Join Our WhatsApp Group

FULANI Complete Hausa Novel Document by FULANI


FULANI

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 54403



FULANI

Reading Time: 4 Hours

Added On: 05, Nov 2023

Author: Khadeeja Candy ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : 08036126660, +22790165991

Book License : Paid

Category: Love Novels

File Size: 278.73 kb

File Type: txt

Views: 2396+

Download: 889+

Last download: 5 hours ago

Description/Story: 03/12/2021, 08:04 - Messages and calls are end-to-end encrypted. No one outside of this chat, not even WhatsApp, can read or listen to them. Tap to learn more.
03/12/2021, 08:06 - 🤐🤐🤐🤐: *🐄🐄 FULANI 🐄🐄*


By Khadeeja Candy


1

_©®Hakkin mallaka nawa ne ni kadai, ban yadda a saffaramin labari ta kowace siga ba tare da izinina ba, yin hakan kuskure ne babba a kiyaye⚠_

*FICTION.*

FREE PAGE.

FALMATA POV.

Yola...

Tun tana surfen da kuzari har ta kai bata iya daga tabaryar da karfi, babu komai a tare da ita sai tarin yunwa da gajiya ga wani uban ciwon kai da ya saka ta gaba. Cike da dauriya ta
karasa surfen sannan ta risina tana kwashewa tana zubawa a kwayar da ke gefen turmen, sai da ta kwashe shi tas sannan ta hade da sauran da ta surfe, mikewa tai tsaye tana rike da surfen ta nufi gurin tukuyar ruwansu.

"To mai kunne kashi ban fada miki idan kika yi surfenki ki rika zuwa bohal kina debo ruwanki ba? Ke wai Fulani sau nawa za ayi miki magana ne?"

A wahale Falmata ta kalli Tumba wacce ke mata maganar, ta amsa mata tana jin kamar ta fadi a tsakar ranar da ke dukan kanta.

"Inna idan na gama zan je na debo wasu sai na cika"

"Ban yarda ba, kije ki fara debowa ki yi abunda za ki yi wannan wanda kike debo mana na aiki ne bana wankewa wasu banza surfe ba"

Uffan bata sake ce mata ba, sai ta nufi gindin bishiyar dogon yaro ta aje surfen, sannan ta sake komawa ta dauko wani katon bokoti ta riko shi a hannu ta nufi kofar fita jiki ba gwari, tafiya take a hankali kanta a kasa bata kallon kowa sai hanya, gaisuwar girmama ce abunda yake fitowa daga bakinta sa'adda duk tai arba da sa'ar iyayenta. A yayinda ta isa bohal din sai ta nemi guri ta tsaya tana ta kallon yadda fanfon bohal din yake cike da mutane yara da manya. Matsawa ta kara can gefe tana daga zanenta kamar mai kyankyamin ruwan da ke zube a kasa.
Kallo daya za ka yi mata ka karancin irin natsuwa da tarbiyar dake tare da ita, sa'aninta na gaban fonfon suna gogoriyon dibar ruwa ita kuma tana tsaye gefe abunta tana kallonsu kamar ba diban ruwan ta zo yi ba.

"Falmata kawo na baki bokiti daya"

Cewar Khadija kawarta, abun ka da mai nema sai tai saurin cira kafa ta isa gurin da Khadija take tsaye rike da kan fonfon ta mika mata bokitinta.

"Na gode kawata"

"Karki damu, indai akwai mu ba kya rasa komai kawata"

Khadija ta fada tana daga mata gira, murmushi ne ya fadada kansa a fuskar Falmata ya bayyana fararen hakoranta wanda ya karawa bakar fatarta sheki.

"Yau ba za ki je gidan Sarki ba? Kin san fa ke ce mai gyara dakin yan uku da kula da su"

Khadija ta tambaya tana daga muryar wai dan mutane da ke gurin su san kawarta na aiki a gidan Sarki. Wata irin kunya ce ta rufe Falmata abun ka da bakauyen mutum sai duk ta ji ta muzanta.

"Ke Madam ba za ki ba yau?"

"Na tafi, har na dawo sai kuma gobe"

Ta amsa mata kamar ana matso maganar daga bakinta, gaba daya kunya ta gama rufe ta, kamin bokitin ruwan ya cika duk ta tsawwala, bokitin na cika Khadija ta kama mata ta dora a kai sannan ita ma ta dora nata suka kamo hanya tare.

