Join Our WhatsApp Group

BAYAN RAI Complete Hausa Novel Document by BAYAN RAI


BAYAN RAI

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 78157



BAYAN RAI

Reading Time: 6 Hours

Added On: 25, Apr 2024

Author: Jeedderh Lawals ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : +234 816 492 9724‬

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 428.02 kb

File Type: txt

Views: 246+

Download: 188+

Last download: 3 hours ago

Description/Story: BAYAN RAI! BY Jeedderhh....


[5/2, 10:39 PM] ‪+234 816 492 9724‬: 💕🐾•°•° *BAYAN*•°•°🐾💕
💕🐾°•°• *RAI...*°•°•🐾💕


*JEEDDERH LAWALS*


🐾°•01•°🐾


GARIN KANO
Tafe take cikin natsuwa mai tattare da kwantaccen nishadi a kawatacciyar fuskarta. Budurwace mai kimanin shekaru ashirin da uku zuwa da hudu, ba zaka gane yanayin kalar fatar ta ba, ita ba fara ba, ba kuma baka ba, haka ba zaka kirata da chocolate color ba, a takaice dai tana da wata irin kala ce ta daban. Wani babban gida mai wargajejen gate irin mahadi-ka-ture dinnan ruwan gold take dosa, sai data tsaya suka gaisa da wasu maza biyu dake zaune a can gefen gidan a karkashin bishiyar umbrella a zaune suna hira sannan ta shiga gidan, nan ma sai da ta tsaya suka gaisa da maigadi gidan cikin girmamawa kafin ta bi wata siririyar hanya mai shimfide da grass carpet wadda zata sadaka da ainihin main parlour na gidan.

Cikin siririyar murya tayi sallama falon ta shiga a nutse, kamilalliyar dattijuwa dake zaune a cikin falon tana kallon tashar Saudi 1 idanunta saye da farin medicated glass na kara karfin gani, ta dago ta dubi inda mai sallamar take shigowa bakinta ya motsa a hankali wajen amsa sallamar, fuskarta ta dan washe da fara'ah lokacin da tabi budurwar da kallo yayin da take zama a kan carpet din gefen kafar dattijuwar. Hajiya Karima ta kalleta a nutse tace "Rayyanatu, har kin dawo kenan?" ta gyada kai a nutse kuma cikin girmamawa tace "ehh Ummie, Hajiya Tabari tace tana gaishe ki sosai" fuskarta ta kara washewa da fara'a sosai tace ina amsawa kuwa.... Yara sun kusa dawowa, yakamata ki hanzarta ki dora abinci kafin su dawo koh? Ta amsa da toh Ummie. Har ta mike taji Hajiyar na cewa.., "Modibbo yace yau sakwara yake son ci, don haka sai a cire shi cikin namu abincin ki mishi nashi, kin dai san irin yadda yake son sakwarar shi tayi" ta koma ta kara rusunawa tace "Ehhh Ummie, za ayi in shaa Allahu" Ummie tace to madallah.

Dakin da aka ware mata ta fara shiga ta cire kayan jikinta ta sanya wasu sannan ta shiga kitchen din, ta duba time table na abinci ta ga jallof rice ne da farfesun kayan ciki ne abincin daren yau, don haka ta hau shirye-shiryen komi. Ta fereye doya ta dora bisa wuta, sannan ta fito da kayan ciki daga cikin freezer ta wanke su tas ta dora akan wuta bayan ta zuba wadatacciyar albasa da citta, ta kuma dora shinkafa. Doyar na dahuwa ta sauke ta ta dauko turmi ta fara aikin kirbi, kafin kace me! ta hada zufa sharkaf. Ta dan dakata tayi tsaki a fili tace "haka kawai a dinga saka mutum yin wahalar banza, yanzu haka duk wahalar dakan wannan da nasha nasan a banza zata tashi tunda ba wani ci za ayi ba, don dai kawai halin mugunta da son a wahalar da mutum, an san ba za aci abu ba amma sai a saka shi girka abu mai wahala..." Ta kara jan wani tsakin da yafi na dazu tsawo..., "aichhh! I cnt really understand wat's in dix guy's head, he's a total jerk... Very selfish...!" daga kan wannan da za tayi sai idanunta biyu cikin nashi... Tsaye yake a kofar kicin din ya harde hannayenshi biyu a kirji sanye da shadda bugaggiya dinkin Abacha sai dai kanshi babu hula, akwai alamun ya dan jima a wajen babu mamaki duk zagin da ta dinga auna mishi sun shiga kunnuwanshi. Gabanta ya bada sautin dararasss!! kamar fadowar gini, ta zaro wasu dara-daran fararen idanuwa tass kamar madara, ta shiga motsa dan karamin bakinta amma sautin maganar taki fitowa......




