Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

KALLON KITSE Complete Hausa Novel Document by KALLON KITSE


KALLON KITSE

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 139985



KALLON KITSE

Reading Time: 11 Hours

Added On: 20, Aug 2023

Author: Samira Harouna ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : ZAMAN AMANA WRITER'S

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 691.51 kb

File Type: txt

Views: 1431+

Download: 2233+

Last download: less than 1 second ago

Description/Story: 13/12/2019 à 20:33 - Les messages envoyés dans ce groupe sont désormais protégés avec le chiffrement de bout en bout. Appuyez pour plus d'informations.
13/12/2019 à 20:33 - Vous avez créé le groupe “💑KALLON KITSE💑”
13/12/2019 à 20:34 - Vous avez retiré Sis Meerah
13/12/2019 à 20:35 - Vous avez changé l'icône de ce groupe
21/12/2019 à 15:34 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑



_SAMIRA HAROUNA_


*Littatafan marubuciyar*


*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._


*SADAUKARWA GA*

_MATAN FARKO_🧕🏼 *(UWAREN GIDA)*


🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛


_Na karb'i uzurin uwaren gida wannan karan, na kuma fahimci kukan su, sun ce kullum in dai labari ya biyo tsakanin miji da matan shi biyu, to sai marubuta sun yi k'ok'ari sun nuna uwar gida ce marar kirki, a k'arshe sai amarya ta mallake mijin, alhalin kuma a zamanin nan yanzu ba haka bane, dan haka dan Allah mu gyara, zaiyi wuya ace kullum uwar gida ce marar mutunci, duba da dayawa daga cikin maza sai sun k'ara auren ma su ka gane kirkin matan su na farko, ba ma miji kad'ai ba har da dangin shi, dan haka ku share hawayen ku, *Samira* za ta cika mu ku zuciyar ku da farin ciki, a matsayin ta na uwar gida ita ma uwar katarere😉, su momyn Dady *d'ogalawa* ne😂, ku biyo ni muji wa ake wa kallon kitse ne._


```Fatan alkairi masoya```


_Bismillahir rahamanir rahim_


*1*



Cikin kuka ta cire glishin (glass) idon ta ta kalle shi tace " Abban *Bilal* me na yi ma ka? Wane laifi na aikata da har za ka hukunta ni ta hanyar yi min kishiya? Abban Bilal ka dai na so na ne ko me? Me na rage ka da shi da har za ka k'ara aure a wannan lokacin? *Shekara goma sha uku* mu na tare da kai, ba ka k'ara aure ba sai yanzu, sai yanzu da na fi buk'atar ka a kusa da ni? Me ya sa? Me ya sa za ka k'ara aure? Ka gaji da zama da ni ne? Ko kuma dangin ka ne su ka saka ka k'ara aure, saboda har yanzu ban k'ara..."

Yasan me za ta fad'a, dan haka ya yi saurin rufe mata baki, manna kan ta ya yi a k'irjin shi ya na shafa bayan ta ya na fad'in "Haba Momyn Bilal, me ya sa za ki bari har shed'an ya shiga zuciyar ki ya rik'a raya mi ki wannan tunanin? Ni na fad'a mi ki kin min laifi? Ko kuma na fad'a mi ki zan k'ara aure ne saboda na dai na son ki? Haba dan Allah, ki nutsu mana, sannan ki saurare ni, ta hakane kad'ai za ki fahimce ni."

Da k'arfi ta d'ago daga jikin shi tace "Fahimta? Na fahimce kama ka ke cewa? Ai ni da k'ara fahimtar ka kuma har abada, ka riga da ka ruguza yarda da fahimtar da na ke ma ka a baya, Abban Bilal, wallahi ba zan sake sauraren ka ba, ka cuceni, ka zalunce ni, tsawon shekaru na d'auka ina rayuwa a k'ark'ashin yaudarar ka, kullum ka na fad'a min ni kad'ai ka ke so, ba ka da sha'awar k'ara aure a rayuwar ka, ba ka da wani dalilin da zai sa ka k'ara aure, amma shine yanzu za ka zo min da wai za ka k'ara aure, lallai, sai yau na yarda da ake cewa namiji ba d'an goyo bane, kuma duk macen da ta rik'e namiji uba, to tabbas za ta mutu marainiya, gashi na ga zahiri."

Ganin yanda take kallon shi ya san ba ta ganin shi da kyau saboda lalurar ta, dan haka ya d'auki glishin da ke gefe ya fara k'ok'arin saka mata, buge hannun shi ta yi ta zauna kan kujera ta na fad'in "Rabu da ni, macuci kawai."