"Mtswwwww Wallahi Falmata ba ki hadu ba, wai ina son ayi kurin nan ke kuma kin wani noke ba ki ma son amsawa"

Abun nan dai da ya zame mata al'ada ta yabawa fuskarta, wato murmushi sannan ta soma magana da muryarta mai taushi da dadin sauraro.

"Khadija kunya na ke ji"

Wani banzan kallo Khadija tai mata.

"Kunyar me? Aikin a gidan sarki? Allah ya kai Khadija Wallahi har tafiya sai na sauya"

Wannan karon dariyar marar sauti Falmata tai, tana jinjina lamarin kawarta, daman can indai kaudi ne da iyayi da ba ni na iya ba dai Khadija ba.

"To ai na ga ni ban wani dade da fara aikin ba, da har za a ce na fara kuri wannan zuwan da nai dazun fa shi ne zuwana na uku, kuma ni na ga..... "

Sai kuma yai shiru bata karasa ba, sai dai karara yanayinta ya nuna akwai damuwa a tare da ita kamar yadda fuskarta ta nuna akwai tarin maganganu a kasan halshenta.

"Miya faru?"

Tsayawa tai tana kallon Khadija kamar yadda Khadijar ma ta tsaya tana kallonta.

"Sai na ke ganin kamar ba su yarda da ni ba...."

Fuskar Mamaki Khadija tai.

"Ban gane ba?"

"Kin ga tun da aka dauke ni aikin, har yanzu ban ga yaran ba, sai dai na gyara dakinsu, kuma idan zan gyara sai a saka dogari ko wata baiwa sun tsayaa dakin har nai na gama"

"Suna da wulakanci ne?"

"Aa har yanzu ba a taba min ba, ban ga alamun hakan a iyalan gidanba, sai dai da alama suna da wuyar aminta da mutum"

Hannu daya Khadija ta saka ta daga kafadarta.

"Karki damu, daman su yan sarauta basa saurin aminta da mutun, amman dai da sannu za su fahimci kawata mutuniyar kirkice su aminta da ita"

Ta karasa tana dariya tare da rika fuskarta.

"To Allah yasa"

"Amin, kuma bari na fada miki ba wai saboda wannan bakar Tumba ta tura ki aiki dan ki samo mata kudi ba, ba wai duk abunda aka ba ki za ki bata ba, albashin ma rabi za ki bata ki boye rabi, dan alherin idan kin samo karki kuskura ki bari ta gani, ke abinci wannan ma da ki kawo mata Wallahi kara ki ɓarar dashi a akwata"

Har wani yatsine fuska Khadija take tana jin kamar ace ita ce a matakin Falmata take da step mother kamar Tumba da Allah kadai ya san irin sherin da zata kulla mata.

"Mahaifina yace idan ban mata biyayah ba be yafe min ba, ko da ace bata san yawan kudin aikin ba zan bata dika balle kuma ta riga ta sani, idan ma na hana ta zata iya duka ko taja Baba da kansa ya doke ni, ba ni da wani yanci a gidan nan Khadija kin sani"

"Hmm ai har da ke Wallahi da kike biye mata, ke ko yar ketar nan ba ki iya ba, Wallahi da ni ce da sai ta sha wuya, shiyasa na tsani shegiyar matar nan bakar Tumba kawai"

Falmata da dai bata ce mata komai ba, ta cigaba da tafiyarta, sanin kanta ne idan zata ce Khadija ta daina kiran Step mom dinta gatsasa sau hansin sai Khadija ta aikata sau dari biyu.

"Ki duba ki ga fa saboda ki Wahala ta tura ki aiki a gidan, ga yayanta, muna wai dan tsabar zalinci tace ita zata karbe albashin, bayan babu abunda take tsinana miki"

Tafiya suke Khadija na jifar Tumba da kalamai marasa dadi, Falmata dai bata ce mata uffan ba har suka raba hanya, kowa ya dauki hanyar gidansu. Da sallama ta shigo cikin gidan amman aka rasa mai amsa mata kamar masu gaba da ita ko kuma wadanda ba su ji sallamar ba. Ko kadan hakan be dame ta ba, inda da sabo kusan ta saba da wannan rayuwar. Kallo daya tai ma Naja ta dauke kai ta hade wani abu daya tsaya mata a makoshi, yar gata kenan masu yin yadda suke so a gida ba kamar ita ba, wacce aka hana wanke surfen da ruwan da ita da kanta tai aikin jigilar debo su da safe, an bar yar gaban goshi tana wanki da su.