🐾💕💕💕🐾
[5/2, 10:39 PM] ‪+234 816 492 9724‬: 💕🐾•°•° *BAYAN*•°•°🐾💕
💕🐾°•°• *RAI...*°•°•🐾💕




🐾°•02•°🐾

Wani irin murdadden mutum ne mai wani irin murdadden hali da fahimtar inda ya saka gaba ke matukar ba mutane wahala, hatta da iyayenshi kuwa. Miskili ne na gaban kwatance.
Ya karasa shigowa cikin kicin din a hankali kuma cike da ginshira, ba zaka taba fadin ga yanayin da zuciyar shi da fuskar shi ke ciki ba, sai ma wani guntun murmushi daya saki wanda siraran fatar lebbanshi ne kadai suka nuna yayi. Ya bude fridge ya dauko ruwan faro ya bude ya daddaka, bai kara kallon inda take ba ya doshi hanyar barin kicin din hannunshi rike da sauran ruwan a cikin robar. Ta bishi da kallo tana marmara idanuwa kamar ta saki ihu har ya gama fita daga kicin din kafin ta sauke idanunta cikin saddakarwa ta maida su kan sakwarar ta dan rankwashi kanta "ohhh! Wat did I jst do? Oh my....!" "....idan kin gama a ajiye min a karamin dinning..." kamar daga sama ta tsinkayi muryar tashi, ta zabura ta mike tsaye, sai kuma ta kara komawa ta zauna dabas. Cikin rawar murya tace "uhhh??.. Toh... Toh..." ya dan saki guntun murmushi ya juya. Ta dafe kai tace waiyoo!! Yau na bani ni kam. Cikin sanyi da rawar jiki ta gama aiyukanta na ranar.
Tana cikin yin wanke-wanke taji hayaniyar yara suna shigowa cikin falon, ta danyi murmushi tace yara an dawo kenan! Ba'a jima ba taji an rungumota ta baya, an kuma rufe mata idanu a lokaci guda, tayi dariya tace Hauwa.... Adam.... A tare suka saki dariya kafin Adam daya rufe mata ido ya saki ya zagayo ta gabanta ya rungumeta yana cigaba da dariyar da yake yi. Ta hadesu gaba daya ta rungume a jikinta na tsawon lokaci kafin ta sake su ta shafa kawunan kowannen su tace "oyaa, magriba ta gabato maza aje a cire kaya ayi sallah, yau sai bayan Isha'i zamu yi lesson ok??" Hauwa tace "toh Anti, amma ai ke zaki ja mu sallahr koh?" tayi murmushi tana shafar kanta "a'ah, aiki nake yi sosai yau, kuje wajen Ummie" a tare suka amsa da toh, suka fita daga kicin din da dan gudunsu ita kuma ta mike ta cigaba da wanke-wankenta.

