Join Our WhatsApp Group

A GIDANA Complete Hausa Novel Document by A GIDANA


A GIDANA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 151166



A GIDANA

Reading Time: 12 Hours

Added On: 06, Oct 2023

Author: Ayusher Muhammad ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 833.03 kb

File Type: txt

Views: 969+

Download: 781+

Last download: 5 hours ago

Description/Story: [10/27, 10:33 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: *A GIDANA*

In the name of Allah the most Beneficent the most merciful.
Praise be to Allah lord of the words.
The beneficent the Merciful.
Master of the Day of judgement.
Alone we worship;Alone we ask for help.
Show us the straight way
The way of those on whom Thou has bestowed the Grace, those whose portion
Is not wrath, and who do not go astray.


   Gaisuwa tare da jinjina da fatan alkairi gareku daukacin masoyana, ina mika sakon gaisuwa gareku, dafatan kowa yana lafiya, musulmai da suka rigamu gidan gaskiya Allah ya jikansu, mu da muke da rai Allah ya sa mu gama da duniya lafiya, masu ciki Allah ya saukesu lafiya, wadanda ke neman haihuwa Allah ya basu, masu neman aikin yi Allah ya taimakesu yasa su samu Ameen suma Ameen.
_Oh ina fatan me karatu yayi saurin cewa Ameen..... lol duk da nasan ke ko kai ka fada.........._

Dafatan za'amin uzurin jina shiru da akai😄

_Sai dai dan Allah inaso mai karatu yamin uzuri akan wannan littafin bazan samu damar yin posting kullum ba saboda wasu dalilai._

Nagode🥰

🍀 *A GIDANA*🍀

*_Na Ayusher Muhd_*

*Shafi na Farko*

Da sauri ta gama shafa hoda sannan ta dau dankwalinta ta daura, agoggo ta kalla sannan ta jawo jakarta da sauri, ta bude wardrobe ta dauko mayafinta ta rike a hannu ta fito.

Kitchen ta nufa dan tasan yana ciki, tana shiga ya juyo ya kalleta yace "Honey an fito?"

Rugumeshi ta matso tai tace "Yau wani irin bacci ne ya kammani dakyar ma bude idona."

Murmushi ya mata sannan ya sumbaci kuncinta yace "your tea."

Dauka tai ta kalleshi sannan ta sumbaceshi itama tace "Thanks love."

"Kin manta ni zan kaiki?"
"Oh! Ashe fa na sallameshi."

Kai ya girgiza yace "Honey a rage fada, dan Allah drivers nawa kika kora?"

"Ka zauna zani da kaina." Ta fada tare da juyowa, da sauri ya riko hannunta yace "na manta sune basaji."

Harararsa tai tace "wato ni uwar fada ko?"

"Nooo inji wa? Yanzu na dau mataki?"

Murmushi tai tace "ni ka bari na tafi da kaina yafi sauki."

Key dinsa ya dauko wanda ke saman fridge yace "muje."

Falo suka fito hannunsu rike da juna, Goggo suka gani zaune tana kallo a falan.

Kusa da ita ta karasa tace "Goggo ina kwanan mu?"

Goggo ta kalleta tace "ni jiya mantawa kikai kince zaki bani kudin anko?"

"Oh na manta, amma ni Goggo wai wani anko ne ku manya daku?"

Fuska ta hade tace "ba sai kin fadamin magana ba, in bazaki bani ba kawai kice bazaki ban ba, fadar maganar na menene?"

Kallan agogo tai ganin lokaci na wucewa tace "zan bashi sai ya kawo miki."

Da sauri tai gaba "ke wlh Goggo, ina laifin ki bari sai ta dawo? Bayan na fiki bukatar kudi yanzu."

Harara ta maka mai tace "wannan damuwarka ce, kuma wlh ka kawon kudina yanda aka baka."

Binta yai da gudu, tana tsaye gaban motarshi yai saurin bude mata sannan ya zagaya ya shiga gun driver.

Yana zama ya tada motar yaja suka bar gidan.

Mai gadin daya bude ta kalla tace "zan turama kudi kaba mai gadi nashi naga wata yazo karshe, sai kaba Goggo na ankon, dan ko tambayarta ban ba nawa ne."

Yai saurin cewa to, kallansa tai tace "ka cinye kudinka ne?"

Kallanta yai sannan yadan sosa keya, ajiyr zuciya tai sannan tace "zan turoma dan dama anyi albashi, sai dai Honey plz adan rage kashe kudi."

Kallar tausayi yai yace " sry Honey."

