Join Our WhatsApp Group

BA NI NA KASHETA BA Complete Hausa Novel Document by BA NI NA KASHETA BA


BA NI NA KASHETA BA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 39234



BA NI NA KASHETA BA

Reading Time: 3 Hours

Added On: 21, May 2023

Author: King Boy Isa ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 202.61 kb

File Type: txt

Views: 606+

Download: 304+

Last download: 2 days ago

Description/Story: →BA NI NA KASHE TABA← PART 1 na bigboy isah
me yasa kakashe ta me tama kane da zaka kashe
musu ita banyi zatan zaka iya kisan kaiba
zaharaddin sannan ta sake shi daga shake mai
wuya da tayi idanun shi sunyi nare nare ta koma
gefe tana kuka a hankali idan shi cike da kwalla ya
durkusa yace momy wllh BANI NA KASHE TABA
cikin kuka ya karashe maganar yace amma nasan
ba wanda zai saurare ni ya fashe da matsanan cin
kuka abun tausayi ji sukayi ana girgiza get din
gidan kamar za'a karya shi Daga ji kasan katti ne
majiya karfi a kofar gidan sai cewa suke wllh a fito
muna da dan mafia nan bazamu yarda ba ya yanka
masoyiyar sa bale yaran mu da kannan mu ay wllh
bazamu yarda ba sai mun kashe shi shima. da
maman deeny da kuma shi kanshi zaharadeen din
duk sun firgita da jin kalaman jama'ar nan na kofar
gida tunani suke ya za'ayi lalai idan ta basu deenyta
kashe shi zasuyi shima tunani yake bazai iya mika
kansa ba idan ya mutu mahaifiyar sa wane hali zata
shiga. suna ta faman saka wannan kwance wancan
su kuwa matasan nan tuni sun gaji kuma sunga
anki bude get hakan yasa aka nemo jarkar man
fetur a cewar su idan suka ji an fara toya gidan sa
fito su kuma sai su kama zaharadeen din su kashe
kamar yadda suke zargin yayi kisan kai. haka suka
fara watsa fetur a gidan su momy suna cikin tunani
sai sukaji ana jika su da ruwan fetur da dai suka
fahimci fetur ne sai duk suka tsorata jikin su ya
fara bari suka rasa abun yi momy cewa take cikin
kuka ay kaga abunda ka jawo mana yanzu gashi
zasu toya mu da rai kamar wasu yan wuta lol.
deeny yace wllh momy BANI NA NA KASHE TABA
momy tace towa ya kashe ta hawaye kawai naga
ya sake zubowa a fuskar shi karan jiniyar motar
police suka ji a waje ana ta koran mutane da ke
kokarin cin nawa gidan wuta dan har an samo
ashana ana kokarin kyastawa police da duka suka
kori mutane suka je kofar gidan cikin murya me
karfi suka ce zaharadeen ka fito ka mika kanka ga
hukuma dan tabatar da rashin laifin ka ko kuma
laifin jikin shi na rawa sai kuka yake yana wallh
BANI NA KASHE TABA2 momy ta kama hannun shi
tace hakuri zamuyi mu rungumi kaddara isha allah
bazaka cutu ba kayi hakuri ka mika kanka ina ga
hakan zaifi sauki. a gare mu ta karashe maganar ta
cikin kuka haka ya tashi yana tafe yana hawaye
yana juyowa kamar ya bude get din kuma kamar ya
bari a cikin zuciyar shi kuwa yace gwara in fita a
kashe ni ma hakan zaifi min sauki ya kalla sama
yace allah ka fitar dani daga zargin nan da ake min
yana bude get wani police yayi carat ya damke shi
gam sannan wani ta kama hannayan shi ya maida
su baya aka samai ankwa a hannayan shi aka tura
kyyarshi har cikin motar police din mutane ne suka
fara jifar shi suna sai mun kashe ka wllh bazamu
barka ba haka yasa police din cikin hanzari ya
warci motar tasu sai police station ana zuwa aka
nufi sel da shi aka rufe ganin an rufe deeny a sel
yasa na tsaya nan ku biyu ni dan jin labarin

→»ku dinga comment
→»yan mata da samari ayi invite
→»dan momy na gaisuwa
↓Yauwa haka nakeso
comment↓
bigboy



