullahi suke kwantarwa da Maimuna hankali ita kuma ta nuna musu hakan ba komai bane dama ai namiji mijin mace hud'u ne.
D'aki d'aya shi ya zama na Maimuna, d'aya na Abdullahi d'ayan kuma na Bulki.
Ranar juma'a aka d'aura auransu kuma a ranar ta tare, farin ciki gurin Iya ba'a magana kamar ta zuba ruwa a k'asa ta sha, tunda take ba ta tab'a taka gurinsu ba sai a ranar da aka kawo Bulki.
To zamansu dai ga shinan da dad'i babu dad'i a haka rayuwar take juyawa.
Shekarar Nusrat d'aya Maimuna ta sake haihuwar mace wacce taci sunan mahaifiyar Maimuna SAFIYYA suke kiranta SHUKHURA, wata uku tsira Bulki ma ta haifi 'yarta mace wacce taci sunan Iya na gaskiya ZAINAB suke kiranta da NIMHA, anan fa Iya ta baje kolin gata da soyayya, fad'i take yanzu ne aka haifa mata jika.
Tun haihuwar Shukhura sai da Maimuna ta shekara biyar kafin ta haifi wata macen aka saka mata NA'IMA suke kiranta da YUSRA, ita kuwa Bulki ba ta sake haihuwa ba tun daga kan Nimha.

Malam yadda kuka san bai da wata jika sai Nusrat, komai ya samu 'Yar baiwa, kayan ciye² kuwa sai ta rage ake samwa k'annenta, ta shak'u da kakan nata fiye da zatonku masu karatu, shima kuma ta shiga ransa sosai da sosai, ya na bata kulawa ne ba wai don fifici ko wani abuba, sai dai shi a ganinsa dole ne jikanka na fari ya banbanta da sauran, saboda gaba d'aya soyayyar da kakewa d'an naka kake 'yebowa ka aza a kansa.
Amman a gurin Iya da Bulki cin fuskane kawai, don a nuna ba'a son Nimha, hakan yasa suma suka d'auki dukkanin tsana suka d'ora akan Nusrat.


Nusrat Fara ce, amman farinta mai duhu ne, fuskarta siririya ce mai d'auke da siririn dogon hanci, idanuwanta suna da girma matsakaici masu shape d'in k'wan k'walati, cikin idonta fari ne tas ruwa ya kwanta a cikinsa mai maik'o, k'wayar idonta kuwa bak'a ce me silkin brown a ciki, bakinta d'an madai daici ne haka zalika lab'b'anta basu da wani tudu, ko ya ta motsa bakinta wani siririn dimple ne ke bayyana a gefen kumatunta na tsaye wanda yake k'ara fito da zallar kyahunta.
Shukhura kuwa fara ce k'al, suna yanayi da Nusrat, amman ta fi Nusrat kyau, kina ganinta kai tsaye za ki kirata kyakkyawa, saboda ita ko ba tai murmushi ba kumatunta a lotse yake, kuma nata irin na kwance ne.
Yusra ma fara ce kamar Shukhura, itama ta na yanayi da su, amman kuma ba ta da dimple.

A yanzu shekarun Nusrat goma sha biyar a duniya, ta na sss1, su Shukhura kuma shekarunsu goma sha hud'u suna jss 3
auta Yusra kuma shakarunta tara a duniya ta na aji hud'u a primary.
Allah ya yiwa Malam rasuwa shekaru hud'u da suka wuce bayan ya yi jinya kad'an, kowa ya ji babu dad'i domin anyi babban rashi mai girma, musamman Nusrat, bayan mutuwarsa ne kuma soyayyar da Abdullahi wanda yanzu suke kira da Baba yakewa Nusrat ta fara bayyana, don har ga Allah ya fi k'aunarta ya na b'oyewa ne saboda kada ya kuma janyo mata bak'in jini.
mutum ne me wadatar zuciya, ba wani k'arfi ne da shi ba sai dai rufin asiri na Ubangiji, don sun wuce cin yau da na gobe a gidansa, haka zalika bai bar iyalansa a wulak'ance ba, a ko da yaushe za ka samesu cikin kyakkyawar kamala.