Sai da ta sauke ruwan sannan ta nufi gurin da surfen yake ta dauko ta wanke, ragowar ruwan ta juye a karamin bokiti ta shiga bandaki tai wanka, dakinsu ta nufa ta shafa mai abun ka da mai son kwaliya sai ta dauko ragaggin kayan kwaliyarta ta tai kwaliya har da su jan baki. Ta yi kyau sosai duk kuwa da kasancewar ta baka sai dai bakin be rage ta da komai ba daga kyaun sura kwarjini ta halitta da kuma cikar sura da zati irin na ya mace. Baka ce amman ba mummuna ba, baka ce kyakkyawa irin kyau ne mai shining. Bakinta mai kyau ne wanda ya kara fito da manyan idonta kuma farare tas, sai dai bayan ido da hakora da tafin hannunta da na kafa babu sauran wani gurin da fari ya bayyana a jikinta. Yana daya daga cikin dalilin da ya saka Falmata bata sha'awar saka bakin kaya, domin ganin take ita da tufafin za su saje ne.
Bayan ta gama shiryawa ta mike tsaye tana cigaba da kallon kanta a madubi kamin ta maida dan karamin madubin a mazauninsa da ke cikin kayan kwaliyarta.
Tsakar gidan ta fito ta nufi kitchen dinsu ta dauko abinci da ke rufe a langa (Kwano) ta zauna jikin kitchen din ta soma ci tana ta kallon awakin gidan da ke ta aikin kuka suna fada da junansu, sun ɓata turkensu sun masa kacha-kacha kamar ba dazun ta gama gyara shi ba. Can kuma ta maida dubanta gurin mayan shanun da ke daure guda biyu a gafen garken awakin.

"Idan kin gama ki taso ga surfen masarar nan ki surfa ko tiya daya ne"

Kam ta gama cin abinci Tumba tai mata furucin, a take yanayinta ya canja tai narai narai da fuska kamar ta fasa kuka.

"Inna ba kin ce sai gobe ba"

"To masu masarar yau suke son abunsu, kuma da safe ai sai dabobi su samu abunda za su ci"

Kalma daya idan ta kara fitowa daga bakinta ta san ba tasha ji da dadi daga bakin Tumba. Bata da wani zabi da ya wuce ta gama cin abinci ta taje tai surfen kamar yadda ta umarce ta. A hankali tai ta cin tuwon marar har ta gama ta tashi ta nufi gurin butarda ke gindin ice ta wanke hannunta sannan ta nufi gurin da masarar take ta dauka ta bude turmi ta fara surfawa. Tsakanin fara surfen da sallamar Maman Baby makociyarsu ba zaka iya tantance wanda ya riga wani ba. Tumba da ke tsakar gidan ta amsa sallamar tare da kallon Falmata da sauri.

"Kina da son wahalar da kai Fulani, ina ke ina surfe da tsakar ranar nan? Dan Allah ki aje har zuwa anjima ko kuma idan Naja ta gama wanki sai ta surfa"

Kallonta kawai Falmata tai ta sadda kanta kasa ta cigaba da surfen.

"Aa zan iya"

Sai kuma ta fada kasa-kasa idanuwanta na cika da kwalla, haka take mata a duk lokacin da wani a shigo gidan ko kuma idan a gaban mahaifinta ne. Kowa a unguwar ya shaidi Tumba akan kaunar da take nunawa Falmata agaban idanuwansu, wani lokacin har da ita ake bada kwacen matar uba wacce ta rike yar kishiya da amana.

"Oh Tumba ikon Allah, ke dai ba ki kaunar ganin Falmata tana aiki"

Cewar Maman Baby tana dariya.

