Join Our WhatsApp Group

RUWAN JIRA Complete Hausa Novel Document by RUWAN JIRA


RUWAN JIRA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 41386



RUWAN JIRA

Reading Time: 3 Hours

Added On: 21, Oct 2023

Author: Ummu Hairan ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : 09013718241, 09031307566

Book License : Paid

Category: Love Novels

File Size: 226.86 kb

File Type: txt

Views: 1260+

Download: 606+

Last download: 9 hours ago

Description/Story: *RUWAN JIRA.....*






*_Rubuta labari_*



*Fauzah* *(Ummuh Affan)*




*Dedicated to*

_Mijina Abdul Sidi Isah Haruna, son so fisabillillah_❤️



*1-2*


Kallonta yakeyi da shanyayyun idanunsa ya kalleta yace “Zuhura zaki dawo fah" murmushi tayi masa tace “Ya Nura baka rabo da abin dariya waye ya fada maka ni rayuwata da waiwaye a cikinta, bana waiwaye Yaya nura don Allah ka daina wannan mgnr sabo kakeyi" lumshe idonsa yayi yace “shikenan kije Allah ya bada saa amma nasani tabbas zaki dawo malamina ya fadamin hakan" bata bawa batunsa muhimmanci ba ta tsayar da dan sahu ta hau tayi masa bayanin inda zai kaita ya zaro kudin ya biya tayi masa godiya ta nufi gdanta.
A qofar gdan ya sauketa ta sanya mukulli ta bude ta shiga komai yananan inda ta tafi ta barshi ta sauke numfashi ta zauna tare da kunna TV domin hutawa idanunta nakan TV amma zuciyarta bata gurin tana gurin Yayanta Nuraddeen, jitayi an dafata ta dago da sauri tare da qaqalo fara'ar dole ta sauke masa tare da cewa “lahh hubby dama kana gida ai nayi tunanin baka dawo ba" zama yayi kusa da ita yace “ko yaushe idan kikaje gida kina dawowa da wani mood mara dadi Wanda nake kasa fahimtar inda ya dosa Zuhura meye yake sanyaki damuwa a yan watannin nan ne game da visiting din family house dinku da kikeyi?"



Qoqarin saita nutsuwarta tayi ta hadiye wani yawu me daci tace “ba haka bane Ahmad kawai halin da baba yake ciki shine yake damuna sosai Amma nasan insha Allahu zai samu sauqi" janyota yayi jikinsa yace “kiyi masa addu'a yafi wannan damuwar da kikeyi Ina kika baromin yarinya ta?" Sake narkewa tayi a jikinsa tace “tana gurin ummah harma Shafeeq din shima wai ya girma yaqi biyoni"
Narkar da ita yayi yace “shikenan sai muji dadinmu mu biyu ko?" Lumshe idonta tayi ta zura hannunta cikin gajeran wandonsa tace “abarnan taka bata qara girma kullum haka take Ahmad ka rinqa neman magani" zuba Mata ido yayi yana nazarin kalamanta tayi saurin cewa “aa bafa wani Abu nake nufi ba Ina nufin maganin rage jaraba My Ahmad ka fara damuna kayita qwaqulata ko gajiya bakayi" ajiyar zuciya yayi yace “yau na zakiyi bayani ne"
Daga haka suka miqe tace kaje masallaci ka dawo bari nayi wanka nima nayi sallah" fita yayi itakuma ta nufi dakinta tayi wanka tayi sallar magrib ta zauna tana addu'o'inta zuwa wani dan lkc ta miqe tayi isha ta fara shirin kwanciya bacci, tana gamawa ta haye gado ta kwanta gabadaya zuciyarta tana gurin Nuraddeen kalamansa sunayi mata yawo “Zuhura da rana daya cikin shekarun da mukayi bamu tare bantabajin kinyi rawa a zuciyata ba, bantaba hada sonki da na wata mace ba a duniya, Zuhura bansan ke rayuwata bace saida na rasaki, na rasa kowanne farin ciki don Allah ki yarjemin zan rabaki da Ahmad cikin sauqi banso Kuma bana fatan rabon dake yawo a tsakaninmu yayi kisa"