Shamsu ya yi aure da matarsa Fiddausi da d'iyarsu Amima sa'ar yusra, sunanta na gaskiya Zainab, shima Iya ya yiwa takwara, a kaduna suke a zaune a saboda anan ne yake aiki, ya ninka yayan nasa sosai a fannin dukiya wanda k'arara Iya ke nuna banbanci tsakaninsu da Baba.
Aunty Maryam kuma mijinta ya koma kano da aiki don haka ya d'ebe su suka koma kano da zama, 'ya'yansu hud'u yanzu, Hidaya, Abdul, Hibba, Abbas, suma sosai Iya take ji da su saboda suma mahaifinsu na da kud'i, kuma anai mata aike akan kari.


*Wannan kenan*

300 za ku biya domin samunsa cikin sauk'i.
0567838462
NABABA FADILA SHU'AIB GTBANK
in kuma katin waya ne ki turo ta wannan layin, shaidarki ta biya ma ki turo cikinta.
09037093702
In katin wayane 400 zaku biya.




Garab'asa gareku masoyana, duk wacce ta sayi wannan littafin za ta sami wanda zan rubuta gaba kyauta, ban yadda ki sayi littafina ki dinga turawa gruop ba, in hakan za kiyi ki sameni a layina muyi magana.




Allah ka k'arawa mahaifanmu lafiya da nisan kwana.


#Team KTG
#N.W.A
[10/8, 3:42 PM] Binta Lawan: *BEBE'ARTH*


Wattpad@Rashuna


*KATANGA*


____________
*TWO*
Yau ta kama lahadi, duk da suna cikin hutun makarantar boko, su Nusrat duk sun tsefe kawunansu zasu kitso, sai da Nusrat ta fara wanka ta yiwa Yusra ma ta wanke mata kanta ta taje ta shafe mata shi da mai sannan suka shirya zasu tafi, kallon Shukhura Mama ta yi da ta saka hijabi zasu tafi tace.
"Ke yanzu ba za ki wankan ba haka za ki bisu?“
Sai da ta fara turo baki gaba kana tace.
"To Mama nan da nan d'in sai na yi wanka, abinda yanzun nan za'a mana mu dawo. “
"Allah ya shirya. “
Mama kawai tace ta na mik'awa Nusrat kud'in kitson nasu had'e da fad'in.
"Ta fara yi miki kitson, kuma tai miki manya don kinsan yadda yawan kanki yake, kuma ke zan barwa girkin dare don fita zan yi, saura kuma kice a fara yiwa Yusra don na san hali. “
Murmushi Nusrat ta yi, bayan ta saka hannu biyu ta anshi kud'in kana tace.
"Mun tafi.“
Maman tace.
"Allah ya tsare, ku dai yi addu'a kafin ku fita. “Tace.
"Amin, tom insha Allah.“ Tare da jan hannun Yusra suka bi bayan Shukhura da ta fita tun d'azu.

Har sun d'an gota gurin Iya ta hango giftawarsu da sauri ta k'walowa Nusrat kira.
"Ke ke A'i zo nan. “
Da yake haka take kiranta tun ma Malam na raye, juyowa Nusrat ta yi, Yusra ta turo baki gaba tace.
"Wallahi na san aiki za ta sakaki, kawai kizo mui tafiyarmu mu rabu da ita.“
Murmushi Nusrat ta yi tace.
"Bara dai naje na ji kiran da take mini.“
"Tak'i ta rabu da ni d'in, shegiya ifrituwa me zunb'utun baki. “
Suka jiyo muryar Iya daga ciki, kuma turo baki Yusra ta yi ta na hararar gurin kafin ta fice waje da sauri, Nusrat kuma ta nufi gurin Iyan ta na murmushi.
Gyaran d'aki tace tai mata da wankin band'aki sai 'yan tsunmokaranta ma da tace ta wanke mata.



Kallon Shukhura Nana me kitso ta yi tace.
"Ina su Yayar taku?“
"Ga sunan suna hanya. “
"To shiga ciki, gani nan bari na k'arasa sharar nan. “
Rufe bakinta kenan Yusra ta yi sallama, kallon ta Shukhura ta yi bayan ta amsa sallamar ta ta tace.
"Ina Yayarmun?“
"Ba Iya ce ta kirata ba, har ta na ce mini ifrituwa. “
Wani haushi ne ya kama Shukhura, ta zura takalminta ta fasa shiga d'akin ta fice a fusace Yusra ta biyo bayanta.