Da tsantsar mamaki ya kalle ta har ya zauna kusa da ita, ba tare da ya daina kallon ta ba yace "Dan Allah Momyn Bilal ki daina kukan nan, kinfi kowa sanin matsalar ki, dama ya lafiyar idon ki, bare kuma ki na irin wannan kukan, ki daina dan Allah, kinsan kukan ki ya na matuk'ar tab'a zuciya ta, wallahi ba na son ganin zubar hawayen ki ko da na farin ciki ne, da kinsan irin rad'ad'in da na ke jin a game da zubar hawayen nan na ki, to hak'ik'a da kin tausaya min kin share hawayen ki, sannan ki saurari mijin ki."

Cikin share hawaye tace "Ai da kan ka ka je ka ciro min tikitin (ticket) kuka, sannan da hannun ka kama nawa hannun ka d'ora ni a motar tashin hankali, *Usman* wallahi ban yi tsammanin haka daga gare ka ba, ama shine har ka ke wani cewa wai na daina kuka, humm."

Jingina bayan shi ya yi ga makekiyar kujerar cikr da nuna damuwa yace "Assha, ban zaci haka daga gare ki ba, gaba d'aya na ji na rasa k'arfin gwiwar da na shigo da shi gidan nan, gaba d'aya na ji na tsani kai na, na ji ina ma mutuwa ta d'auke ni kafin wannan ranar, ni *Usman*, ni ne yau na yi silar zubar hawayen mata ta, abar alfahari na, farin ciki na, kwanciyar hankali da nutsuwa ta, kuma uwar d'ana mafi soyuwa a zuciya ta, tabbas yau d'in nan na ji kamar rayuwa ta ba ta da anfani, macen da na ke matuk'ar so fiye da komai, wai yau ita ce ta ke kira na da macuci, macen da na ke d'aukar farin cikin ta da mahimmanci, yau ita ce ta ke kira na da azzalumi, macen da bayan mahaifiya ta, ita kad'ai ce na fi d'auka da mahimmanci, amma ita ce ta ke kira na da mayaudari, macen da na ke d'aukar addu'ar ta gare ni tamkar addu'ar mahaifiya ta, amma ita ce ke cewa na yankar mata tikitin kuka, matar da na ke da yak'inin rayuwa ta ba za ta tab'a moruwa ba idan babu ita a tare da ni, ita ce ke k'ok'arin ruguza farin cikin gida na."

D'agowa ya yi daga jinginar ya na kallon ta yace " *Nana Khadija* ta da na sani, ta na da hak'uri, ta na yakana, ta na da fahimta, sannan ta na da uzuri wa mutane, haka ma ta na son duk abin da na ke so, da zan ce wannan abun bak'i ne alhalin fari ne, to ba musu Khadija za tace tabbas bak'i ne, ko da kuwa za'a yanka ta ba za ta sauya maganar ta ba, dan haka ni ba zan bar wannan hawayen na ki su ci gaba da zuba ba, ni mai son ki ne har kullum, k'auna kuma ba k'arya ba ce, dan haka Nana Khadija ta na fara *auren nan*, in dai har auren da zan yi shine silar fara shiga damuwar ki, to na fasa har abada."

Tun da ya fara magana ta ji jikin ta ya yi sanyi, maganganun shi sun tab'a zuciyar ta sosai, amma sai ta kasa kallon shi saboda kunyar da ta rufe ta, a hankali ya dafa kafad'ar ta ya kwantar da ita a kan k'irjin shi ya na ci gaba da shafa ta ya na fad'in "Abu d'aya da banji dad'in shi ba, shine rashin samun yardar ki, na yi mamaki da takaici da ki ka kasa fahimta ta, ban ji dad'in yanda ki ka rufe idon ki ba ki ka k'i saurara ta, na so ace kinfi kowa sanin mijin ki, na so ace kin fahimci zan k'ara aure ne ba dan na gaji da ke ba ko dan na wulak'anta ki ba, kamar yanda na sha fad'a mi ki kuma yanzu ma zan sake jaddada mi ki, Khadija ba na da burin had'a ki da wata mace a duniyar nan, kin gama min komai a rayuwa ta, kin mayar da ni cikakken namiji, kin bani farin cikin da duk na ke buk'ata, hankali na ya na kwanciya idan har ina tare da ke, idan har ki ka ga na yi aure to Allah ne ya tsare haka, kuma kinsan duka abin da Allah ya hukunta babu mahalukin da ya isa ya tsallake shi ko ya canza shi, amma tun da na ga kin kasa fahimtar hakan, maganar aure na rushe ta saboda farin cikinki, dan dama ba wai zanyi bane dan ina son haka d'ari bisa d'ari, zanyi ne saboda sunna ne, kuma ina sha'awar samun ladar da ake samu ta ciyarwa."


_Me ku ka ce masoya, ta
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download KALLON KITSE

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album