Join Our WhatsApp Group

KALLON KITSE Complete Hausa Novel Document by KALLON KITSE


KALLON KITSE

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 139985



KALLON KITSE

Reading Time: 11 Hours

Added On: 19, Aug 2023

Author: Samira Harouna ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : ZAMAN AMANA WRITER'S

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 691.51 kb

File Type: txt

Views: 751+

Download: 540+

Last download: 2 hours ago

Description/Story: 13/12/2019 à 20:33 - Les messages envoyés dans ce groupe sont désormais protégés avec le chiffrement de bout en bout. Appuyez pour plus d'informations.
13/12/2019 à 20:33 - Vous avez créé le groupe “💑KALLON KITSE💑”
13/12/2019 à 20:34 - Vous avez retiré Sis Meerah
13/12/2019 à 20:35 - Vous avez changé l'icône de ce groupe
21/12/2019 à 15:34 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑



_SAMIRA HAROUNA_


*Littatafan marubuciyar*


*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._


*SADAUKARWA GA*

_MATAN FARKO_🧕🏼 *(UWAREN GIDA)*


🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛


_Na karb'i uzurin uwaren gida wannan karan, na kuma fahimci kukan su, sun ce kullum in dai labari ya biyo tsakanin miji da matan shi biyu, to sai marubuta sun yi k'ok'ari sun nuna uwar gida ce marar kirki, a k'arshe sai amarya ta mallake mijin, alhalin kuma a zamanin nan yanzu ba haka bane, dan haka dan Allah mu gyara, zaiyi wuya ace kullum uwar gida ce marar mutunci, duba da dayawa daga cikin maza sai sun k'ara auren ma su ka gane kirkin matan su na farko, ba ma miji kad'ai ba har da dangin shi, dan haka ku share hawayen ku, *Samira* za ta cika mu ku zuciyar ku da farin ciki, a matsayin ta na uwar gida ita ma uwar katarere😉, su momyn Dady *d'ogalawa* ne😂, ku biyo ni muji wa ake wa kallon kitse ne._


```Fatan alkairi masoya```


_Bismillahir rahamanir rahim_


*1*



Cikin kuka ta cire glishin (glass) idon ta ta kalle shi tace " Abban *Bilal* me na yi ma ka? Wane laifi na aikata da har za ka hukunta ni ta hanyar yi min kishiya? Abban Bilal ka dai na so na ne ko me? Me na rage ka da shi da har za ka k'ara aure a wannan lokacin? *Shekara goma sha uku* mu na tare da kai, ba ka k'ara aure ba sai yanzu, sai yanzu da na fi buk'atar ka a kusa da ni? Me ya sa? Me ya sa za ka k'ara aure? Ka gaji da zama da ni ne? Ko kuma dangin ka ne su ka saka ka k'ara aure, saboda har yanzu ban k'ara..."

Yasan me za ta fad'a, dan haka ya yi saurin rufe mata baki, manna kan ta ya yi a k'irjin shi ya na shafa bayan ta ya na fad'in "Haba Momyn Bilal, me ya sa za ki bari har shed'an ya shiga zuciyar ki ya rik'a raya mi ki wannan tunanin? Ni na fad'a mi ki kin min laifi? Ko kuma na fad'a mi ki zan k'ara aure ne saboda na dai na son ki? Haba dan Allah, ki nutsu mana, sannan ki saurare ni, ta hakane kad'ai za ki fahimce ni."

Da k'arfi ta d'ago daga jikin shi tace "Fahimta? Na fahimce kama ka ke cewa? Ai ni da k'ara fahimtar ka kuma har abada, ka riga da ka ruguza yarda da fahimtar da na ke ma ka a baya, Abban Bilal, wallahi ba zan sake sauraren ka ba, ka cuceni, ka zalunce ni, tsawon shekaru na d'auka ina rayuwa a k'ark'ashin yaudarar ka, kullum ka na fad'a min ni kad'ai ka ke so, ba ka da sha'awar k'ara aure a rayuwar ka, ba ka da wani dalilin da zai sa ka k'ara aure, amma shine yanzu za ka zo min da wai za ka k'ara aure, lallai, sai yau na yarda da ake cewa namiji ba d'an goyo bane, kuma duk macen da ta rik'e namiji uba, to tabbas za ta mutu marainiya, gashi na ga zahiri."

Ganin yanda take kallon shi ya san ba ta ganin shi da kyau saboda lalurar ta, dan haka ya d'auki glishin da ke gefe ya fara k'ok'arin saka mata, buge hannun shi ta yi ta zauna kan kujera ta na fad'in "Rabu da ni, macuci kawai."

