Join Our WhatsApp Group

SHIGAR SAURI Complete Hausa Novel Document by SHIGAR SAURI


SHIGAR SAURI

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 39528



SHIGAR SAURI

Reading Time: 3 Hours

Added On: 29, Sep 2023

Author: Maman Shalele ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : PROFICIENT WRITERS ASSOCIATION

Author Phone : 0806 672 6866

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 227.51 kb

File Type: txt

Views: 728+

Download: 263+

Last download: 22 hours ago

Description/Story: [4/4, 10:33] Shalele: *SHIGAR SAURI*
Painful love story
Romance special


Writing by
*MAMAN MAMY (SHALELE)*

*Wattpad@mumies122*


*Dedicated to my close friend ikra Rukayyat*


*Devoted to identical twins hassan & Husain 80k*

*Small gift to my real fans*


*PROFICIENT WRITERS ASSOCIATION*


тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/

FACEBOOK: https://mobile.facebook.com/groups/2455147078097572/

TWITTER: https://twitter.com/pro__writers?s=09


Page > 1&2


*Muna saida kayan mata da na maza suna da kyau sosai kuma cikin sauki muna turawa koina ga me bukata seya tuntubi wannan number👉🏼 0806 672 6866*


Fans gaisuwa ta musamman a gareku ku din masoyane kun nunamin kauna ta hanyar siyen novels dina musamman raggon miji return nagode sosai wannan littafi karamar kyauta ce daga gareni insha Allah zakuji dadinshi sosai ku dai kuyi kokari Ku fara daga farko sannan Ku dage da suburbudomin comments don naji dadin yi maku typing nagode sosai da kauna luv u all🥰


*shafin farko na kine kawata maman mujaheed Allah yabar kauna*😍


*Alhamdulillahi kaseeran*



"Assalamu alaikum, Baban farouk Ina kofar gidan ka"

Baban farouk na kwance idanunshi cike da bacci yayi juyi yace"karfe 7 batayi ba fa"

Yayi yar dariya yace"ka fito plss akwai muhimmiyar maganar da nakeso zamuyi "

Baban farouk yayi hamma yace"to ganinan"

Ibraheem ya katse kiran ya zauna bakin dandamalin dake a kofar gidan yayi shiru yana tunani,

Baban farouk ya tashi batare da yin komi ba yana sanye da jallabiya yana fitowa karamin danshi khaleefa ya rugo aguje wurinshi ya daukeshi yana murmushi yace"har ka tashi ?"

Ya daga masa kai

Yace"ina mama?"

Cikin koyon mgna yace"a kitchen "

Baban farouk yayi murmushi yana dauke dashi ya nufi kofar gida ,

Gida ne karami Wanda baida gate koina sibull shafe da siminti gidan dai kwas da alamu maman farouk nada tsafta sosai,

Ya bude gidan ya fito yaga aminin nashi zaune ya karasa ya zauna yana kallonshi yace"wannan sammako haka kamar zakaje kamun fara?"

Ibrahim yayi karamin murmushi sannan yace"aure nakeso nayi"

Baban farouk yayi mamaki sosai ya bude baki da idanu yana kallonshi babbane sosai yakai 40yrs baki sosai amma kyakkyawan baki yana da hanci sosai shine ya kawata fuskarshi yana da jiki da tsawo ba laifi,

Ganin yanayin kallon da yake masa yasa ya jawo khaleefa jikinshi yace"aboki kayi salla kuwa?"

Khaleefa ya girgizakai yace"mama brush a bani"

Ibraheem ya kuma murmushi yace"ya kamata kai salla ko jeka ciki"

Khaleefa ya nufi ciki dasauri ,

Sannan ibraheem ya juyo wurin Baban farouk yace"kayi shiru banason haka"

Baban farouk yana cigaba da mamaki yace"I'm very surprise ban taba tunanin hakan ba yanzu can baya nayi_nayi kayi aure ka ki amma yau daya kace kanason aure dole nayi mamaki"

Jikin ibrahim sanyaye yace"kasan bani da matsalar shaawa kuma kasan yadda rayuwata ta taso mahaifiyata ta rasu wurin haihuwa da ita da abin da ke cikinta duk sun rasu babana yakasa jurewa da jin labarin ya fadi ya mutu akabarni ni kadai cikin yawan dangi amma rikeni ya gagaresu yau ina wancan gida gobe wancan da sungaji zasu turani wani wajen harnagaji na dawo wurinka da zama kafin kai aure kabarni cikin shagonka na ki yin aurene saboda da manufofi da yawa idan banda abun rike iyalin saboda me zanyi aure ?wasu zakaga daga little three month da aure anfara samun matsala saboda kudi ,na biyunshi yadda na tashi ya zamar min darasi tarin yanuwa baya nufin idan kabar diyanka zasu samu gata zaa kula dasu abu mafi muhimmanci ka Samar masu Uwa ta gari bayan mutuwa mahaifiya zatayi iya kokarinta don ganin yaranta sunyi rayuwa me kyau da inganci "

Baban farouk duk jikinsa yayi sanyi yana ta kallon Ibrahim yace"yanzu kasamu wacce kakeso?"