Kamar an jefota ta shigo ta na kallon Nusrat da ke zubar da shara.
"Sannu"
Tace mata, kafin ta shige zuwa gurin Iya, iya na ganinta ta d'aure b'arin goron da ta b'antara a gefen zaninta kana tace.
"To rasa kunya b'eran tanka, kinzo kimin rashin kunyar taki ne? “
Kar katar da kai Shukhura ta yi tace.
"Ashe 'Yar aljanu na da rana tun da har an iya sakata aiki, me yasa ba ki kirawo 'yar lelen taki tai miki ba sai ita za ki saka, amma in abu zaki bayar babu wanda ke gabanki sai Nimha, amman in aikine sai wacce kika raina, don kin san Nimha ko tsintsiya ba za ta iya d'aga miki ba.
Bayan kuma kitso zamu je kina gani kuma Mamanmu na zaman jiranmu“

"Tunda dai ba ke na saka ba, ki shige ki bani guri, kiyi can da rashin kunyarki. “
Cewar Iya
"Waa aini kin san abinda bazai tab'a yuyuwa bane, don wallahi bazan bautawa wanda bai san ina yi ba, in cin mutumci ne ya taso azo a tarkace mini, lalalala wallahi, itama ita taga za ta iya.“
"Ni kikewa cin mutumci Safiya, Allah ya dawo da Audu, wallahi za ki gane Ubanki na haifa. “
"Amin, ya dawo d'in ki gaya masa, wallahi duka d'aya yamin kinsan sai na bi ta inda zan rama, Allah ya baki sa'a. “
"Wai da sa'ar ki kikeyi ne Shukhura?“
Cewar Nusrat ta na kallonta, ba ta bata amsa ba ta fice ta na zunb'uro baki, Iya kuwa k'ifi² ta yi da ido tunowa da ta yi sanda ta saka Nusrat a gaba ta na zaginta Shukhura ta amshe ta hayayyak'o kamar za ta daketa har sai da Mama ta fito ta kikkifawa Shukhura mari, shine Baba ya na dawowa Iya ta kwashe ta gaya masa, aikwa ranar Shukhura ta sha duka gurin Baba, ita kuwa ta d'auki aniyar wallahi sai ta rama akan Iya, sai da ta bari duhu ya yi ta kad'a karkashinsu me yauk'i taje ta zuba a band'akin Iya,don ta na da tabbacin yanzu za ta fito ta shiga band'akin ta lab'e a bayan k'ofa, Iya na shiga ta yi sufa ta fad'i Shukhura ta fito ta na ta k'yak'yata mata dariya, tace mata kad'an ta gani muddun ta na sakawa Baba na dukanta, Iya kuwa jiki yai tsami da k'yar ta iya mik'ewa.


"Yanzu Mama kina kallo ga Iya can ta saka Nusrat aiki.“
Shukhura ta fad'a ta na turo baki gaba. “
"To meye, don ta sakata aiki?“
Mama ta fad'a ta na cigaba da tankad'en da take.
"Amma Mama kefa kikace a fara mata kitson saboda za ki bar mata girki.“
"Yanzu kuma na fasa ba, kije ke a fara miki sai ki baro Yusran a can in Yayar taku tazo sa taho tare sai ki karb'i girkin na samu na fita. “
"Amma Mama....“
Dakatar da ita Mama ta yi had'e da fad'in.
"Ban san jin komai ki shige kije kiyi abinda na saki. “
Fita ta yi ta na tutturo baki Mama ta girgiza kai had'e da fad'in.
"Allah ya shirya. “




