Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

SANADIN BOKO Complete Hausa Novel Document by SANADIN BOKO


SANADIN BOKO

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 98001



SANADIN BOKO

Reading Time: 8 Hours

Added On: 18, Oct 2024

Author: Maryam Abdullahi K Mashi ,

Ebook Compiler : Zaharaddeen Shomar

Author Group : Anam Dorayi

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 486.46 kb

File Type: txt

Views: 555+

Download: 807+

Last download: less than 1 second ago

Description/Story: Sanadin Boko 1 01
Posted by ANaM Dorayi on 09:25 AM, 10-Sep-15
Under: SANADIN BOKO
Na
Maryam Abdullah K.Mashi
Ina sauraren duk hirar da kowaccen su ke yi, motar ta
kacame da surutu. Wasu na murnar ganin Iyayensu, wasu
kuma suna zancen auren su. Mafi yawa daga ciki kuma
suna fadin makarantun da za su ci gaba, wasu su ce
poly wasu Jami'a, wasu Nursing school.
Sa'adatu da ke kusa da ni ta ce, "Hafsy don Allah kema
ki shigo (A.B.U Zariya) mu hadu mana." Nayi dan
murmushin takaici.
"Samun (A.B.U) fa ba kamar shiga Bakori ba ne, saboda
in ma zan samun bani da wani tabbas akan za a barni."
Ta zaro ido. "Kada kice min kina cikin wadanda za'a
dakile a kai gidan miji?
Na sake ajiyar zuciya.
"Ke dai Sa'a taya ni da addu'a, Allah Yasa ina da rabo,
dan kuwa ina son in ga karshen boko." Jamila ta dube ni,
"Hafsy ko yaushe kina bani mamaki in kina cewa za ki
ga karshen boko. To bari kiji, sai dai boko yaga karshen
ki. Ance miki wannan lokacin yana jira ne?
Na ce, "To Malama, ban saka bakin ki ba, ina ruwanki. Ke
ba kince aure ba?" Jamila ta ce, "Aure kuwa insha Allahu
ba ya hana karatu, zan yi aurena na ci gaba da karatuna.
Sa'a ta ce, "Wahala ai daya za ki zaba, don da kin yi ciki
za ki watsar da batun karatu. Na ce, "Dubu nawa akayi?
Ai ni boko yanzu muka sa dan ba."
Ta ce, "Shikenan, Allah Ya taimaki kowa kan niyyarshi ta
aikhairi". Na ce, "Ga magana da za ki yi kawai, Amin".
Da tafiya tayi tafiya, sai ka ji kowa shiru. Ni kam
fargabar Babana nake yi, nasan inba wani ikon Allah ba,
da wuya naje wata Makarantar.
An sauke *yan zariya, sannan mu *yan Kaduna muka
nausa hanya, motar makaranta da ke Bakori Katsina, ita
ce ta debo mu zuwa gidajenmu, bayan mun yi bankwana
da makarantar wato mun kammala.
Gidanmu ya kaure da sowa, yara na ta murna "Ga Hafsat
ga Hafsat". Innarmu ta fito da gudu ta rungume ni, ina ta
dariya. Almajiran da suka dauko min kaya suka sauke, na
ce, "Innarmu ba su hamsin". Ta kwance habar zani ta
mika musu.
Yaran gida suka taya ni da kaya zuwa cikin daki, matan
gidanmu kowa sai sannu da zuwa suke min ina amsawa.
Inna ta aje min kwano tare da cewa, "Alalar har ta
huce". Ta dire min kofin ruwa na ce, "Har yanzu bata
kare ba ne?" Ta ce, "Ta kare mana, ai tun kwanaki da
Kawunku Bako yazo ya ce min cikin kwanakin nan za ku
kammala, kullum sai na aje alalar sai dai in naga
magariba tayi ne sannan in ba yara.
Nayi dariya tare da cewa, "Innarmu kenan! Ina Yaya
Ummar?" Ta ce, "Tun safe bai dawo ba, kin san nasai