Gabanta ne yabada wani rass a bayyane tace “waye zai mutu kenan ni ko Abban Husnah?" Saurin girgiza kai tayi tare da kawar da tunanin a ranta daidai lkcn da Ahmad ya shigo ya kashe fitilar ya kwanta yana addu'a ya janyota jikinsa ya fara lalubarta tanason salon mijin nata amma yau ta kasa basa hadin kai data rintse idonta kalaman Nuraddeen ke dawo mata a haka suka raya daren bacci ya daukesu da mamakinta kamar yanda ta saba ko yaushe yau ma hakance tafaru mafarkinta sama da 10 years indai zatayi da namiji to Nura ne, ta miqe tayi alwala tayi nafila tare da roqon Allah ya yaye Mata abinda yake damunta,
Tanayin sallar asuba ta shiga kitchen kasancewar mijinta da wuri yake fita ta dora abin karyawa tana aikin wayarta tayi ring ta dauko ta duba taga baquwar number ta daga tare da sallama a daya bangaren aka amsa da cewa “qanwata kin tashi lfy?" Gabanta ne ya fadi ta dubi qofar da sauri tace “yaya Nura meye haka da safennan?" Ji tayi yaja numfashi yace “nakasa jurewa ne Zuhura inayin iyakar qoqarina amma abin yana neman fin qarfina zuciyata tana qoqarin rinjayata waini meye ma yasa nayi Miki saki uku ne har wani ya samu damar samunki...."




Katse wayarta tayi tana share hawaye taci gaba da aikinta tace “nikam na shiga ukuna Yaya Nura neman sanyamin wasu wasi yake a aurena" da haka ta gama girkinta ta jera a parlour ta nufi dakin baccinsu yana tsaye yanasa kaya ta matsa ta rungumeshi tace “morning Sweet" murmushi yayi yace “morning darling" dariya sukayi tare tajasa suka fita ta rinqa basa abincin a baki yanaci suna yar Hira kadan kadan bayan ya gama suka fice tare ya sauketa gurin aikinta shima ya wucce nasa,
Tunani ya hanata aiwatar da komai a haka Suwaiba tazo ta sameta tace “Zuhura ana nemanki a waje" dagowa tayi tace “waye" sunkuyar dakai tayi tace “Yayanki da yake zuwa gurinki kwanaki" zaro ido tayi tace “ki rufamin asiri kice masa kinje kin tarar na fita ta qofar baya" kallonta Suwaiba tayi tace “why?" Daganta hannu tayi tace “kawai ki fada masa haka" juyawa tayi ta fita bata jimaba ta dawo ta zauna suna facing din juna idonta na zubar da hawaye Suwaiba tace “subhanallahi waini meye tsakaninki da mutumin nan ne duk sanda zaizo sai kinyi kuka shima sai naga yana sharar hawaye don Allah ki kwancemin wannan qullin Zuhura"




Girgiza kai tayi tace “kada ki damu da abinda Bai shafeki ba Suwaiba komai da kikaga ya faru ya farune da amincewar Ubangiji Kuma yana cikin qaddarorin bawa Abu daya da zan iya fada miki shine Yaya Nuraddeen yayanane abokin wasana kuma tsohon mijina da mukayi auren saurayi da budurwa dashi yasoni ya nunamin qauna Kuma ya sadaukar da abubuwa da yawa domin ni a baya Amma ya kasa samun zuciyata qarshe a lkcn da na fara aminta dashi na farajin zanyi rayuwar dashi Kuma sai qaddara ta ratsa muka rabu rabuwar da cikinmu babu Wanda yasan dalilinta illah mun barwa Allah komai"
Jinjina Kai Suwaiba tayi tace “don Allah ki bani lbrn dalilin rabuwarku naji inason jin wannan labarin Zuhura inasonki da zuciya daya Kuma na fahimci kema kinason yayanki"









~@Ummuh Affan~
[10/18, 5:43 PM] MRS AGB SIDI: *RUWAN JIRA.....*


*Freedom writer's association📚🖊️*



*_Rubuta labari_*



*Fauzah* *(Ummuh Hairan)*




*Dedicated to*

_Mijina Abdul Sidi Isah Haruna, son so fisabillillah_❤️



_Am sorry Fan's littafin *RUWAN JIRA....* na kudine 300 ta wannan account 0255526235 Fauziyya Tasi'u Umar GTB_
_Ko Kati MTN ta WhatsApp akan wannan number 09013718241, ko VTU ta wannan number 09031307566_



_Ga masu buqatar karanta tsoffin littatafai na na kudi guda tara ga sauqi yazo da 1k dinki Zaki samesu documents gabadaya memakon a baya da sai kin biya 1800 kudai kada ku bari a barku a baya ta wannan account din na sama zaki biya kudinki idan kina buqata_