Murmushi tai ta riko hannunsa da hannunta dayan hannun koma ta dan kurbi tea dinta sannan ta sakeshi ta zuge jakarta ta dauko wasu takardu tana dubawa.

Kallanta yai yace "in kaka nustu kina aiki you look soo......"

Kallan data masa ne yasashi yin dariya ba tare da ya karasa ba, tace "Honey a nemo wani driver din."

Ajiyar zuciya yai yace "wannan karan bari muga wanda zamu samo wata nawa zaiyi."

Kallansa tai tace "zaka fara ko? Wannan sai ya shekara 2 zuwa 3"

Dariya yasa yace "muna fata, amma indai wannan Honey dince hmmm."

Takardun hannunta ta cigaba da dubawa hakan yasashi yin shiru.

Suna isa yai parking, kallansa tai tace "bari na turama yanzu yanda zaka cirar mata nata dana mai gadin."

Yace to.

Nan ta dau waya ta tura mai kudi sannan ta dau jakarta ta fito, harta kusa shiga taji ya kirata, juyowa tai ya taho da sauri rike da tea dinta ya mika mata, thanks ta fada tare da nuna cup din alama ta amsa ta gode.

Ciki ta shiga, tana shiga cikin bakin kofar ta hade fuska tamau, duk inda ta wuce gaisheta sukeyi tana amsawa tana wucewa.

Tana shiga office dinta ta ajiye jakarta da tea din sannan ta juyo ta fito, gun program din ta fara shiga, kallan masu aikin gun tai wadanda ke kokarin ganin komai ya tafi daidai tai tace " acanza wannan background din is too light."

Da sauri yace "okay."

Kallan jikin camera's din tai kafin tace "meye hakan? Sau nawa zance a rage contrasts din nan?"

Da sauri yace "am sorry, yanzu zan gyara."

Dan ajiyar zuciya tai sannan ta duduba hasken light din gun sai da ta tabbatar komai yayi ta kalli agoggo sannan tace "is live so you have to be extra careful."

Da sauri sukace okay.



*********

  Da sauri ya fito daga soronsa ya fita waje, dan yanda ake kwalla sallama sannan daga jin muryar ya fahimci wanene.

Dan dattijon na ganinsa ya murtuke fuska tamau ya kalleshi rai a bace yace "Khalid karka batamin rai kar kuma ka bata min lokaci bani kudina."

Khalid ne ya kalleshi yace "Malam Mamman dan Allah kayi hakuri, ga dubu daya dazun nan aka biyani kudin fenti, gobe insha Allah......."

Dubu dayar ya amsa yace "karfa ka maidani dan iska, nan nan ubanka yai hatsari kazo kamar zakai min kuka na ara maka dubu goma ka kaishi asibiti yau wata hudu kenan amma haryanzu dubu biyar ka bani da wannan ta yau kenan, nifa shi yasa banasan harka da matsiyata wlh, ubanka yaki barinka kai aikin noma wai shi a dole sai kayi boko, to dakagama bokon uban me ka tsinana? Uban me kake dashi? Dubu goma ta gagareka biya a wata hudu? To wlh ni bazan dauki iskanci ba."

Khalid yace "kayi hakuri insha Allah zuwa karshen watan nan zan hada maka."

Tsaki yaja sannan ya wuce yana tafe yana masifa.

Shiru khalid yai sannan ya wuce ciki.

Mahaifiyarsa na tsaye a tsakar gida yana shigowa ta matso tace "Malam Mamman ne ko?"

Murmushi yai yace "eh amma bakomai Umma, ina Asiya? Ta biya kudin makarantar dana bata jiya?"

Tace "ta biya, haryanzu ba labari?"

Yace "Karki damu Umma insha Allah zan samu aiki."
Idanunta ne suka ciciko tace "shekara 4 kenan da gama karatunka, sai dai haryau babu labari sai uban wahalar siyan form kake kana zuwa yin jarabawa."

Murmushi yai sannan ya danyi gaba yace "kiyi tamin addu'a, lokaci ne."

Kallan tausayi tamai, ciki ya shiga inda mahaifinsa ke kwance ba lafiya, saboda hatsarin motar dayai wanda yasa kafarsa daya ta samu matsala, ya dade yana sana'ar tokin mota sai dai lokaci daya tsautsayi ya hau kanshi komai ya zama labari.

  Kusa dashi yaje yace "Abba kanasan wani abu ne? Dan zan wuce gun sana'ar mu ne."

Hannunsa ya riko yace "Allah ya taimaka, in inasan wani abu zan sanar da mamanka."

To saina dawo.
Abinda ya fada kenan ya mike.