Ibrahim yayi murmushi yace "kasani bana soyayya auren kawai nakeso nayi "

Baban farouk yayi dariya yace "to taya zakayi auren haka ?ai seka samu wacce kakeso kun dedeta"

Ibraheem yace"ban shaawar yin aure garinnan nafison in auro yar kauye wacce asalinta kauyene"

Baban farouk yace"meyasa? Baka ganin kana iya auro wacce zatai ta baka wuya saboda kauyanci da duhun kai?"

Ibraheem yace"a'a bana nufin auren jahila kauyawa suna da makarantun allo dana islamiyya suna da ta boko primary inaga in na samu me primary ko bayan aurenmu seta cigaba da karatun nafison in auri wacce bata wayen ba me saukin kai wacce zan reneta muyi zaman lpy "

Baban farouk yace"nan a state ma akwai duk Wadannan amma de yadda kakeso yanzu wane kauye zamu dauko matar?"ya karasa da murmushi,

Ibraheem yace"kauyen mu wagini ina da kawu a can yana da kirki sosai inaso ka rakani muje shi nake son ya zabamun Matar "

Baban farouk na masa wani kallo yana wata iriyar dariya yana Sosa gemunsa yace" Allah yasa alheri yaushe zamuje?"

Ibraheem yayi karamin murmushi yace"mu bari se week end kaga time ba aiki amma fa kwana zamuyi lahadi mu dawo "

Baban farouk ya sakeyin dariya yace "Allah yakaimu"

Ibraheem yace"naga kana daukar abun wasa zakayi mamaki "

Baban farouk yayi dariya ya mike tsaye yace"daganan kana jiyo kamshi ko?madam tagama hadamin delicious nayi ciki a je asha tea da bread"yana gama fada ya shige gida,

Ibraheem yayi murmushi ya girgizakai sarai ya gane nufinshi saboda shi matarshi classmate dinsa ce ta kware a komi musamman girki, aganinshi kowa ba da iyawa aka haifeshi ba don haka duk macen da bata iya sanwa ba kowani abu ita taso bayajin matarshi zata dawwama ba iyawar idan harma bata iya ba kenan,

Ya tashi ya nufi mashin dinsa me suna ledis ya hau ya tada ya nufi shagon da yake matsayin gidansa ,

Bayan 3 days

Ya kama ran Saturday tunda safe ya isa kofar gidan abokinsa yana cikin riga da wando shadda ya fito babban mutum kamar magidanci, yaciro wayar shi Nokia ya kirashi ringing biyu ya dauka yace"ango ina shiri yanzun nan zan fito"

Ibraheem yayi murmushi ya kashe kiran,

Bayan mintuna Baban farouk me suna isa ya fito cikin tashi shaddar ya dana hula gaban goshi ibraheem na ganinshi yayi murmushin zuci yace"mu tafi angon zulfau"

Baban farouk yayi dariya yace "bazan ce komi ba se naga lantanar matarka"

Ibraheem yayi murmushi suka dauki hanyar tashar mota don duk mashina garesu,

Suna zuwa suka dau hanyar wagini village,

Tafiyar two hrs ta kaisu kauyen suna sauka suka dauki hanyar gidan kawun nashi,

Yana zaune kasan wata bishiya an shimfida tabarmar kaba ga casbi a hannunsa yana ja ,

Suna isa wurin bishiyar sukayi yayinda kawun ya kara gyara zama yana kallonsu yana murmushi yace"maraba da mutanen birni"

Suka zauna suna ta sunkuyar da kai suka fara gaidashi,

Ya amsa yana faraa yace"iro kwana biyu shiru kadena lekomu lpy de ko?"

Ibraheem yace"ayi hakuri kawu"

Kawun yayi murmushi yace"bari na sa a kawo maku ruwa"

Ya tashi ya nufi cikin gidan da yake na jar kasa ,

Suna zaune ya fito ya dawo ya zauna ,

Suna ta dan labari wani matashi ya fito da kwanon ruwa da kwaryar fura yazo ya ajiye gabansu sannan ya kallesu yace"sannunku da zuwa"

Suka ce "yawwa ya aiyuka?"