Sai da Iya ta kinta tanci dawowar Baba ta fito babban tsakar gida ta k'wama kujera ta na jiran dawowarsa, aikwa ta na jin sallamarsa ta saki kuka me k'arfi, a gigice ya nufota ya na tambayarta.
"Lafiya Iya, me ya faru kike kuka haka?"
Face hanci Iya ta yi tace.
"Wai ni yau A'i za ta kalli tsabar idona ta zageni ta uwa ta uba. “
" 'Yar baiwa.“
Baba ya k'wallawa Nusrat kira, Nusrat da ke d'aki tun da ta dawo daga kitso kanta ke ciwo shine ta nemi guri ta kwanta, ta na jiyo abinda Iya ke cewa Baba gabanta ya yanke ya fad'i, da ta ji kwa ya k'wallo mata kira nan da nan idonta ya yi rau-rau zai fidda ruwa, a hankali ta mik'e ta fito ba tare da ta amsa kiran ba, kallonta Shukhura ta yi da ke kwashe tuwo ta cika k'atuwar kula ta kai d'akinsu, tace.
"Kinga dai da abinda ta saka miki ko? kuma wannan ba shi zai hana gobe idan tace yimin kaza kiyi mata ba. “
Ba tace mata komai ba sai juya idonta da tayi da ya fara fitar da ruwa ta nufi tsakar gidan, Shuk'hura kuwa taci gaba da kwashe tuwonta ta na mamakin sanyin hali irin na Nusrat, ta yi k'wafa a hankali, a ranta tace.
'Iya kenan, ai gara ki tab'ani akan ki tab'a Yayarmu wallahi, don ba ki son son da nake mata bane.'

Baba na ganin ta taho a sanyaye ya saki murmushi had'e da fad'in.
"Taho mana 'yar baiwa. “
Ganin murmushi akan fuskar Baban nata yasa ta samu k'arfin guiwar k'arasawa gareshi, bak'ar ledar hannunsa ya mik'a mata, me d'auke da d'ata manya-manya kasancewar yasan ta na matuk'ar son d'ata, kana yace.
"Ga masoyin naki.“
Murmushi me sauti ta saki tace.
"Na gode Babana. “
Baki galala Iya ta saki ta na kallonsu daga bisani ta tafa hannuwa tace.
"Yau naga lalacewa ni Asabe, yanzu ina gaya maka abinda yarinyar nan ta yi mini amma kai d'ata ka d'auka ka bata, gani ni wacce na yi silar zuwanka duniya ka san da cewa ina mutuwar son ka'za amma baka tab'a siyowa ka bani ni kad'ai a gidan nan ba, sai dai ka siyo gaba d'aya aci, amman ita da yake shafi da mai ce ka ware ta cikin 'yan uwanta uku, ture biyunma tunda su cikinsu d'aya ai ko Nimha ka siyowa don gudun fitina.“

"D'atan da na siyo mata na tabbata ba za ta cishi ita kad'ai ba, rabawa zasui gaba d'aya da ita da 'yan uwanta, zancen kuma Nusrat ta zage ki wallahi Iya ko jikina duk kunne ne bazan tab'a yadda za ta iya zaginki ba, ko da kuwa dukan mutuwa kikai mata a cikin gidan nan, bare kuma na san halinta ba sawa ba fitarwa, da dai Shukhura kika ce to tabbas wannan zan yadda amma 'yar baiwa lalala, sai dai kice Shukhura ce ta zageki kikace 'yar baiwa ce saboda.... ”Da sauri Iya ta dakatar da shi da fad'in.
'Ni wallahi bance maka Safiya ba, ko sunanta ban ambata a gurin nan ba in ba yanzu ba, jama'a ko kunji na ambaci Safiya? “
Ta fad'a da k'arfi yadda 'yan ciki zasu jiyo ta, murmushi Baba kawai ya yi ya ja hannun Nusrat sukai ciki.
"Kedai Mero kin haifi jarabar aljanu a gidan nan, yarinya ta bi ta zamar muku masifa duk kunfi k'aunarta cikin 'yan uwanta, su kuma hakan ko kad'an hakan ba ya damunsu, wannan wata iriyar musifa ce?
Kai kuwa Audu k'atuwar asara ce ta hau kanka don zan iya dafa qur'ani kafi son wannan 'yar aljanun ko nace 'yar ruwa akan ni da na diroka duniya, bacin haka har maganata za ka k'aryata ka zab'i d'iyarka, babu komai ai gobe Shamsu zai zo garin, Allah sarki d'an albarka na san gobe miyarmu da ka'ji zan cisu har na ture, don ni ina jin idan yazo ma tattara kayana zan na bisa, don wallahi na gaji da cin shinkafa 'yar hausa da tuwon garin masara kullum suna cushe maka a ciki, don na ji ana rad'e rad'en tuwon masara gini yake a cikin mutum, haka kawai na zauna naje na kashe kaina tun wa'adina bai cika ba. “



DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment