Join Our WhatsApp Group

HAUWA KULU Book 1 Complete Hausa Novel Document by HAUWA KULU Book 1


HAUWA KULU Book 1

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 36935



HAUWA KULU Book 1

Reading Time: 3 Hours

Added On: 03, Apr 2024

Author: Sumayya Abdulkadir Takori ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : 07030137870

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 194.03 kb

File Type: txt

Views: 209+

Download: 182+

Last download: 5 hours ago

Description/Story:  ‘YAR CIKIN BADALA
(HAUWA-KULU)


(Paid Book)
SUMAYYAH ABDULKADIR
07030137870
(whtsp only)

babbangoro2015@yahoo.com
takorikabara@gmail.com






WANNAN KARON SADAUKARWAR KACOKAM TA KANAWA CE, A DUK INDA KUKE, LITTAFIN YAR CIKIN BADALA SADAUKARWA NE GA DUKKAN MAKARANTA NA ‘YAN ASALIN KANON DABO





SHIMFIDA

NIGERIAN BAR ASSOCIATION
(CONFERENCE HALL)

W
ani irin cika dakin taron yayi, da manya da kananan lauyoyi wasu sun zo ne tareda iyalansu, wasu sun halarta babu iyali, a can gefe kuma a muhallin baki na musamman wakilan kungiyoyi ne masu zaman kansu (International NGOs) masu kare hakkin masu nakasa da tabbatar da ‘Equal Rights, Inclusion and Opportunities ga mutane masu bukata ta musamman.

Duk da cewa dakin taron bai cika girma ba, amma ya hadiye mutane da yawa da suka halarta. Wasu da yawa ba don taya ta murnar mukamin da aka bata yau suka zo ba, sun zo ne musamman don son ganinta ido da ido (don debe haso da kore shakku), na son tabbatar da jita-jitar da suke yawan ji akan cikar lafiyarta, a matsayin ta na ‘celebrity’ din Najeriya ga duniyar masu nakasa, wadda sunanta ya watsu, ya fantsama a kafafen yada labarai da soshiyal midiya. Haka muryarta ta dade da zamowa familiar (sananniya) ga kowa akan kwato hakkin nakasassu da kare martabar su (physically-challenged people) a arewacin Najeriya.
Wasu kuwa sun zo taron ne kawai ta hanyar ganin sakon gayyata a kafafen sadarwa wato sun zo ne don farin jininta shiyasa kawai suke son ganinta. Kwarai ita din mai farin jini ce ga kowa.
Kungiyoyin kare hakkin masu bukata ta musamman, su suka hada mata wannan taron na gani da ido (meet and greet), domin taya ta murnar karbar shugabancin kungiyar gamayyar lauyoyin kasa da aka fi sani da suna Nigerian Bar Association.
Wadannan kungiyoyin sun tsaya mata ne a dalilin tsayuwar ta tsayin daka wajen kare hakkin nakasassun arewa, da tsayawa cigabansu da ilminsu dana 'ya'yansu, karkashin hadin guiwarta da Sustainable Development Goals da kuma aikin da ta zaba na zama lauyar marassa 'yanci da physically-challenged persons.

Bayan kasancewarta SDG ADVOCATE har ila yau, lauya ce ita mai zaman kanta, wadda aikinta yafi karkata ga tsayawa less-privileged da wadanda basu da halin daukar lauya ko akaci zarafinsu adalilin nakasa ko aka take hakkinsu na 'yan kasa a dalilin nakasa, itace kan gaba wajen kare hakkin nakasassu a duk fadin arewa.