*3-4*



Lumshe idonta tayi kafin ta budeshi a hankali tace “eh hakane suwaiba wlh inason Yaya Nuraddeen fiye da yanda tunaninki yake baki Amma na haqura na rungumi qaddarata Allah daya kawo rabuwa cikin tarayyarmu yafi kowa sanin dalilin da yasanyashi yin hakan saboda haka na tura lamurana gareshi nasani tabbas zaiyimin magani Kuma zai kawo min mafita"
Daukar Jakarta tayi ta rataya zata fice Suwaiba tabi bayanta tace “da Allah na hadaki ki bani lbrn soyayyarki da Nuraddeen zanji dadi kuma zanji a Raina kin yarda Dani matsayin yar'uwa ba qawa ba" turus taja ta tsaya tare dayin Jim kafin ta dago tana gyara zaman glass dinta tace “ki bini bashi ranar Saturday kizo gidana nayi alqawarin fadenki biri har wutsiya"




Day wannan kalamin tasa Kai ta fice daga office din ta shiga motarta taja ta nufi gida yau gabadaya jin ranar takeyi wata iri komai ya kwance Mata takasa gane tsakanin fari da baqi komai duhu yakewa zuciyarta, tanayin parking ta shiga cikin gdan ta fada wanka ta fito ta dauki hijjab tasa ta nufi gdan da take Kai Shafeeq da Husnah ta daukosu ta dawo gda ta hadawa yaran abinci ta zauna,
A zahirance abinci take bawa yaranta amma badinin zuciyarta yana wajen Nuraddeen a hankali ta furta A'uzubillahi minasshaidanur'rajim zuciyarta takai qololuwa wajen shagala da tunanin abubuwa boyayyu da suka faru a baya idan ta tuno ranar da Nuraddeen ya dubi tsabar idonta yace ya saketa saki uku sai taji gabanta ya yanke ya fadi, ita da kanta take tambayar kanta ma'anar faduwar gaban nata.
Jingina tayi da jikin kujera zuciyarta nayi Mata suyar da tazama sabonta a wannan yanayin a hankali ta rinqa sauke numfashi yaran na binta da kallo har zuwa lkcn data miqe ta shige dakinta ta kwanta tana juya abubuwa masu wuyar mantuwa a zuciya, a wannan yanayin mijinta yazo ya sameta bataji shigowarsa ba sai jinsa da tayi a jikinta tana gwauruwar ajiyar zuciya ta tallafo kansa tanajin nutsuwa na kwararo Mata tace.




“Barka da dawowa Sweet" lumshe idonsa yayi ya dora bakinsa a kuncinta ya sauke Mata kiss me ratsa jiki yace “miss you luv Amma naga kamar akwai abinda yake damarmin ke kwana biyunnan don Allah meye gskyr lamarin?"
Qirjinta yayi kamar zai fado tayi saurin tareshi tace “I mean ka gane Ina cikin wani yanayi Ahmad" Jinjina Mata Kai yayi da alamun sanyawa zuciya karsashi yace “sama da ten months na fahimci haka bansan yawaita yimiki bincike ne shiyasa nake qyaleki course ke ba yarinya bace 27 years yaci ace kin saba da nemawa kanki mafita dear don Allah ki daina yawaita tunani yana lalata kwarjinin mutum musamman mace me qaramar qwaqwalwa irinki kinji?"
Lumshe idonta tayi har zuwa wannan lkcn zuciyarta harbawa takeyi tace “is ok mijina insha Allahu zan kwatanta cirewa kaji" lakace Mata hanci yayi yace “koke fah matata kinfi kyau da walwala fah" yanda yayi maganar ya sanyata murmushi shima yayi dariya yace “tashi kiyimin wanka" turo masa baki tayi yasa nasa ya lashe natan yace “kada ayi rejected request dina don Allah"




Bataso amma dolenta ta miqe ta fara rage masa kayansa shima yana rage Mata nata hardai suka cire komai ya sunkuyar da kansa ya kama boobs dinta a hannunsa ya dora harshensa akai taja numfashi tare da yin baya ya tallafota da sauri ya direta a gadon ya kashensu fitila ya fara lashe duk wata kafa da qofa ta jikinta,
Hakanan taji tanajin wata faduwar gaba da take neman hanata sukuni ta sanya hannunta da sauri ta ture kansa daga qirjinta yayi saurin mayarwa kawai sai taji zuciyarta ta karye bata ankara ba saijin hawaye tayi ya kwaranyo Mata a hankali cikin sautin da batasan ya fito ba tace “Yaya Nuraddeen ka barni zuciyata Babu dadi bana feel komai a rayuwata...."
Wani Abu Ahmad yaji ya caki qahon zuciyarsa ya dagata a tsorace yace “Nuraddeen Kuma Zuhura? Meye ya kawo sunan nan gdana Ina kika hadu dashi da har kike ambatona da Nuraddeen...." Rufe bakinta tayi da sauri tace “na shiga ukuna Ahmad don Allah kayi hqr wlh bansan sunan ya fito bakina b...."