Yace"lpy lau "ya tashi ya tafi,

Ibraheem ya dauko ruwan ya mikawa Baban Farouk sannan ya matso da furar sosai gabansa,

Bayan sun dansha kawu ya nata kallon ibraheem yadda ya kara girma ga shekaru nata tafiya amma yaki aure a hankali yace" iro nace se yaushe zakayi aure ne ?gashi de kannan kannan ka har sunyi haihuwa bibiyu "

Kanshi sunkuye yace"kawu nazo ne Ku zabamin mata wacce kuka yarda da tarbiyyarta da asalinta"

Kawun yayi murmushin manya yace"nadade banji labari medadi kamar wannan ba, naji dadi da ka girmamani kabani damar yi maka zabi nagode sosai Allah yajikan mahaifinka"

Ya tsagaita yana murmushi yace "amma baka fadi kalar da kakeso ba kar akawo wacce batai ma ba"

A kunyace Ibraheem yace"kawu yarinya ta gari na keso ko ya take inde tana da tarbiyya "

Kawu yayi shiru har ya gama yiwa dan nasa zabe domin kuwa akwai yarinyar da duk safiya take wucewa makarantar boko sannan Ko giftawa nawa zatai saita gaisheshi kyakkyawace sosai sede ba fara ba black beauty yana jindadin yadda take girmamashi marainiyace amma masu iyayen ma wasu basu kaita tarbiyya ba kakarta na iya kokarinta wurin bata tarbiyya ,

Ya kalli ibraheem yace "insha Allah zanyi iya kokarina wurin zabar maka abokiyar zama ta gari kafin ka dawo"

Ibraheem yayi godiya yace"anan zamu kwana zuwa gobe zamu tafi"

Kawu na kara jin dadi yace"madallah naji dadi sosai Allah ya muku albarka"

Suka ce "ameen" atare,

Kawu ya tashi ya shiga cikin gida yasa a yanka masu agwagi ai musu farfesu a soya don yaji dadi jin zasu kwana ya koma wurinsu suka kara shan hira sannan suka shiga ciki suka gaida tsoffi suka wuce gaido megari,

Da marece kawu Wanda shine autan babansu ibraheem yaje wurin megari abokinsa ya fadamai yadda sukai da ibraheem megari ma yayi farinciki saboda baban ibraheem mutumin kirki ne da son jamaa shima ya bada goyon baya sannan yayi jagora wurin nemarwa ibraheem auren yarinyar,

Kafin dare angama nemawa ibraheem auren aiken kudi kawai ya rage da kuma abubuwan al'ada,

Ibraheem yaji dadin labarin cikin daren ya bada dubu 30 kudin neman aurenta da sadaki a hakan yayi kokari sosai a lokacin nera na da daraja,

Daren ibraheem ya kasa bacci cike yake da d'okin ganin wacece zabin kawunsa ?wacece zaya aura? Juye _juye yayi tayi kafin bacci ya samu daukeshi,

Bayan asuba suka zauna fira abokinshi kuma amininsa nata zaulayarshi da safe suka sha koko da kosai sukai wanka sukaje wurin megari sukai godiya karfe sha daya suka kama hanyar birni batare daya samu damar ganin wacece zai aura ba,

Bayan kwana biyu da tafiyarshi aka saka bikin wata hudu masu zuwa,

Da dare da muneerat da kakarta suna daki suna cin tuwon dawa a tare cikin kwano daya kakarta tanata kallonta tai murmushi tace"muneera kin kusa girma"

Muneera ta kalli kanta shekarunta 14 ciff a duniya duk wani abun da ke nuna girman mace ba abinda bai fito ba sede bata da jiki ta meda kallo gun kakarta tai dariya ta sunkuyar da kai,

Kaka tace"kinason zuwa birni?"

Muneera ta girgizakai tace"kaka ni banason karamin abun da zai rabani dake kullum tare muke kwana banason zuwa koina"

Kaka tai murmushin manya tace"dazun nan kawunki yafadamin sun gama saka ranar aurenki nan da wata hudu"

Muneera tai shiru ta shiga tunani towa zata aura?

Kaka na jindadi tace"zaki tafi birni ki huta da daka da surfe da debo ruwa"

Memakon murna se muneerat ta zare hannunta daga cikin kwano ta fara kuka hawaye suka balle mata kamar famfo ta cigaba da kuka har da sheshsheka sosai take jindadin zama da kakarta wasu na ganin nuna soyayya da yawa ga yaro na lalatashi amma ita hakan bai mata komi ba se gyaran rayuwarta ,

Hankalin kaka yayi mugun tashi don batason ko digon hawaye ya fito daga idon jikarta se taga kamar ta gaza wani wuri bata manta time da uwarta ke labour irin wuyar da tasha kafin ta haifota Wanda sanadiyyar haka ta rasa diyarta guda daya shiyasa ta kwashi duk soyayyar ta meda akan muneerat ,

Tai saurin tande yatsun hannunta ta jawo muneera jikinta murya sarke tace"minene muneera auren ne bakyaso komi ?"