→BANI NA KASHE TA BA← PART 2 na bigboy isa
a gidan su halima kuwa ganin su nayi jigum jigum
kowa yayi ta gumi sai hawaye hajja hauwa hawaye
take tana fadin zaharadeen ashe ba san halima
kake ba ashe duk san da kake na kaje ka kashe ta
ne kayi kudi da ita ta karashe maganar da fashewa
da kuka kacuce mu deeny kaci amanar mu ka
kashe muna yar mu wace ita kadai muka haifa. kiyi
hakuri maman halima wllh wllh wllh sai an kwatar
muna hakin mu sai inda karfina ya kare wllh bazai
kashe muna diya a banza ba sai an kashe shi
shima hawaye ne suka gangaro fuskar shi. jikin
fushi ya tashi ya fita hajja hauwa kuwa kanta a
kasa kuka kawai take. momy kuwa tana ji an tafi da
deenyta cikin hanzari ta dakko hajib dinta ta saka ta
fito da sauri ta kulle gidan kunya duk ta cikata duk
majalisar data wuce ana nunata ana cewa ga
mahaifiyar yaran nan da kashe budurwar sa haka
tata wucewa ana nunata har takai gidan su kawun
deeny wanda shine kanin mahaifin deeny da yake
allah ya amshi ran mijin nata wanda shine mahaifin
zaharadeen tana shiga cikin gidan da sallamar ta
aka amsa ta shiga suka gaisa da amina matar
kawo kenan aka zubo mata koko da kosai dama
bata karya ba amma ko kallan shi batayi ba saboda
abunda ke damun ta su kam basu san komai ke
nan ba saboda labari bai kawo musu nan ba amina
matar kawu tace mamar deeny lafiya naga duk
fuskar ki cike da damuwa daidai nan ne kawu ya
fito daga ban daki kallo daya yama matar yayan
nashi yagane ba lafiya ba alamun tasha kuka ya
karaso wajan a lokacin da yake tambayar ta lafiya
kuwa tana kallan shi ta fashe da kuka a lokacin ne
duk sukayo kanta suna menene ya faru mamar
deeny lafiya kuwa. nan ta fara magana cikin kuka
tana deeny ne da maryam ta maimaita3 har sau
uku cikin kuka ta kasa fada.amina ce ta kamata
tana rarashin ta sannan tadan rage kukan kawu
yace me yasama zaharadeen din da maryam
kuma? nan ta fara shesheka tana musu bayani.tace
maryam tun jiya da ta fita islamiya jiya da yamma
to bata sake dawowa ba har yanzu deeny kuma a
yanzu maganar da nake muku yan sanda sun kama
shi sun tafi da shi wai ana zargin shi da kisan kai
nan ta fashe da kuka su kuma duk suka kama
inalilahhiwa ina ilaihir raji'u
inalilahhiwa ina ilaihir raji'u
inalilahhiwa ina ilaihir raji'u
suke fasa
*****************
acan kuma DPO ne yasa deeny a gaba yana
bazaka fada mana gaskiya ka hutar da kanka kuma
ka hutar damu ba yace yalabai wllh wllh BANI NA
KASHE TA BA dpo ya kara kallan shi yace watto sai
jikin ka yayi tsami zaka fada ko?…… tsoran kar a
hada dani ne yasa na tsaya a nan nima
mu hadu a whatsapp→ 08096831009 Group
bigboy
.


→BANI NA KASHE TABA← PART 3
na bigboy isah
a ranar koni da nake gefe na tausayawa
zaharadeen irin dukan da yasha suna dukan shi
suna bazaka fada mana gaskiya ba shidai abun da
yake cewa kawai wllh BANI NA KASHE TABA. BANI
NA KASHE TABA FA. haka akaci gaba da narkar shi
wai yaki fadan gaskiya har saida ya sume.
***************maman deeny kuwa gidan kawu ta
koma da zama kullum cikin kuka tana tunanin halin
da ta tsinci kanta a ciki yaran ta biyu su duka ba
daya har gwara shi deeny ma tunda ansan yana
hannun yan sanda amma ita kanwar tasa maryam
kenan ba'a san inda take ba kawu yayi yawo har ya
gaji ya dawo gida yana yin sallama suka amsa su
mashi da sauri maman deeny ta mike tana fadin
angan ta anga maryam dina kuwa? gani tayi ya
sunkuyar da kanshi kasa alamun ba labari kenan ai
kuwa ta dora hannun wanta akai ta saka uban kuka
matar kawu dake gefe ita ce ta taso ta rungume ta
tana cewa haba maman deeny hakuri zakiyi kuka
ba namu bane adda'u itace ma fita a wannan lamari
ita ma hawayan ne a fuskar ta. salama suka jiyo a
kofar gida da sauri kawu ya fita dan ganin wake
sallama police yagani cikin kayan aikin sa dan
sandar ya mikawa kawo hannun suka gaisa sannan
dan sandar yace kaine kanin mahaifin zaharadeen
ko kawu yace kwarai kuwa nine police din ya ciro
wata farar takar da ya mikawa kawo yace wannan
san maci ne daga kotu ku gaugauta samun lauya
domin gobe gobe zamu shiga kotu a bisa kes din
danku dan yaki amsa laifin sa a hannun mu kawu
ya karba hannun shi har bari yake yace na gode
sukayi ban kwana har ya juya zai shiga gida dan
sandar yace amma fa ku gaugau ta samun lauyan
ku saboda gobe ko baku da wani lauya bazai hana
zamanan ba a gobe haka kawu ya koma cikin gida
cike da damuwa yana ta tunanin shi ba kudi gare
shi ba ga basu dawa kadara da zasu sayar su
dauka lauya. abban aliyu me ya faru maman deeny
ce ta je4 mai wannan tambaya bai ce mata komai
ba kawai takardar dake hannun sa ya mika mata ta
karba tana bude wa ta fara karantawa sai hawaye
tana tunanin a ina zasu sama lauya Barrister
fadilah ta tuna sai sukaji tace alhmdulilah suka juya
suna kallan ta itama juyowa tayi sannan tace inada
kawata Barrister fadilah nasan tabbas zata taimaka
min idan na nufe ta da wannan alamarin sannan
kwarariyar lauya ce itama. gaba daya sukace
alhamdulilah saiki tashi ki shirya maman aliyu ta
rakaki inji kawu.
mu hadu a whatsapp→ 08096831009 Group
bigboy