Da tsantsar mamaki ya kalle ta har ya zauna kusa da ita, ba tare da ya daina kallon ta ba yace "Dan Allah Momyn Bilal ki daina kukan nan, kinfi kowa sanin matsalar ki, dama ya lafiyar idon ki, bare kuma ki na irin wannan kukan, ki daina dan Allah, kinsan kukan ki ya na matuk'ar tab'a zuciya ta, wallahi ba na son ganin zubar hawayen ki ko da na farin ciki ne, da kinsan irin rad'ad'in da na ke jin a game da zubar hawayen nan na ki, to hak'ik'a da kin tausaya min kin share hawayen ki, sannan ki saurari mijin ki."

Cikin share hawaye tace "Ai da kan ka ka je ka ciro min tikitin (ticket) kuka, sannan da hannun ka kama nawa hannun ka d'ora ni a motar tashin hankali, *Usman* wallahi ban yi tsammanin haka daga gare ka ba, ama shine har ka ke wani cewa wai na daina kuka, humm."

Jingina bayan shi ya yi ga makekiyar kujerar cikr da nuna damuwa yace "Assha, ban zaci haka daga gare ki ba, gaba d'aya na ji na rasa k'arfin gwiwar da na shigo da shi gidan nan, gaba d'aya na ji na tsani kai na, na ji ina ma mutuwa ta d'auke ni kafin wannan ranar, ni *Usman*, ni ne yau na yi silar zubar hawayen mata ta, abar alfahari na, farin ciki na, kwanciyar hankali da nutsuwa ta, kuma uwar d'ana mafi soyuwa a zuciya ta, tabbas yau d'in nan na ji kamar rayuwa ta ba ta da anfani, macen da na ke matuk'ar so fiye da komai, wai yau ita ce ta ke kira na da macuci, macen da na ke d'aukar farin cikin ta da mahimmanci, yau ita ce ta ke kira na da azzalumi, macen da bayan mahaifiya ta, ita kad'ai ce na fi d'auka da mahimmanci, amma ita ce ta ke kira na da mayaudari, macen da na ke d'aukar addu'ar ta gare ni tamkar addu'ar mahaifiya ta, amma ita ce ke cewa na yankar mata tikitin kuka, matar da na ke da yak'inin rayuwa ta ba za ta tab'a moruwa ba idan babu ita a tare da ni, ita ce ke k'ok'arin ruguza farin cikin gida na."

D'agowa ya yi daga jinginar ya na kallon ta yace " *Nana Khadija* ta da na sani, ta na da hak'uri, ta na yakana, ta na da fahimta, sannan ta na da uzuri wa mutane, haka ma ta na son duk abin da na ke so, da zan ce wannan abun bak'i ne alhalin fari ne, to ba musu Khadija za tace tabbas bak'i ne, ko da kuwa za'a yanka ta ba za ta sauya maganar ta ba, dan haka ni ba zan bar wannan hawayen na ki su ci gaba da zuba ba, ni mai son ki ne har kullum, k'auna kuma ba k'arya ba ce, dan haka Nana Khadija ta na fara *auren nan*, in dai har auren da zan yi shine silar fara shiga damuwar ki, to na fasa har abada."

Tun da ya fara magana ta ji jikin ta ya yi sanyi, maganganun shi sun tab'a zuciyar ta sosai, amma sai ta kasa kallon shi saboda kunyar da ta rufe ta, a hankali ya dafa kafad'ar ta ya kwantar da ita a kan k'irjin shi ya na ci gaba da shafa ta ya na fad'in "Abu d'aya da banji dad'in shi ba, shine rashin samun yardar ki, na yi mamaki da takaici da ki ka kasa fahimta ta, ban ji dad'in yanda ki ka rufe idon ki ba ki ka k'i saurara ta, na so ace kinfi kowa sanin mijin ki, na so ace kin fahimci zan k'ara aure ne ba dan na gaji da ke ba ko dan na wulak'anta ki ba, kamar yanda na sha fad'a mi ki kuma yanzu ma zan sake jaddada mi ki, Khadija ba na da burin had'a ki da wata mace a duniyar nan, kin gama min komai a rayuwa ta, kin mayar da ni cikakken namiji, kin bani farin cikin da duk na ke buk'ata, hankali na ya na kwanciya idan har ina tare da ke, idan har ki ka ga na yi aure to Allah ne ya tsare haka, kuma kinsan duka abin da Allah ya hukunta babu mahalukin da ya isa ya tsallake shi ko ya canza shi, amma tun da na ga kin kasa fahimtar hakan, maganar aure na rushe ta saboda farin cikinki, dan dama ba wai zanyi bane dan ina son haka d'ari bisa d'ari, zanyi ne saboda sunna ne, kuma ina sha'awar samun ladar da ake samu ta ciyarwa."


_Me ku ka ce masoya, ta yi farin ciki? Ko kuma ta hak'uri ayi kawai?._


*Sai mun had'u a shafi na gaba.*
26/12/2019 à 11:32 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑



_SAMIRA HAROUNA_


*Littatafan marubuciyar*


*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._


*SADAUKARWA GA*

_MATAN FARKO_🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*


🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛


