Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

SHAREEF SEXY BOY BOOK 1 Complete Hausa Novel Document by SHAREEF SEXY BOY BOOK 1


SHAREEF SEXY BOY BOOK 1

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 159004



SHAREEF SEXY BOY BOOK 1

Reading Time: 13 Hours

Added On: 26, Jul 2024

Author: Nafisat Isma'il Lawal ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : PERFECT WRITER'S ASSOCIATION

Author Phone : 07065334256

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 806.27 kb

File Type: txt

Views: 1154+

Download: 3360+

Last download: 1 day ago

Description/Story: [04/01, 11:59 am] OumƊahirah نفيسة: 🌱🌱🌱🌱🌱

      *SHAREEF*
             _SexyBoy_
🌱🌱🌱🌱🌱


_Writer: Nafisat Isma'il Lawal_
_Wattpad: UmmuDahirah_

*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT🧝*



*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞

```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)```

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

       *P.W.A✍️*










__________
*BOOK1*
_______________*FREE PAGE1to2*
             Malam Sama'ila Abashe; Mutum ne mazaunin Zaria cikin anguwan Ƙofan kibo, sana'ar sa shi ne jan babban mota, yana bin babban Motan ɗan gote. Shi yasa kodayaushe ba wai ya cika zama bane, idan ya tafi wurin sana'ar sa ya kan yi fiye da watanni uku before ya dawo. Ya jima Allah bai sa yayi aure ba; don sai da yakai aƙalla shekaru arba'in sannan Allah ya ba shi Matarsa wacce ya aure ta a gida, bazawara ce kuma yar uwansa ne, tunda tayi aure bata taɓa haihuwa ba har Mijin ya rasu, bayan fitowan ta shi kuma yace, "yana sonta zai aure ta."

Kowa a dangi yayi murna tunda bai taɓa zancen aure ba sai a wannan karon, ko an kawo mishi Mace ba ya auren ta sai ya gudu zuwa Legos idan aka matsa mishi, a haka dai yake shashantar da zancen har ga shi da lokacin yin sa yayi, dama aka ce aure lokaci ne, baza ka taɓa yi ba idan har ba lokacin ka ne ya zo ba. Ga shi sai a wannan karon Malam Sama'ila ya samu Samira ya aura

Sun yi aure cikin rufin asiri tunda Allah yana buɗa mishi sosai, baya ga jan Motan yana sana'o'i na siye da siyarwa a can inda suke zaune. Yanzu haka ya gina sabon gidan sa a nan Ƙofan Kibo sun tare da Matarsa. Suna zaune lafiya babu wani CeCe-kuce a tsakanin su, suna mutunta junansu matuƙa tare da taimakon juna, domin tunda aka yi auren Samira take ɗan saye da sayarwa na kayan miya. Shima tun lokacin da yayi auren ya rage daɗewa a can garin, ya kan yi wata ɗaya ko fiye sannan ya dawo, zaman su son Barka kowa yana sha'awar su

Abun da suka soma fuskanta shi ne rashin haihuwa, tunda tun sanda aka yi auren yau kimanin shekaru biyu kenan Samira bata haihu ba, ga shi Allah ya zuba mishi son ya'ya tunda yayi auren nan. ya kan ce, "yana son ganin ƴaƴansa tunda yanzu lokacin sa ya soma tafiya, ya fara manyanta ga shi bai yi aure ba sai Yanzu."

Yanda yake damuwa shiyasa itama Samiran ta soma damuwa, tunda ta san cewa daga ita ne matsalar kasancewar tayi wani auren bata haihu ba. Malam Sama'ila bai fito fili ya gaya mata wata magana mara daɗi da zai tayar mata da hankali ba, amma a yanda take ganin shi da kuma yanda yake ƙaunar yara, bai da zance sai maganar haihuwa, ga yawan damuwa a kan fuskarsa shiyasa ta gane halin da yake ciki, kuma ta san tabbas ya damu da ya ga ƴaƴan sa. Shi yasa a wata rana ta zaunar da shi tayi masa maganar ƙarin aure, tace, "ita a ganin ta tunda ba ta haihuwa bai kamata ya zauna haka nan ba, ya ƙara aure domin ya ga ƴaƴansa, ita ta yarda ta amince ya auro ko wace ce."

Da farko bai amince da maganar nata ba, har an shafe kusan rabin shekara da tayi mishi maganar. Ganin ta matsa da zancen dole ya amince yace mata, "shikenan zai nemo."

Su ma iyayensa sun ba shi goyan baya tunda hakan shi ne maslaha, bazai zauna babu ya'ya ba dole ya nemi wata, duk da wannan ƴar uwansa ne amma ba an yi don a wulaƙanta ta bane, bare suna matuƙar ƙaunarta kasancewar ta mai hankali da natsuwa, akwai son jama'a da  faram-faram.



               Da yin maganar bai fi wata uku ba ya samu Mata a nan A.B.U Samaru, sai dai ita budurwa ce kuma yarinya ce sosai, Allah ya haɗa su a can Kano lokacin ta je hutun makaranta wajen ƴan uwan Babanta. Dayake kuma tana son shi shiyasa nan da nan ta ba shi dama suka soma soyayya, basu jima ba ya tura gidan su tunda shi ya ƙosa ya ƙara auren