Lokacin data durkako dakin taron, wato (ta doso) cikin shiga ta kamala da kwarjini, hannunta yana makale cikin nasa, suna taku a hankali zuwa inda aka tanadar musu don tsayuwa tare. Sai aka mike don nuna girmamawa a gareta, da yawa yau da suka samu ganinta a zahiri sun ce a zukatansu "hakika *HAUWA* ganin ki ya fi jin ki!"
Duk da cewa wannan karon ma da bakin gilashin nata a idanunta. Hakan bai boye zahirin cikar zatinta da cikar kamalarta da iya adonta ba.
Bayan an zauna an nutsu, ta karbi lasifika ta fara da rero godiya ga duk mahalarta taron, da sauran zaqaquran lauyoyi 'yan uwanta, da kungiyoyin da suka hada mata wannan muhimmin taron gani da ido da gaisawa, kungiyoyin ne masu tabbatar da cewa, mutane masu bukata ta musamman sun samu rabauta daga duk wani matsatsi na rayuwa karkashin tallafin Sustainable Development Goals da take yi wa aiki partially, ta sake godewa kungiyoyin nan da suka roki ta fito yau, duniya ta ganta, a wannan ranar mai muhimmanci a gareta, kasancewar muryarta kadai aka sani a kafafan sadarwa, sun roki ta baiwa al'umma labarin ta, maiyuwuwa ya zamo inspiration ga al'ummar da suka samu kansu cikin kwatankwacin irin situation dinta.
Kungiyoyin sun hada da manyan kungiyoyin kare yancin masu nakasa da tabbatar da cigabansu wato kungiyar 'AGILE', da kungiyar 'Sight-Savers', sannan kungiyar 'Action Against Hunger' da 'PERL (Partnership to engage, Reform and Learn) '.
Ta kuma godewa manema labarai daga gidan rediyon BBC, karkashin jagorancin wakilin yada labarai na BBC a Kano, da gidan rediyon VOA karkashin jagorancin wakilinsu HAMZA MUSTAPHA MAWONMASE.

Sama da kowa, above all, and above all, tace tana godewa Uban ‘ya'yanta, wanda ta kira da suna My PACE-SETTER....".

Zazzakar muryarta ta cigaba da karade dakin taron ta cikin bututun lasifika, wadda murya ce da dama take familiar (sananna) ga kowa tun kafin bayyanar fuskarta a zahiri a ranar yau, a daidai sanda take cewa;

Kamar yadda kowa ya sani sunana na yanka Hauwa-Kulu. Hauwa shine sunan da aka yankamin rago dashi. Sau-tari idan na bushi iska musamman a lokutan nishadi na da son baiwa kaina farin ciki na kan bugi kirji in gayawa kaina da kaina,
babu wanda ya kaini samun yin kuruciya mai dadi!
Na kan yi tunanin ai nafi duk tsararrakina jin dadin dabdalar kuruciya, dalilina na fadar haka shine nayi kuruciyata ne a zamanin da hankulan kasarmu da jihohin arewa bakidaya suke a kwance, sannan kuma dukkan iyayena Uwa da Uba suke a raye tare, ina jingine jikin su musamman Innata, ina rabar ni'imar dake tattare da kulawar Uwa da ta Uba a tare, cikin rayuwar rufin asiri irin ta kowanne talakkan Bakano.
Nayi yarintata a sa'ilin da muke cikin shekarar nan mai tarin abubuwan bada labari a kasarmu ta Najeriya, zamanin da sojoji suka kwace mulki daga hannun sibiliyan koko in ce musu (farar hula) cikin shekarun (late 80s), wanda lokacin da wayona mulkin Najeriya ya koma hannun mulkin soja, bayan mulkin (Alhaji Shehu Shagari)”.

Hauwa ta cigaba da cewa a lokacin ana gudanar da wata irin rayuwa ne mai matukar sauki da hadin kai a tsakanin alummar jihar Kano, har ma da daukacin kasar Najeriya gabadaya irin wanda yayi karanci ko kuma ace babu shi sam! A halin da muke ciki a yanzu.
Ni Hauwa-Kulu nayi 'yammatancina a zamanin mulkin Shugaban kasa Janar Ibrahim Badamasi Babangida.
A wancan lokacin da muke zance, kwanciyar hankali shine babban arzikin da al'umma suka mallaka, suka Kuma wadatu da shi ba tarin dukiya ta yaki-halak yaki-haram ba.
Koko ince a lokacin Ubangiji yayi mana ludufin arzikin kwanciyar hankali da wadatar zuciya sama dana komai, wanda yafi tarin dukiyar yanzu alfanu ga dan adam alhalin babu kwanciyar hankali, godiyar Ubangiji ya wadaci zukatan al'ummar BADALAR Kano da kewayenta, saboda kowanne talakkan birni a zamanin, in kayi duba na tsanaki zaka ga cewa ya iyawa talaucin sa, dai-dai gwargwado kuma daidai misali jama'a basa cikin halin wahala da kaka-ni-kayi; tunda kowa yafi karfin hatsi, wato duk tsananin talauci ba zai sa a kwana da yunwa ba, saboda ba'a damu da cewa lallai sai an ci mai dadi ba, ko sai an sha koko da sukari, ko sai an ci abinci mai maiko da nama, ko sai an sha shayi da madara, gidan talakka da gidan mai kudi kusan duk irin rayuwa daya ake yi babu banbanci, abinci iri daya ake ci, babu yi wa juna rowa, haka suttura kusan iri daya ake daurawa tsakanin matayen cikin badala duka, daga na masu kudi har na talakkawa.