Bayan sallahr isha'i suka yi lesson kamar yadda ta musu alkawari, a dakin ta baro su suna tilawar Al-qur'ani ta fita falo ta tattara kwanukan da aka yi amfani dasu zata wanke. Kamar yadda tayi tsammani, ba a wani ci sakwarar data kirba da yawa ba. Ta ja wani dan guntun tsaki tana tattara kayan, tace Allah ya isa na wahalar da aka bani. Fita tayi da sauran ta mikawa mai gadi ita kuma ta koma ciki ta kimtsa komi, ta duba agogo lokacin karfe tara na dare. Hijabi ta saka ta fita, a harabar gidan taci karo dashi yana ta kai kawo hannunshi daya saye cikin aljihu da alamun waya yake yi, da yake farfajiyar gidan akwai wadataccen haske sakamako bulbs da aka saka, yadda ya mata kallo daya ya kawar da kai itama sau dayan ta kalleshi ta watsar, kanta mike ta bude gate ta fita.
Makotansu ta shiga wanda tazarar gidaje uku ne a tsakaninsu. Shima babban gida ne mai kyau, masu manya-manyan motoci ne jibge a harabar ajiye motoci, wasu an rufe su ma da tamfol saboda ba kasafai ake hawansu ba. Ta danna kararrawar dake manne da kofar falon aka mata izinin shiga, ta tura kofar a hankali ta shiga falon. Yana ganinta yayi fara'a sosai, itama dan guntun murmushi ta saki ta nemi waje ta zauna suka gaisa a dan tsaitsaye, ta lalubo first aid box a karkashin karamin teburin da yake a tsakiyar falon ta isa gefenshi ta zauna. Hannunshi ya mika mata, ta fara warware bandeji dake a babban dan yatsanshi ta wanke raunin har ya fara kafewa ta manna mishi plaster, nan yayi mata godiya sosai, ta hada kan kayan ta mayar inda suke, daga nan suka yi sallama ya rakata har bakin kofa bakinshi dauke da godiya, murmushi kawai take yi har ta bar falon. A tsakiyar dakinta ta same su sun bararraje suna ta shakar barci, ta ciccibe su daya bayan daya ta kaisu dakinsu ta kwantar dasu bayan ta shafe su da addu'o'in tsari sannan ta koma nata dakin, bandaki ta fara shiga ta rage mararta ta dauro alwala ta dawo ta canza kayan jikinta zuwa doguwar riga mai rangwamen nauyi ta barci, ta rufo dakinta tare da kashe wutar dakin ta nufi dan karamin gadon dake gefen dake shimfide da tattausan zanin gado ta kwanta, idanuwanta ta lumshe tana bude su a hankali, wani dan tattausan guntun murmushi ya subucewa fatar bakinta, addu'ar kwanciya barci tayi ta janyo filo ta kankameshi kam a kirjinta kamar mai tsoron a kwace mata shi, a haka barci yayi awon gaba da ita.

••••••••••••
Da sassafe ta fito ta fara gyaran falo kamar yadda ta saba dama tuni ta kammala shirya karin safe, ta shiryawa su Adam lunch box nasu, ta shiga dakin yaran ta tashe su ta musu wanka suka yi sallah sannan ta shirya su cikin kayan makarantarsu suka fito falon, iyayen na kan dinning suna karyawa, Rayyah ta duka ta gaishe su cikin girmamawa, suka amsa mata. Kicin ta koma don ta ida sauran ayyuka kafin su gama karin. Suna gamawa ta raka su Adam har gaban motar da direba ke jiransu zai kaisu makaranta, ta bude bayan motar ta ajiye musu jakunkunansu da hade da lunch box, ta shafa kawunansu tace bye! Suka hada baki suka ce take care! Tayi murmushi yayin da direba yaja motar suka tafi ita kuma ta koma ciki. A dan corridor mai shimfide da grass carpet suka ci karo da ita, ta ci ado kamar wadda zata je modeling sai tashin kamshi take kamar a kamfanin turaruka sai wani yatsina take yi, ta mika mata keys din dakinta ta amsa, bata furta uffan ba ta wuce sai itace ta bita da Allah ya kiyaye hanya. Safeenah Biebie kenan!!