Abba yace "adawo lafiya Khalid."

Fitowa yai daga dakin ya kalli Umma yace "na wuce."

Wayarsa ce tai kara ya dauka da sauri, Salmanu! Ya?"

"Kana ina?"
  "Ina danbatta ya akai?"

Salmanu yace "zaka samu zuwa kano yanzu? Dan wlh wani aiki ne muka samu gidan akwai maiko, kai sauri kazo."

Da sauri Khalid yace "turomin address din gani nan zuwa."

Nan ya kashe wayar yao waje da sauri.

Jakarsa kawai ya dauka a soro ya fita, yana zuwa ya samu mota ya hau ya nufi kano.


**********

A bangaren Adamu kuwa yana ajiyeta yai wata yar kara tare da duba account dinsa, gani kudi yasashi yar taka karamar rawa daga zaune, da sauri ya juya kan mota ya nufi Atm, yana zuwa yaciri kudin Goggo da za’a bata dana mai gadi, sannan ya ciri dubo goma yasa a aljihu, kida ya saka a motar yana tafe yana kada kai, yau akwai jin dadi a majalisa.

Jin dadin yanayi yasashi kawai yai ta dan yawo a gari, nishadi kawai yakeyi ji yake duk duniya ba wanda ya kaishi jin dadi.

Tsayawa yai yana kallan wanda ke kokarin tsalaka titi.

Fuskar sa ya kara kallo sai dai ya tsallaka titi, da sauri yaja mota ya nufi gefen titi yana binshi.

Horn din motar dayajine ya sashi dakatawa, juyowa yai cikin mamaki dan dai ba tare hanya yai ba.

Juyawa yai zai cigaba da tafiyar sa yaji ance “Danbatta.”

Cikin mamaki ya juyo, bai gane mai maganar ba hakan yasa ya dan matso kadan.

Hannu ya daga mai tare da nunashi yace “Danbatta kaine wlh.”

Khalid ya kalleshi yanzu kam ya ganeshi cikin mamaki yace “Adam?”

Dariya Adam yai yace “Danbatta cinye duu daga ina haka?”

Yace “daga danbatta saukata kenan.”

Shigo na karasa dakai.

Kallansa yace “karka damu yanzu zan nemi taxi ko bus.”


Dariyar dake neman kofcemai ya kara dannewa yace “shigo dalla.”

Ganin suna bata lokaci yasashi zagayowa ya shiga.

Adam ya kalleshi yace “ikon Allah, kwaro ashe da raban zan ganka.”

Ran Khalid yadan soso sai dai bai nuna ba yace “inasu Zakar?”

“Suna nan lfy, sai dai duk yanzu kowa hidimar gabansa yakeyi, kasan yanzu Zakar yana aiki a kaduna, Mansir kuma yana aiki a Abuja.”

Khalid yai yake “masha Allah.”

Adamu ya kara kallan jikinsa yace “kwaro ya? Kaifa? An fara aiki? A wani asibitin ko babban company?”

Khalid ya kalleshi yace “me kake nufi?”

Adamu yai dariya yace “me nake nufi kuwa? Kawai dai naga ne kai jarabawarka bazata wahalar dakai ba, duk fa shekararmu kai kadai ne ka fita da A class kaga kuwa ai kai sai babban company.”

Adamu ransa ya baci, kallansa yai yace “ai ba wannan bane hujja komai lokaci ne.”

Kai ya jinjina yace “haka.”

Sannan ya ja mota, shiru sukai kafin Adamu yace “yanzu dai ba aiki kenan kake san cewa ko me?”

“Eh.”
“Oh Allah kenan yanda kaci karatu waya taba kawo haka?”
Kallansa yai yace “saukeni anan, anan zan sauka.”

Nan?

Khalid yace “eh.”

Adam yai parking sannan yace “to ya? Ko na samoma aiki? Dan ni bana aiki kasan ni banasan wahala sannan jarabawa ta ma dai to, sai a hankali, sai dai matata akwai kudi, tana neman driver ko kana sha’awa na samoma?”

Kallanshi Khalid yai cikin mamaki, Adam yace “ya? Baka yarda bane? Wlh bana aiki, sai dai ta ko ina a jiki nake.”

Khalid yace “ba laifi.”

Har ya bude motar zai sauka Adam ya zaro kudi yace “ga wannan.”

Khalid ya kalleshi yace “no, karka damu.”

“Na manta ashe Mr Right ne, nasan bazaka amsa ba, amma ga numberta in kanasan aikin kamin magana.”

Numbersa ya rubuta a jikin paper ya bashi.