Sanin kowa ne a lokacin babu ta'addancin 'yan kasa da zaluncin shuwagabanni sosai, shiyasa ake cikin kwanciyar hankali da koshin ciki, wato babu masifar talauci da yunwar da har zata tunzura matasa sana'ar nan ta satar mutane da yin garkuwa dasu, sannan babu hadama da gasar rayuwa tsakanin mazauna badalolin Kano, kamar gasar motocin hawa, dana dogayen gine-gine, ko gasar sanya suttura mai tsada a tsakanin matan badala. Wannan a takaice shine misalin irin zamanin da ni Hauwa na taso a cikin sa, wato zamanin da duniya take a kwance lumui.
Babban kwanciyar hankalin da ake ciki a lokacin shine; al'ummar 70s da 80s basa cin bashin bankuna don su rayu, irin yadda ake ci a zamanin yanzu kamar yadda ake cin dussa, wai don biyan bukatun yau da kullum wadanda ba masu karewa bane.
Ga daukar zunubin kudin ruwa.
Shiyasa zaka ga duk tsananin talauci a lokacin iyayenmu basa cikin fargaba da zullumi, irin wanda tunanin bashi ke haddasawa magidantan yanzu, mai haifar da cututtukan kwakwalwa irin na damuwa da akeyi a zamanin yanzu wanda yake yiwa magidanta illa.

Hakan ya faru ne sakamakon cewa kowa yana da abin yi daga (sana'ar data karbe shi), ta kuma ishe shi rufawa kansa asiri, da biyan bukatun sa na yau da kullum batare da ya ci bashi ba. Kuma ba tareda yayi rayuwar dage ba.
Kusan kowanne mutum a cikin Badalar birnin Kano da kewaye (kauyuka da kananan hukumomi) yana rayuwa ne daidai shi kuma cikin farin ciki, yalwa da wadatar zucci, domin kullum cikin sa a koshe yake da *Gurasa* Tuwo, Dumame, Kunu, da Koko da Kosai (manyan abincin Kanawa).
A takaice, ko da a ce kai ne beran masallaci sabida talauci a zamanin can da nake yarintata a gaban Innata da Babana, zuwa balagata (‘yammatancina) nayi rantsuwa bazaka rasa abincin da zaka ci sau uku a rana ba.
A kullum ranar Allah tunanin Babana wanda anan unguwarmu ake kira "Baban Hauwa, dama na kowanne magidanci kamarsa na jama'ar dake zaune cikin kwaryar gidajen Badala da ganuwoyin garin Kano, shine; na yadda gobe idan garin Allah ya waye, karfe nawa zai yi sammako ya fita kasuwa ko wajen sana’ar sa??
Ba kuma don komai ba sai don samowa cikinsa dana iyalinsa abincin da zasu ci a yinin ranar.
Kowa ya san a lokacin fiye da rabin Kanawa yan kasuwar saye da sayarwa ne. Wannan ne yasa ba'a kwana ana jin yunwa, sannan za'a wuni a koshe. Kuma ba'a tara komai a banki ba, sannan hakan baisa sai an ci bashin kowa ba. Duk da hakan kuma ana zaune lafiya cikin farin ciki. Wannan ita ce hakikanin rayuwar da ake yi a gidanmu.
Ina farawa da baku labarina ni HAUWA_KULU tun daga tushena, ta hanyar dora shi akan katangar zamantakewar gidajenmu na Kanawa, wadanda aka fi sani da 'yan kwaryar BADALA, yanayin rayuwar iyayenmu na cikin Badala wata irin rayuwa ce irin mai ban sha'awa ga wanda ba Bakano ba.
Rayuwa ce wadda bako zai tafi gaba ya bada labara, tunda an ce wai Allah daya gari bambam.
**** **** ****