*5-6*




Janye jikinsa yayi daga nata yana furzar da iska me zafi ya nufi bathroom ya sakarwa kansa ruwa jikinsa duk yayi sanyi Nuraddeen... Sunan yana qara amsa amonsa a kwanyarsa, ya jima a bandakin kafin ya samu damar fitowa ga mamakinsa sai ya isketa zaune ta hade Kai da gwiwa tanata gursheqar kuka,
Zama yayi kusa da ita ya sanya hannunsa ya dago kanta ta fada jikinsa da sauri ta rungumeshi qirjinta naci gaba da luguden da takejin kamar zai iya bawa zuciyarta damar yin tsalle ta fito waje tace “My Ahmad!" Yanda tayi furucin numfashinta na sarqewa yasashi saurin dago kanta yace.




“Wai meye matsalarki ne Zuhura kada ki jefamu cikin damuwa fah?" Bata iya furta masa kalma daya da zata bashi nutsuwa ba ta zame daga jikinsa ta dora kanta a saman cinyarsa tana shafa sumar dake kwance a sangalalinsa tana sauke numfashi, murmushi yayi na tausayin kansu yace “Zuhurah kina burgeni amma zurfin cikinki yayi yawa meye matsalarki?"
Shiru tayi kamar me bacci hakan ya sanyashi shima ya kwanta ya janyota jikinsa yana shafa bayanta da haka bacci ya daukesu, dasafe ya rigata tashi ya hada musu abin kari tana tashi yara angama shiryasu suka daukesu suka tafi Shafeeq gidan raino aka kaisa Husnah makaranta sukuma suka wucce gurin aiki dake juma'a ce ita yabarwa motar kasancewar tana rigasa tashi ma'anar hakan shine taje ta dauko yarsu.
Daya da rabi suka tashi ta shige ta dauki Husnah suka tafi gda suna shiga layin gabanta ya rinqa dukan uku uku ganin mota a qofar gdansu kallon motar takeyi sabuwa dal tayi horn megadi ya bude Mata ta shiga gdan tana daidaita parking dinta motar na shigowa ta fito riqe da hannun Husnah Shafeeq yana kafadarta ta zubawa motar ido, bayan shudewar wasu yan daqiqu ya zuro qafarsa ya fito ta sake bude idonta akansa dogon mutum kyakkyawa me cikakkiyar halittar mazantaka baqi irin baqinnan me kyau da qawata idanu wajen kallo.




Batasan ya iso ba Saida taji iska a idanunta tayi saurin dawowa hayyacinta tare da juyawa da nufin shigewa ciki yayi saurin riqe hannun Husnah yace “kin gama qaremin kallo kina hango ramata kin juya Zaki tafi Little Yaya Noor dinki ne fah ko kin mantane?" Wannan kalma tayi tasirin narkar da zuciyarta hawayen da take hadiyewa ya zubo Mata ta kalleshi da idanunsa da suke saukar masa da kasala yace “tun shekarun baya nayi Miki alqawarin mota burina bai cikaba sai yanzu naso siya Miki wacce tafi wannan abubuwa sunsha kaina Tsoho ya matsa sai na qara aure sun kasa ganewa Zuhura bazan iya zama da kowacce mace ba wlh indai bake bace....."
Sakin yarinyar yayi yace “da quruciyata Little zan auri mace ta hudu bayan ke itanma Kuma bazata rayu dani ba mahadina yana jikinki don Allah rabonnan ya tsaya haka ki dawo gareni kada na haukace Zuhura...." Bazata iya jurewa ba shiyasa ta shige gda a guje yabita da sauri yana kiranta amma ta murda mukulli a qofar ya daki qofar tare da ficewa da sauri sai yanzu ya tuna cewa ashefa gidan mijinta ne nan din"




Ta jima a zaune tana kuka a fili tace “aure! Yanzu aure Yaya Noor zai qarayi Innanillahi..." Da wadannan tunane²n ta shiga kitchen ta dafawa yaran indomie ta shige daki ta kwanta saboda har wani zazzabi takeji yana sauko mata, qarfe biyar Ahmad ya dawo tunda ya shigo idonsa akan motar yake yana shiga ya tarar da yaran sunata games a falo ya shige dakin ya tarar da ita rufe da bargo yace “Ina muka samu baquwar mota? Gabanta ne ya fadi ta dago tace “am... uhmmm... Dama Yaya Yunus ne ya siyamin..." Yanda tayi mgnr da in...Ina yasa masa kokwanto yace “tohhhh Kuma da izinin wa shi Yunus din ya siyanki mota?"
Shiru tayi batace qala ba ya miqe ya dauki wayarsa ya fita ya jima sosai sannan ya dawo ya dubeta...


Read / Download RUWAN JIRA

START READING

OR

DOWNLOAD TXT NOW
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album