Sai dai iyayenta sun ce, "sai dai ya jira har ta ƙarisa karatun ta tunda bai fi wata biyar ba."

Kuma ya amince, shiyasa ya nemi a saka ranan auren zuwa lokacin. Aka saka ranan auren ya ci gaba da neman ta

A hankali - a hankali biki ya zo tunda komai aka saka mishi lokaci zuwa yake yi. Aka sha biki Amarya Bilkisu ta tare

Allah da ikon sa kuma sai suka fara zaman lafiya da Samira sosai, tamkar Ƙanwa da Yaya tunda Samiran tana da hankali matuƙa, bata ɗauki Bilkisu a matsayin kishiya ba sai Ƙanwarta kasancewar ta girme mata, ta riƙe ta da amana sun zauna lafiya. Haka itama Bilkisun tana girmama ta kamar mahaifiyarta, komai ita take mata ba ta barin ta tayi komai, idan ka shigo gidan za ka yi tunanin uwa da ƴa ce tsaban biyayya da girmama juna

Kowa yana cewa, "Sama'ila yayi dacen Mata." Tunda kowa sha'awar su yake yi. Duk yanda Mutane suka so su shiga tsakanin su abun ya faskara tunda soyayyar junansu a jinin su yake

Allah da ikonsa da shigan Bilkisu ta samu ciki, sai dai kasancewar ba mai laulayi bane shiyasa basu gane ba sai da yayi kusan watanni biyar. Sun yi murna matuƙa tunda har sun cire rai a tunanin su shima Sama'ila yana da matsalar ne. Nan aka je asibiti da ita aka duba ta komai Lafiya, daga nan ta ci gaba da zuwa asibitin tana awo

Daga lokacin kuma Samira ta amshi komai na gidan ita take yi, ta hana ta komai tace, "baza ta sake yin aiki ba sai ta haihu."

Amma Bilkisu ta ƙi yarda tace, "tunda cikin ba mai wahalar wa bane Ita dai ta barta ta riƙa yi, shima ƙarin lafiya ne ga cikinta tunda motsa jiki zata yi."

Shi yasa Samira ta ƙyale ta tana yin wasu abubuwan, amma ba masu wahala ba

Cikin ikon Allah lokacin haihuwa ta haifi ɗanta namiji sak irin Babansa kamar an tsaka kara. Zo ku ga murna a wurin familyn nan, domin kowa yayi murnar zuwan Yaron nan duniya, tamkar ba a taɓa haihuwa ba a dangin su saboda ƙauna

Sai dai kuma Allah yayi nufin Malam Sama'ila bazai ga girman Yaron sa ba, yanda yayi murnan zuwan Yaron nan ko abinci ba ya iya ci tsaban bai da lokacin kansa sai na yaron, wuni yana hannunsa tunda aka haife shi. Ana gobe suna aka kira shi a kan an yi mishi lodi. Farko yace, "bazai je ba saboda gobe ne sunan ɗansa." Amma Matansa suka dage sai ya je tunda idan bai je ba zai iya samun matsala, ƙarshe ya rasa Motan ma, shi kansa ya san da haka, but tsaban ƙaunar ɗan shi ne yasa ba ya son ya jirga ko nan da can. Shi yasa da suka matsa mishi sai yace, "to shikenan tunda kun matsa zan je, amma bazan wuce sati ɗaya ba in sha Allahu zan dawo. Ga Yarona nan kafin in tafi zan bada kuɗin rago, zamu yi magana da Yaya Shehu komai na sunan zan ba shi, Yaro na raɗa mishi Ahmad Allah ya raya shi."

"Amin Amin." Suka amsa mishi cikin farin ciki. daga nan suka sake sallama dashi sannan ya bar gidan bayan ya haɗa ƴar Jakar shi

To tafiyar kenan wanda basu kai can inda zasu je ba; Allah yayi mishi cika wa sakamakon mummunan hatsarin da suka yi, ko gawan su ba a samu ba sai toka

A sanda labari ya riski Matan sa sai suka yanke jiki suka faɗi a nan take. Aka yi da su asibitin Ƙauran Wali domin basu taimakon gaggawa. A can jini ya ɓalle wa Samira ashe itama cikin take dashi, wanda babu wanda ya sani sai Allan da ya ɓoye kayan sa, ko ita bata san cewa tana da juna biyu ba ashe har ya kai wata Bakwai. A take a nan ta soma naƙuda cikin wahala ta haifi ɗiyarta Mace

Lallai Allah gagara misali ne, mai raya wa kuma mai kashe wa, ga shi ya ɗauke Uba ita kuma ƴa ta zo. A sanda ya amsa sannan yayi musu kyauta

Hakika babu wanda bai ji mutuwar Malam Sama'ila ba, su kansu Matan shi an rasa kansu domin ba kaɗan ba mutuwar tayi muguwar ratsa su, musamman ma Samira; tunda ita sai da tayi kusan kwana goma a asibitin tana fama da kanta, haihuwar ta zo mata da matsala sosai, ga kuma rashin Mijinta wanda yasa ta damu ta kasa kwantar da hankalinta, tayi jinya sosai tunda hawan jini ne ya kama ta. Daga baya aka sallame ta

Already an sanya wa yarinyar suna Hafsah duk da babu wanda aka yi suna. Daga Ahmad har Hafsan,
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download SHAREEF SEXY BOY BOOK 1

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album