GIDAN MALAM BILYAMINU
T
sakar gidanmu mai fadi da yalwa ne sosai, irin ginin nan ne tun na 70s wato ginin Kanawan zamanin da, Gidan namu yana nan a bayan tsohuwar Badalar nan mai tsohon tarihi daga cikin Badalolin Kano, wato bayan Badalar Kofar Naisa, a lokacin nan ni Hauwa-Kulu, zan kimanta shekaru na da cewa ina yar shekaru goma.
Yalwataccen gidan namu duk da cewa a can cikin surkukin lungu yake, wanda ainahi mahaifina Malam Bilyaminu ya gaje shi ne shida dan uwan sa Malam Zakari, daga baya rigima ta hada shi da Zakari a kan gidan, wadda har ta kaisu gun mai unguwar kofar Naisa, aka ce zaaje kotu, inda mai unguwa ya hana, ta hanyar kawo shawarar bai kamata su je kotu alhalin sun fito gida daya ba akan abin duniya kararre, duk da ya san cewa Zakari ne mara gaskiya, don so yake ya gaje gidan shikadai, mai unguwa ya kawo shawarar daya ya sayarwa daya gidan, don a samu maslaha a tsakanin su. Don ya gaji da rabon fada tsakanin Bilyaminu da Zakari akan gidan gadon sunnan.
Don haka Zakari ya sayar masa da gidan, don a lokacin babu ta yi masa yawa yana neman abinda zai ja jari ne, kudin yafi bukata ba wai gidan ba shiyasa yakeso a sayar. Don haka gidan ya zama mallakin Malam Bilyaminu shi kadai bisa shaidar mai unguwa da makwabtansa, bayan ya biya shi kudaden da ya yanka masa da kansa, ko kusa bai zaci Bilyaminu zai iya biyansa wadannan kudin ba, don haka yana karba ya bar masa unguwar, ya koma kofar Dan agundi da zama, inda ya sayi karamin gida a can da rabin kudin, ya cigaba da sanaar sa ta wankin hula. Malam Bilyaminu kuwa saboda kaunarsa da gidan sai ya kara gyare shi daidai bukatar kowanne talakkan badala.

Gidanmu, gida ne na kasa da turbaya (gidan da aka gina da Laka), wanda aka bi aka sumunce shi tsaf da suminti, aka kuma shafe shi tas da farar kasa yayi haske gwanin shaawa. Tsafta da iskar shaqa sun wadace shi, kamar yadda tsaftar zuciya ta wadaci jamaar wannan gidan bakidayan su, wato Mallam Bilyaminu da matarsa Inna Safiya.
A kowanne wayewar gari ko yammaci, zaka samu iska mai dadi da shiga jiki na kadawa a tsakar gidanmu, musaman a lokacin hunturu, wannan ya samo asali daga manyan bishiyoyin da ke girke a tsakar gidan tun ginashi, na darbejiya dana itacen umbrella, zaka ga reshen bishiyoyin dake tsakiyar gidanmu na rangaji, idan iska na kada su, busassun ganyaryaki na zuba a kas.
Amma bazaka gansu sun bata tsakar gidan sosai ba, saidaima ka ga zanen tsintsiya da ya bi nan take ya share su, wanda ke nuna matar gidan, wato Inna (Safiya) wadda kowa ke kiranta da (Innar Hauwa), bata da kyuyar yin shara, abin nufi Innata jaruma ce wurin yawan kauda datti, koina ka shiga a gidanta zaka gan shi tsaf-tsaf gwanin ban kaye da dadin zama, kamar ba gidan dake cikin surkukin lungunan bayan Badala ba.
La-shakka ko lomar tuwon ka ce ta fadi kasa a gidanmu, za ka sunkuya ka...


Read / Download HAUWA KULU Book 1

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album