on-line 14.04 21:00
→BANI NA KASHE TABA← PART 4
na bigboy isah
******************
alamarin maryam kuwa ranar asabar tayi wankan
ta tasaka kayan islamiya tayi ayr kwaliyar ta ta
dauko jakar qura'a nin ta ta fito tace mama zan tafi
makaranta maman deeny tace to maryam adawo
lafiya ayi karatu da kyau tace to momy zamu dage.
har ta fara tafiya tayi taku uku sai kuma ta juyo
tace momy wai har yanzu su yaya zaharadeen
shida halimar basu dawo ba ne momyn tace wllh
kuwa kinga har yanzu basu dawo ba. maryam tace
uhm nidai na tafi karna makara sai na dawo bye
bye tafita tana tafiya tana tilawa dan karta manta
karatun da sukayi jiya sai ji tayi mota ta faka ta
gefan ta da yake dan titin yau weekend ba jama'a
sosai duk ana gida ana hutu wasu kartai biyu suka
fito a motar cikin hanzari suka kamata suka rufe
mata baki sannan suka jefata cikin mota sukayi
gaba da ita sunata tafiya kamar bazasu tsaya ba ita
kuma kuka take har ta gaji tayi shiru sai kuma ta
fara ajiyar zuciya. wayar ogan yan daban ne tayi
kara ya daga ya risina yace oga an cika aiki ga
yarinyar da ka ce mu kamo ta yanzu ma muna tare
da ita. kome ogan yace mai oho jinayi yace ok sir
ya kashe wayar ya mayar aljihu sannan ya juya ya
kalli yarinyar da idanun ta duk sunyi jawur yace
kuba marar kunya ba zaku gane kun tabo wuta mun
kashe dayar sannan kema an bamu umarnin mu
kashe ki amma ba zamu tashi a tutar babu ba sai
mun danaki tukun nan zamu kashe ki. hannu ta
dora a kai ta fasa wani uban iho hade da kuka.
wuka yaciro yace sheet yi mana shiru, kallo daya
zakawa mutumin ka gane bashi da imani gashi baki
ga wasu jaja yan idanuwa fuskar nan tashi ba
annuri sai kace hata damusa maryam kuwa ta kara
kankame jikin ta tana kuka ciki ciki ana cikin tafiyar
ne naga sun faka motar kome ya faru oho sun fito
duk su ukun ba mai fara'a a cikin su dayan naga ya
zagaya baya sannan ya dawo yace oga akwai
matsala fa munyi faci a bayan nan ogan ya daka
masa tsawa maryam dake cikin mota har dan
fitsari ya kufto mata dan tsananin tsora lol. ogan
yace bazaka kunce tayar ka koma baya wancan
dan garin ka wo mana faci ba ka tsaya kana wani
yen yen yen wuce daga nan dallah. cikin hanzari
naga wanda ake kira kumurci yaje ya fara kunce
tayar ya sabe ta akafada ya koma baya wato garin
da suka wuce to gashi dare ya fara yi shi kuma
ogan ya dauki gallan yace wa wanda ake kira da
mugu yace kai zanje wancan gidan man wanda
muka wuce a baya zan je in karo mai dan ina
tunanin wannan bazai karasa damu kano ba
sannan yace ka kula da wannan yarinyar sosai
kuma kasa ido a kanta sosai yace angama oga shi
kuma ya juya ya fice ya bi bayan kumurci suna
tafiya shi kuma ya shiga gaban mota ya kuna
music yana yi yana girgiza kai yana rawa ita kuma
maryam tunanin tserewa take yi sai sake sake take
yi can sai naga tayi a jiyar zuciya ko me ta tuna
oho nima cewa nayi my queen me kika tuna………
Naku bigboy > whatsapp no 08096831009