Jeedderh🐾

5/2, 10:39 PM] ‪+234 816 492 9724‬: 💕🐾•°•° *BAYAN*•°•°🐾💕
💕🐾°•°• *RAI...*°•°•🐾💕




🐾°•03•°🐾

Wata irin dariya ce ta kubce mata lokacin data shiga dakin Biebie, ta tsaya tana karewa dakin kallo kamar ba dakin mutum ba, ko ina kaya ne a zube da littafai dasu takardu duk a watse babu ko wajen saka kafa, kai kawai ta gyada ta fita daga dakin ta koma nata, drawer ta bude ta ciro wata sullubebiyar wayar Samsung edge silver tayi latse latse na en mintuna, kafin ta mayar da ita inda take ta rufe drawer din ta fita falo. Kai tsaye dinning ta nufa da niyar tattara kayan da akayi kari dasu, bata taba tsammani da mutum a wajen ba sai data mika hannu da niyar fara hada plates sai kawai ta ga mutum a zaune yana karyawa, ta ja baya cikin razana da ganinshi da kuma mamaki, ta shiga bashi hakuri kamar zata fashe da kuka, hannu kawai ya daga mata alamun ta tafi, cikin sauri ta juya ta fada dakin yara cikin hardewar kafa. Ta rasa dalilin da yasa duk lokacin da er magana ta shiga tsakaninta da Modibbo take tsintar kanta cikin rawar jiki. Daga bangarenshi shima kallo ya bita dashi, yana ji a jikinsa yasan wannan halittar, not the face, but the personality. His mind kept telling him that yasan ta amma a ina? Duk lokacin da zai ganta sai gabanshi ya fadi, faduwar gaban da take tuno mishi da wata wadda a dalilinta ne har yau ya kasa ganin ko wace diya mace da gashi, to him kowace mace yana kallonta ne kamar namiji dan uwansa. Wannan dayar dai daya rasa tana ina yanzu cikin duniyar nan? Ko wane hali take ciki yanzu?? Take idanuwanshi suka canza kala, zuciyarshi tayi bakikkirin, abincin da bai kammala ci ba kenan ya warci briefcase dinshi ya fita. Kamar wanda zai tashi sama haka ya warci motar cikin matsiyacin gudu ya bar gidan. Sai data ji fitar shi ta iya fitowa daga dakin ta gyara falon, sai a lokacin ta samu ta karya. Wanka ta shiga, kafin ta fito tayi shirye-shiryen da zata yi karfe sha daya da rabi ta wuce, don haka ta dora girkin rana kawai.

°°°°°°°°°°°°
Ranar Laraba da yamma a harabar gidan, Rayyah ce da makocinsu Samuel zaune akan fararen kujerun roba suna hira. Gidan babu kowa, kowa ya tafi wajen aikinshi wasu kuma sun tafi wajen karatu. Maigidan Alhaji Abbas dan garin Yola ne amma aiki ya kawo shi Kano har yayi aure anan, don haka Kano ta zamo mishi gida yanzu, babban controller ne kuma dan kasuwar Electronics daga Japan zuwa Nigeria don haka bai cika zama a gidan ba saboda tafiye-tafiyen shi, matar gidan kuma Hajiya Karimah er asali garin Takai ce ta jihar Kano tana aikine da ma'aikatar lafiya ta jihar Kano. Yayin da babban dansu Abdul-Ra'ouf da suke yiwa lakabi da Modibbo saboda sunan Baban Alhj Abbas ne yaci, babban likitan fata ne a asibitin Aminu Kano, sai Safeenah da take bi mishi suna mata lakabi da Biebie tana kazantar Elect. & comm. Engineer a ECE, sannan en biyu Hauwa da Adam dake primary 5 a makarantar Nurul-Huda Islamic school ce, kullum sai yamma suke dawowa. Don haka idan gari ya waye kowa ya kama harkar gabanshi, Rayyah kadai ake bari a gidan wadda ta kasance mai aikinsu watanni biyu da suka wuce, amma sabon da suka yi da mutanen gidan musamman yaran kai kace ta shekara dasu sai dai fa banda mai karkataccen hali Modibbo, don shi ba a ma zancen shi.

Sau tari idan ta gama ayyukan gidan, kadaici ya kan dame ta, gashi ita ba gwanar kallace-kallace bace. Sai ta fara fita tana dan zagaya anguwar, a haka ne suka hadu da Samuel, tun dai suna gaisawa a tsaitsaye...


Read / Download BAYAN RAI

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album