"Mahaifiyarta amana ta bar min ita, idan ina ganin tana wata wahalar sai na rika ganin kamar na ci amanar mahaifiyarta"

Daga inda Falmata take tsaye tana surfen ta dago manyan idanuwanta masu kamar madara ta kalli Tumba wacce ta shantake da makociyarta suna fira ta sadda kanta kasa ta cigaba da surfe idonta tab da kwalla...!

FADIME POV.

Katsina State...

Shanun na gaba ita kuma tana biye da su a baya tare da karenta, hannunta rike da yar karamar sandarta ta dukan shanun, tana sanye da tufafin riga da zane na fulani gashin kanta a cinkushe. Sosai hankalinta yake akan ko wace shanuwa da ke gabanta, zuciyarta cike da fargaba da zullumi irin wanda ya saba ziyartar a duk sa'in da ta fita da shanun. Ba ta natsu ba har sai da ta isa da shanun a gurin da ta saba tsayawa da su, sannan ta nemi guri ta zauna saman wani karamin dutse ta zuba musu ido.
Haka take wuni a cikin tashin hankali da fargaba a duk lokacin da mahaifinta ya tura kiwo, ba tsoron kiwon take ba, ba dan bata saba ba, sai dan fargabar abunda zai samu shanu a duk lokacin da ta fita da su.
Ba kasafai take zuwa kiwo ta dawo da shanun lafiya ba, wani lokacin a hanyar tafiya wata zata mutu, wani a hanyar dawowa wani sa'in ma har sai ta iso gida.
Tun shanun suna arba'in da uku har sun dawo sauran goma sha bakwai.
   Mikewa tai tsaye tana kallon wata bakar mage mai jajayen indanuwa, wacce ke tsaye saman dutsen da ke gabanta, ba yau ta saba ganin magen ba, kusan kullum idan ta fita kiwo sai ta ganta, tun tana tsorota har ta daina, sai dai su yi ta kallon kallo ita da magen, sai dai a duk lokacin da tai arba da magen sai tsigar jikinta ta tashi, tsakanin ita da magen aka raba mai daukewa wani ido, ba m kamar magen da ke kyakar hakora.
  Can dai Fadime ta nemi guri ta zauna ta dauke kanta daga kallon magane da take, ta maida hankalinta gurin shanunta.

WASIN RAU POV.

As usual, yau ma sai da hasken rana ya fara haska kyakkyawar fuskarsa sannan ya bude idonshi a hankali yana kallon birds din dake saman icen suna rera masa waka kamar yadda suka saba a ko wace safiya.
Lumshe ido yayi sai kuma murmushi ya biyo baya mafarkin da yai yake kokarin tunawa, jinke hannunsa yai gam yana maida numfashi a hankali tare da dantse hakoransa.
Kamar an tsikareshi sai kuma yai saurin bude idon yai hanzarin saukowa daga kan icen ya doro kasa, jikinsa ya girgiza har sai da kowace gaɓa ta jikinsa ta motsa.
Babu riga a jikinsa sai dai hakan be hana shi jin zafi ba, duk kuwa da irin tsananin sanyin da ake kasancewar yanayin safiyar yau a akwai hadari da ya karade ko'ina a sararin samaniya.
For the first time a yau yaji a kasa yake sha'awar yin busar sarewa abunda be taba ba, a kowace safiya a saman dutse yake yin busarsa mai dadi saurare da kawarda duk wata damuwa. Jingina yai jikin icen ya ciro sarewarsa ya kafa bakinsa ya soma busar cikin kwarewa da shauki, a take duk dajin ya dauka, yanayin haduwar hadarin da kuma busar sarewar, da iskar da ke kadawa sai ya bada wani kalar yanayi na musamman wanda ko wace irin halitta zata so kasancewa a ciki. Sai da yai busar ya gama sannan ya kai hannunsa a gefen walkin da ke jikinsa ya kwance wata yar karamar jakar tsaba ya bude bakinta ya zubo hatsin da ke cikin jakar a hannunsa ya watsawa tsuntsaye a kasa, a take suka sauko kasa suka baibaye gurin suna ta cin tsabar har wasu na hawa kan wasu, kallomsu yake suna cin abinci har sai da idonsa ya gundura da abincinsa sannan ya juya ya kama hanyar shiga cikin burninsu.
  ...


Read / Download FULANI

START READING

OR

DOWNLOAD TXT NOW
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album