→BANI NA KASHE TABA← PART 5
na bigboy isah
jakar ta naga ta bude ta ciro wani lacasera mai
sanyi kuma sai naga ta dakko wasu kwayoyi cikin
hanzari ta zuba a cikin kwalbar lacasera din shi
kuma mugu yana can yana jin music din sa har ya
manta tsaron mutum yakeyi can sai naga maryam
din ta dan matso tace bawan allah dan allah zan
sama breadi ko rabi ne zan dan hada shi da
wannan ne ince sai ta dago lacasera haba baaban
yana ganin lemo gashi dama yunwa yake ji ya
kwace kwalbar tare da cewa yar iska waya ce miki
yara suna shan irin wannan miko shi yana amsa
yaji da dan sanyi sanyi kuwa ya kafa kai sai da ya
shanye shi kaf sannan ya yi wurgi da robar
lacasera din waje ya juya ya kalle maryam yace ina
sauran nan take idan shi suka fara lumshe wa
kamar wanda yasha ya bugu. ita kuma a zuciyar ta
karku so kuga farin ciki sai dadi take ji.sai a lokacin
na kula ashe maganin barci ta zuba mai mutumin
ku ya langabe kai ya fara sharar barci hada
minshari. maryam din tana ganin haka sai ta bude
motar da sauri ta fito ai kuwa tace kafa me naci
ban baki ba nan ta ari ta kare tayi cikin daji da gudu
su maryam anga mutuwa saida tayi gudu 5 mint
sannan ta sama wani gidan fulani gari ne karami
duk yan filo ne a garin ji sai daka ake yi can kuma
anyi wa wani daga cikin yaran fulanin biki an dakko
makadi sai cashewa akeyi. alamarin su ogan yan
daba kuwa tare suka taho shida kumurci sai wajan
magari ba suka dawo tun daga nesa suke jin music
na tashi a cikin motar su ogan yace kutt lalai
wannan yaran zai ci uban sa har ya sama damar
kunna waka a motar nan kamar motar uban shi
zaici uban shi bari mu karasa tun daga nesa
kumurci yace oga yarinyar nan fa kamar bata mota
a fusace ogan ya juyo yace zan mare ka dan
ubanka kasan abunda kake fadi kuwa. to ka muna
shiru ai kuwa suna karasa wa sukaga mota wayam
ba maryam sama ko kasa can gidan gaba kuma
mugune sai sharar barcin sa yake tuna ogan yaje
ya bude gidan gaban ya kwada ma mugu mari.
cikin barci ya tashi yana iho yana wllh na tuba
bazan kuma ba. yana ta yan surutan shi dai ogan
ya daka masa tsawa wanda ni kaina saida na
zabura saura kadan in yarda wayar in gudu lol.
amma saboda tsabar juriya irin tawa tsayawa
kawai zan yi anan *************
ku sani wannan abunda ya faru da maryam kanwar
deeny ka sancewar itama tunda ta fita islamiya
bata kara dawowa ba…………Naku bigboy > whatsapp no 08096831009


mu hadu a whatsapp→ 08096831009 Group
bigboy
on-line 15.04 08:12
→BANI NA KASHE TABA← PART 6
na bigboy isah
tsawar da ogan ya mai ita ce ta dawo da shi
hayyacin sa ogan jikin murya mai kara yace ina
wannan yarinyar?. nan fa mugu ya fara kame kame
yana. dama uhmm uhmm ogan yace dama me
bazaka fada ba saina rabama kai biyu ogan ya fiddo
wukar shi yace wllh kayi wasa zan raba maka kai
biyu. jikin mugu na rawa yace oga inaga sayan
lacasera ta biku baku hadu a hanya ba ni dai na san
na kwace mata lacaseran ta ina shanye wa barci
ya kwashe ni ban farka ba sai ynz wllh oga. nida
nake gefe dariya na kama yi ma mugu. tsawar da
ogan ya sake yi ita tasa na kama baki na nayi
shiru. ogan yace kasan me kake fada kuwa kana
nufin ta tsere yanzu kasan ko...


Read / Download BA NI NA KASHETA BA

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album