```Fatan alkairi masoya```


_Bismillahir rahamanir rahim_


*2*



D'agowa ta yi daga jikin shi ta na kallon shi a dishi-dishi, karb'ar gilashin ta ta yi da har yanzu ya ke hannun shi ta mak'ala a idon ta, tarau ta gan shi ta ciki dan haka ta kamo hannun shi ta na murzawa tace "Ka sa na ji kunyar kai na, Abban Bilal na hak'ura, ba zan so ka fasa aure ba a kai na, idan na yi haka na zama azzaluma kuma mai son kan ta dayawa, sannan fasa auren na ka zai iya janyo matsaloli da dama, daga ciki kuwa har da dangin ka, dan za su zarge ni, ni kuma ba zan so haka ba, dan haka na amince ka k'ara aure, na san ba za ka wulak'anta ni ba, duk da dai ina d'an jin tsoron yan matan yanzu, amma ina fatan ka mana zab'i na gari, ba zab'en tumun dare ba."

Murmushin gefen labb'a ya yi yace "Na riga da na yanke hukunci, na san kin amince ne saboda kawai ki faranta min rai, ni kuma ba na son tursasaki a kan abin da ba kya so, dan haka ya wuce kawai."

Da sauri ta gyara zama ta na fuskantar shi tace "Haba aljanna ta, ni fa na ce na amince, wallahi babu takura a ciki, wani k'aramin rashin fahimta ne, kuma sai ga shi cikin ikon Allah fasihi kuma nagartattacen miji na ya fahimtar da ni, dan haka in ba so ka ke na maka kuka ba kawai ka amince."

Yanda ta k'arashe maganar cikin shagwab'a ya birge shi, dan haka ya rumgumo ta jikin shi ya na dariya, cikin so da k'auna ya ci gaba da rarrashin ta tare da saka mata albarka, tambayar ta ya yi "To yanzu ina so ki fad'a min duk abin da ki ke buk'ata, ni kuma insha Allah zanyi mi ki shi a matsayin tukuici da kuma fad'an kishiya."

