Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

NAANAH Book 2 Complete Hausa Novel Document by NAANAH Book 2


NAANAH Book 2

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 13293



NAANAH Book 2

Reading Time: 1 Hours

Added On: 25, Jul 2024

Author: Nanameera ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATIONn

Author Phone : 09086030007, 07041901078

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 74.24 kb

File Type: txt

Views: 521+

Download: 301+

Last download: 20 hours ago

Description/Story: [1/4, 19:10] Nanameera: https://chat.whatsapp.com/DlFBkx450nJA8CYpdTTx8B


🌹🌹 *NANAH*🌹🌹




Story and written by:


*Nanameera*





*🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟*
{R.S.W.A}

https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, fad'akarwa, ilimantarwa da kuma nishad'antarwa_*
_(R.S.W.A)Ruwa kad'ai ke maganin k'ishi_

*Alk'alaminmu 'yancinmu*


🅿️.....3️⃣9️⃣&4️⃣0️⃣


____________✍🏻 Cikin jin haushi Nana ta ce " amma dai Hameeda bakida hankali, nufi kike agaban Daddy zance inason Jawad ?" murmushi ta yi ta ce " haka nake nufi Nana saboda hakan ne kaɗai mafitarki, idan kika faɗa masa haka zaiji haushi kuma jin haushin zaisa ya dinga kulawa da ke ko dan saboda kada ya ga kin kula wani " cikin gamsuwa Azrah ta ce " kuma hakane Nana kawai ki gwada idan an dace fine, in kuma bai yuhuba shikenan sai asami wata hanyar " ahaka suka ƙarƙare sannan Hameeda ta ce " kawai kedai Nana gobe kishirya kiyi kwalliya tare zamu zo da Jawaad " ohk Nana ta ce sannan sukai sallama kowa ya yi gida .....




Bayan ta yi wanka ta na zaune a parlour ta na cin salad saboda sha'awarsa da tayi akayi sallama aka shigo, ɗaga kanta ta yi ganin Jalhan yasa ta yi murmushi. Murmushin itama ta mayar mata sannan ta ce " Nana yau kece a parlour? ɗazu naji uncle na cewa wai Daddynki sun tafi abuja " cikin sanyin murya ta ce "Eh nima haka naji dana dawo amma ai anjima zasu dawo "



Ajiyar zuciya ta sauke ta kama hannunta ta riƙe ta ce "Nana kizo muje part ɗina mu zauna kinji " girgiza kai ta yi ta ce


"Bazan biki ba saboda idan Daddy ya ji labari faɗa zaimun" kallonta ta yi sosai ta ke tausaya mata ta ce


"Shikenan Nana babu komai, amma dan Allah Nana ki dinga cin abinci kodan abinda ke cikin ki kinji " ɗaga mata kai ta yi ta ce "toh zan dinga ci, nagode sosai " murmushi ta yi ta ce " babu komai Nana, amma dan Allah Nana ki ƙara haƙuri, nasan halin da kike ciki amma babu damar fitarda ke saboda haka ki dinga addu'a kuma ki dinga yiwa Daddynki kinji, kar kiji haushinsa domin Daddynki nasonki har gobe kawai dai shima baisan haka na faruwa bane kinji Nana " fashewa ta yi da kuka ta ce


" Daddyna baya sona kwata-kwata, wallahi Jalhan ji nake kamar na kashe kaina na huta daddy baya sona, baya tausayina, babu ruwanshi da halin da nake koda kuwa gani ya yi zan mutu wallahi bazai taimakeni ba " rungumeta ta yi ta ce


"Nooo Nana Daddynki nasonki, ki dinga yimasa addu'a shi ne zaki dawo da soyayyarki kinji " ɗaga mata kai ta yi, haka tayi ta bata baki har ta kwantar da hankalinta sannan ta tafi..........




Sai kusan ƙarfe tara suka shigo gidan, alokacin ta na kitchen tana girka indomie. Zama sukayi a parlour'n suna hira har ta gama dafawa ta fito don hucewa sama ta gansu a zaune, har ta yi gaba sai Hafsa ta hangi plate ɗin hannunta hakan ya sa ta ce


"Dear dan Allah kirawo Nana taban indomie ɗin hannunta wallahi ta ban sha'awa " ohk kawai ya ce mata kai kace Mama ce ta bashi umarni ya ce


"Nana zo nan"


Komowa baya ta yi ta tsuguna agabansa ta ce "daddy gani " kallonta ya yi from head to toe sannan ya ce " kibawa auntynki indomie zata ci idan yaso ke saiki sake dafa wata kinga ita ta yi tafiya ta gaji " tunda ya fara magana take kallonsa har ya idar sannan ta ce "daddy nima yunwu nakeji kuma bazan iya sake dafa wata ba wannan ma da ƙyar na dafa banasan ƙanshin dahuwarta ita ta tashi ta dafa " kallonta ya yi afusace ya ce " eehhhyy wato ni nake faɗar magana kina mayarmin Nana?, ni nayi magana bazaki ce toh ba " batai auneba sai jin mari ta yi har biyu, tsabar gigicewa tama kasa kukan sai ajiyar zuciya take, ya daka mata wata tsawa ya ce " tashi kiban gurin, shashasha kawai " da gudu ta shige bedroom ɗinta ta na kuka kamar ranta zai fita, bayan ta shiga ɗaki Hafsa ta kalleshi ta ce " haba dear ai da kabita ahankali yarinyace " tashi ya yi ya shige ɗaki bai ko bata amsaba, bayan taga ya shiga ta yi wani killer smile ta ce " aikin banza ai wallahi saina sa ka kasheta da hannunka " tayi wata dariyar mugunta sannan ta ja plate ɗin abincin ta faraci , bayan ta ci loma biyu ta ce " shegiya kuma ta iya girki".......