Khalid ya amsa kawai ya fita rai a bace.

Adam yana ganin ya fita ya tuntsire da wata muguwar dariya, da sauri ya kira Zakari.

Nan ya fesa mai, ya kira Mansir shima ya fesa mai.

Dariya kam yashata har cikinsa sai daya amsa, sai a lokacin ya tuna ashefa baici abincin safe ba......

Khalid kam yana sauka ya nemi taxi ya karasa inda zaije.


*Ayusher Muhd🏌🏻‍♀*
[10/27, 10:33 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: 🍀 *A GIDANA*🍀

Haske Writers Association💡

Shafi na biyu

Wattpad/@AyusherMohd.

******

  Khalid yana sauka ya wuce inda Salmanu yamai kwatance, ganin anata aiki agun yasa ya gane ya iso, da sauri yasa hannu ya dauko wayarsa ya kirashi.

Jiki a sanyaye Salmanu ya daga yace "Khalid!"

"Na iso, kana ina?"

Salmanu yace "bari nazo." Ya kashe wayar.
Bai jima ba sai ga shi nan ya fito, Khalid na ganinsa ya matsa gun da sauri yace "ya? Har an fara?"

Cikin rashin jin dadi Salmanu yace "Khalid kayi hakuri wai mutanen da sukeso sun isa, ma fada musu akwai sauran daya da zai karaso yanzu sunce wai a'a iya mutum biyar zasu dauka."

Murmushi yai tare da dan dafashi yace "bakomai, shiyasa duk kai wani iri?"

Kallansa yai yace "Allah duk abin ne yaban haushi, gashi ni kuma wlh kudin nakeso kasan ina tara lefe da wlh na barma kayi."

Khalid yai dariya yace "Just forget, kaidai yanzu ka shiga kayi aikinka, kafin kai laifi."

Salmanu ya dauko dari biyu yace "gashi dan Allah na asarar mota dana saka."

"Kai ka sani? Ko na sa kaina?"

Salmanu yace "ni na saka wlh."

Khalid ya zare hannunsa daga kafadarsa yace "Good luck ni nayi nan."

Yai gaba ya barshi rike da dari biyun, Salmanu ya bishi da kallo a ransa yana jin haushin wannan lamari na kasarmu, bazai manta yanda Khalid yai karatu a makaranta ba, duk wani abu da za'ai a faculty's dinsu, shine yake wakiltarsu, shine yi musu tutorials da sauransu amma dan bashida hanya gashi nan ko karamin teaching ya kasa samu.

Khalid kam yana tafe yana tunanin kalaman Adam, ba shakka ransa ya sosu da yanda ya mai magana, dan duk wanda ya kalleshi ya kalli yanayinsa yasan yanayine na dauriya da wahala, amma wai tambayarsa yakeyi wai wani company din yake aiki?
Murmushin takaici yai tare da sa hannu a aljihunsa, dauramai dari uku.

Ajiyar zuciya yai dan wata yunwa da yakeji gashi kuma kudin motar komawa ma yamai kadan.

Mezai danyi yadan samu kudin da zaici abinci ya kara kudin mota?

*********
"Duka duka anan muka kawo karshen shirin mu na Yammacin mu a Yau, sai mun hadu daku a shiri na gaba.

Ni Zainab Aliyu Tahir nake cewa mu huta lafiya."

Ana dauke camera daga kanta ta shiga bubuga kafadarta saboda dan gajiyar datai, kallanta staffs din gun sukai sukace "Hajiya akoda yaushe ke ta dabance, in kina shiri gaba daya komai tsayawa yakeyi, mu kanmu rasa wayar da zamu dauka da texts din da zamu karanta mukeyo."

Kallan mai maganar tai tace "kuma sannunku da kokari."

Ruwan dake gabanta ta dauka ta sha sannan ta mike tace "Ina Ramla?"

Bata nan, dazu kuma tana nan a tsaye.

"A ce mata ta sameni a office."
Ta fada tare da wucewa.

Zama tai a office dinta tare da daukan wasu takardu tana dubawa.

Knocking din datajine yasa tace "shigo."
Ramla ta shigo cikin yanayin tsoro dan ta tabbatar laifi tai, ko kofar bata maida ta rufe ba ta watso mata takardun dake hannunta.
Gaban Ramla ya fadi ta kalleta a tsorace.

"Me kika dauki media?"
Murya na rawa tace "media? Aunty Zee?"

Fuska ta daure sosai, tace "ya akai kika samu aiki a nan?"

Bakinta na rawa tace "munyi interview......"

Bashi nake...


Read / Download A GIDANA

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album