Kasancewar ta mace mai yawan shagwab'a da son jiki ya sa ta turo baki gaba ta kwanta a kafad'ar shi tace "Kaji ka da wata magana, ai ni yanzu ba kai ne za ka min hidima ba, ni ce ma zan bayar da tawa gudunmuwar."

"Ban yarda ba, sai kin fad'a, in ba haka ba kuma zan kama ki ne."

Yanda ya yi maganar cikin sigar rausaya ya sa ta tashi ta nufi d'akin ta ta na fad'in "Na k'i wayon, ka kamani d'in."

Ya na jin haka ya tashi da gudu ya nufe ta, ita ma a guje ta k'arasa shiga d'akin, kasancewar Bilal na wajen kakannin shi (iyayen Khadija) ya sa su ka saki jiki sosai su ka more rayuwar su, dan dama kusan kullum haka su ke.

*Washe gari* kamar kullum misalin *09:30* su ka gama shirin fita, har farfajiyar gida su ka isa tare, ita ma kuma cikin shirin fita ta ke, sai da ya shafi lallausan kumatun ta tare da sumbatar ta kafin yace "Ni zan wuce, ki kula min da kan ki, sannan ki gaishe min da su Mama, tun da ba za ki bani damar da zan kai ki da kai na ba bare na gaishe su."

Masha Allah, duk da cikin gilashi ne ta waina idon ta, amma bai hana su d'aukar hankalin Usman ba, saboda girman idon da kuma farin su tamkar madara, cikin wasa da idon ta ne tace "Na shiga uku, da alama sai an shekara d'ari ka na min gorin wannan maganar."

"Ai dole ne, dan na lura kamar ba kya so na je na kwaso albarka wajen Mama, sannan na sake mata godiya da ta bani ke."

"Gashi kuma ba kya gajiya da godiya kullum."

"Ni kam ina zan gaji da godiya, duk wanda ya baka yar sa ka aura ai ya gama ma ka komai, bare kuma mata irin ki Khadija, ai har duniya ta nad'e ba zan daina mu su godiya ba wallahi, dan na san sun fini sanin ki, amma kuma hakan bai hana su ka rabu da ke ba su ka bani ke, duk da kuwa sun san ba zan tab'a rabuwa da ke ba in ba mutuwa ce ta raba mu ba."

Ajiyar zuciya ta sauke tace "Idan har na biye ma ka, to hak'ik'a zan tabbata anan ban tafi in da zan je ba, dan haka sai an jima, nima ka gaishe min da Mama na da Abba na, tun da ka k'i bani damar bin ka bare na gaishe su."

Ta na fad'a ta juya ta na dariya shi kuma ya na fad'in "Au! Ramawa ki ka yi? Shikenan ai zan kama ki."

Gwalo ta masa tace "Ka kamani d'in, kafin nan na san in da na kai."

Wata tsandareriyar mota ta shiga bla (bleue) shi ma haka, sai dai ta shi bak'a ce, kowa hanyar da za ta sada shi da na shi iyayen ya nufa, dan su dama a *zarya* su ke, bayan masallacin *sahaba*, Khadija gaba ta yi saboda gidan su na gaban sabon gidan mota na *Rimbo*, shi kuma Usman gidan iyayen shi ya na nan *sabon gari* a 'yan *banana* (🤸‍♂aradu unguwar mu).


Ko da ya isa mahaifiyar shi kad'ai ya samu a gidan, dan haka su na gaisawa ya d'auko maganar auren shi, tambayar da ta fara mi shi ita ce "Khadija ta sani?"

"Eh Mama, ta sani, kuma ta bada goyon bayan ta d'ari bisa d'ari, yanzu amincewar ku na ke buk'ata."

Cike da kamala tsohuwar tace "Ba ka da matsala da amincewar mu *Fodio* (sunan mahaifin...


Read / Download KALLON KITSE

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album