Misalin ƙarfe ukun dare ta farka banda yunwa babu abinda take ji ahaka har akayi kiran sallar asuba.....





Tun kusan ƙarfe shidda ta fito ta yi apartment ɗin Amma, ta na shiga ta huce kitchen ta yi ta dubawa ko zata samu abinda zata ci amma babu hakan yasa ta haɗa tea ta fito tabuɗe frigde ai kuwa ta yi sa'a akwai cake ta ɗauko, zama ta yi ta hau ci kamar almajira saida ta cinye tas ko kaɗan bata rageba sannan ta shiga ɗakinta ta kwanta, nandanan bacci ya ɗauketa......




Zaune suke suna breakfast wayarshi ta fara ƙara ɗagawa ya yi ya ce "Big bro! Allah ya taimakeka " can kuma ya ce " ohk nazo na ɗaukeka " sannan ya kashe wayar, kallonsa Hafsa ta yi ta ce " dear kai dawa?" murmushi ya yi ya ce " wallahi wai ya Aleey ne zaizo nigeria shine ya kira ya faɗa "

"Ohk ya Aleey'n kawu " ɗaga mata kai ya yi ta ce " Allah sarki ya daɗe bai zoba dan inaga har yafika daɗewa " tashi ya yi ya ce "gaskiya kam dan rabonshi da nan tun kan rasuwar Baba don baizo da mutuwar Baba ba, bari na shirya kafin yazo " daga haka ya shige bedroom......






Wajen ƙarfe tara suna zaune suna breakfast kasancewar Abba bai fitaba Nana ta fito daga cikin ɗaki, kallonta suke dan basusan ta shigoba har ta ƙaraso ta zauna sannan Amma ta ce "Nana yaushe kikazo?" turo baki ta yi ta ce " ɗazu kuna bacci, inajin yunwa kuma Daddy basu tashiba shine na tawo nan naci abinci na kwanta " lallaima toh ya miki kyau cewar Amma.


Murmushi Abba ya yi ya ce "toh yanzu kin ƙoshi ko zaki ƙara " tasowa ta yi ta zauna gefenshi ta ce " Abba zan ƙara " zuba mata Amma ta yi ta ce "karɓi " karɓa ta yi ta miƙawa Abba ta ce "Abba ka bani abaki kaji " ohk ya ce sannan ya fara bata abincin ta murmushi, girgiza kai Amma ta yi ta ce " Allah ya shirye ki Nana"........




Fitorwasa kenan, sanye ya ke da wata shadda gezner maroon colour ya yi kyau kamar ango Hafsa ta kalleshi ta ce " dear tafiyarce ?" ɗaga mata kai ya yi ta ce " baka turominba kuma yanzu nima zan fita " kallonta ya yi ya ce " oh sorry na manta nawama kika ce?" two million ta faɗa, murmushi ya yi ya ce " don't worry idan nashiga mota zan turo miki " dariya ta yi ta ce "thank you, Allah ya tsare " murmushi ya yi ya ce "Ameen" sannan ya yi waje......




Yana fito ita kuma zata shigo hakan yasa suka haɗu kallo ɗaya ta yi masa ta juya zata gudu ya kamota batareda ya ce mata komai ba ya kama hannunta sukai gaba, buɗe musu kofa guard ya yi suka shiga sannan sauran guards ɗin suka shiga ta su motocin sai convey ne ke tashi ahaka har sukai waje.....



Sai bayan daya tura mata kuɗin sannan ya kalleta ya ce" ke daga ina kike?, kuma ina makarantar?" turo baki ta yi gaba ta ce "gurin Amma naje naci abinci sannan kuma ni banida lafiya shiyasa banje makaranta ba " ta faɗa tana kallon waje. Jawota ya yi jikinsa ya ce


"Ohk wa kika faɗawa bakida lafiya?, kuma daman da safe ake zuwa gurin Amma ko bamuda abinci ne ?" fashewa ta yi da kuka ta ce "ni ka kyaleni babu ruwanka dani, karka sake kulani har abada " murmushi ya yi ya ce " ohk kwaci kan ki toh ko anfaɗa miki ni kulaki nake " yana gama faɗin hakan ya matseta ajikinsa, sosai take kokowar kwace kanta amma ta kasa hakan yasa tafara dukanshi tana cizonshi amma kamar bashi take yiwaba ahaka har ta haƙura ta yi shuru, kusan five minutes ya leƙata yaga ta yi bacci, murmushi ya yi ya gyara mata kwanciyarta kafin su ƙarasa.......





Zaune suke gaban malamin mai ƙirar aljanu ya na magana ya ce " kamar yanda na faɗa miki asirin ya kusa karyewa nan bada jimawa ba" cikin tashin hankali ta ce "malam to
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download NAANAH Book 2

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album