Muneerat na kuka tace"kaka banason auren... nafiso in yita zama tare da ke...ni de kaka karkumin aure banaso"

Kaka tai ajiyar zuciya ita kanta batason ta kifta bataga muneerat ba a hankali cikin rarrashi tace"muneera bakison aure haka zakiyita zama ?bakiso ki taramin jikoki Wanda zan rika gani inajin dadi suna zuwa gaidani suna min wasa suna debemin kewa?ki temakamin muneera kiyi aurenki kiyi zamanki lafiya da mijinki hankalina zaifi kwanciya"

Muneera tai shiru jin Kalmar temako da kaka ta fada take idanunta suka rika hangomata daidaikun gidajen da diyansu da jikoki ke zuwa gaidasu ita kanta abun na bata shaawa,

Take hawayenta suka tsaya babu abinda bazatayi ba don jindadin kakarta, itace uwarta, ubanta, danginta, kawarta kuma aminiya abokiyar wasanta ,

Kaka tace"kiyi hakuri muneera farko hankalina ya tashi jin zaki tafi birni saboda banason bude ido babuke kusa dani amma danayi tunanin zaki huta da wahalar kauyen nan diyanki kuma zasu samu rayuwa me inganci shiyasa nai farinciki matuka karki bani kunya muneera ta"

Muneera ta kara rungume kaka tana sauke ajiyar zuciya,

Kaka tace"kindena kukan ko yanzu ne kadai zaki cigaba?"

Muneera ta boye fuskarta tana dariya abun duk kunya yake bata ,

Kaka tai dariya tana jindadi da karin kaunarta, bata yiwa muneera magana so biyu tana gudun bacin ranta tana kuma son farincikinta sosai, ta shafi kanta tace"Allah ya miki albarka ya baku zuria dayyiba wanda zakuyi alfahari dasu "

Muneera tai gum tana hango ya kalar rayuwar zata kasance nan gaba,

Kaka tace "sakeni na sauyo miki tuwon wannan ya gama sanyi"

Jin haka yasa muneera tashi ta dauki kwanon ta fita zuwa kitchen dinsu abincin ya fita ranta amma dole taci don in bata ci ba hankalin kaka bazai kwanta ba,

Da muneera da ibraheem kowa yanason ganin juna amma basu samu hakan ba har sai saura 1 month bikinsu time din ankawo lefenta akwati guda da kala biyar da kayan shafa dasauransu ,

Ganin lefenta cikin akwati yasa kauyen yagame da zancen aurenta wasu na mata murna wasu na hassada ,

Surutu koina wasu na cewa mijin katone yafi karfinta be kamata a bashi yarinya kamarta ba abun mamakin kuma har kamar megari suna bashi aure wannan kawai aka sawa ido surutu koina Wanda hakan ya daga hankalinta,

Bayan kwana biyu kacal da kawo lefen yazo garin yakasa jurewa har seda yasa aka kaishi gidansu,

Suka tura yaro kiranta se gata ta nufo gidan ta dawo daga school tana sanye da doguwar riga green and white da white hijab,

Yanayin shigarshi yasa ta gane daga birni yake dan rakiyar dan kawune tama sanshi hakan ke mata tabbacin shine Wanda zata aura ganin girmanshi seda gabanta ya fadi yana da jiki sosai tana cikin kallonsu idanunsu suka sauka kanta tai saurin juyawa ta nufi hanyar komawa dasaurinta,

Dan kawu yayi murmushi yace"gata can zata koma"

Ya dage ya kwala mata kira "muneera!!!"

Time daya ibraheem da muneerat zuciyarsu tai motsi tai saurin juyowa don tasan kaka tagama jin kiran ta nufesu kanta kasa,

Shi ko ibraheem jin sunan ne yasa zuciyar sa motsawa bai taba kawo zaiji sunanta muneera ba farat daya sonta ya mamaye zuciyarshi ya kura mata ido yana karemata kallo tundaga sama zuwa kasa.
[4/4, 10:33] Shalele: *SHIGAR SAURI*
Painful love story
Romance special


Writing by
*MAMAN MAMY (SHALELE)*

*Wattpad@mumies122*


*Dedicated to my close friend ikra Rukayyat*


*Devoted to identical twins hassan & Husain 80k*

*Small gift to my real fans*


*PROFICIENT WRITERS ASSOCIATION*


тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/

FACEBOOK: https://mobile.facebook.com/groups/2455147078097572/

TWITTER: https://twitter.com/pro__writers?s=09


Page > 3&4


*Muna saida kayan mata da na maza suna da kyau sosai kuma cikin sauki muna turawa koina ga me bukata seya tuntubi wannan number👉🏼 0806 672 6866*


*Wannan shafin na kune manyan mata mutanen Niger😊ina kuke yan Niger 🗣kufito Ku rausaya pagyn mallakinku...


Read / Download SHIGAR SAURI

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album