mashin da aka yi mana rabon gadon nan, Kawun ku Bako
na kawo min kudin na ce a sai mishi mashin wannan
yaran, tunda zaman banza yake, aikin gyaran wutar nan
ba ko yaushe ake samu ba. Ina fama da kannan shi ina
fama da shi.
Na ce, "Kinyi dabara Innarmu, in yayi Achabar sai a rufa
asiri". Ta ce "Kwarai kuwa. Ummi ta zo ta zauna kusa da
ni, na ce "Ummi da ba ina ta kiranki kin ki zuwa ba? Inna
ta ce, "Kullum sai ta ce Innarmu ina Auntyna?"
Na rungumota a jikina ina cewa, "Gani na dawo". Ta rufe
fuskarta, ita dole taji kunya.
Cin alalata nake ina jin dadi ga ni ga Innata, ta ce "Kin
zo a daidai bikin su Hajara da Sakina ya kusa". Na rike
baki, "Inna har da Sakina?"
Ta ce, "Eh! Na ce, "Uhm! Ni da so samu ne in ci gaba da
karatuna ma". Innarmu ta ce, "Malam ne matsala, amma
ko Nas din nan da 'ya'yan Kawunki suke yi ai zan so
kiyi." Na ce, "Wane Nurse? Ni fa Jami'a nake so, burina
in zama 'yar Media".
Ta ce, "Me kenan? Na kafa kofin ruwa na daddaka,
sannan na ajiye tare da cewa, " 'yar jarida mana! Sai dai
matsalar kudi ne". Kai lomar alala da nayi baki, ta zo
daidai da sallamar Baba, nan take naji wani daci tamkar
na tauna madaci. Innarmu ta mishi sannu da shigowa,
tare da shimfida mishi tabarma.
Cikin fargaba na soma gaida shi, ga mamakina yau
fuskar shi sake ya amsa, har da ce min "An dawo lafiya?"
Na ce, "Lafiya lau". Innarmu ta ce, "Allah cikin ikonSa
Malam yau dai su Hafsat karatun Sakandire ya
kammala."
Ya ce, "To dama tunda da mai sonta sai ta yi masa
magana ya fito in hada su da Sakina in huta". Inna ta ce,
"Anya kuwa? Ina ga daurewa da zaka sake yi ta tafi
makarantar gaba da..."
Wani kallo da ya mata shi ne ya dakatar da ita. Ya mike
tsaye ransa a bace.
"Na gaji da wasa da hankalina da ku ke yi, ba zan iya
ganin Hafsa gandandan cikin gidan nan ba, duk wanda ya
shigo ba zai bambance ta da matan gida ba, duk wata
tana zubar da jini, ta zama Uwar mata. Wannan karon
zamu yi tsiya da ku yanda bakwa zato. Wai menene cikin
wannan bokon da ku ka nace mawa? Ina ce karatun
gidan duniya ne?"
Inna ta kufulo itama, ta ce, "To dama ka saba ka min
tijara cikin gida gaban kowa akan Hafsa, tun da babu
sisinka kasa ido, kuma karatu ba fashi. Ya ce, "To zan ga
wanda ke auren wani, tsakanin ni da ke". Ya fita.
Na dago ido da hawaye, takaicina ace kullum Iyayena
basa rigima sai a kaina, bari Munnir yazo anjima, zan ce
masa kawai ya turo manyansa ayi magana, ko ina dakin
nasa zanyi karatuna. Ban dai fadi ma Innarmu kudurina
ba.
Na mike ina tattara kwanukan gabana, Inna kuma sai
mita take, na ce "Innarmu ki bar batun haka, kinsan
gidan nan da gulma, yanzu kowa ya baza kunnuwa yana
sauraro". Ta ce, "Suyi ta sauraro din, ina ruwana. Iyaka
dai mace tayi da ni naji mu kwashi 'yan kallo ni da ita".
Na idar da sallar isha'i, ina zaune a gurin ina istigfari,
wani yaron gidanmu yayi sallama, bai jira amsa ba ya ce
"Innarsu Ummi wai ana kiran Hafsa a waje". Ta ce, "To".
Na mike, nasan Munnir ne, don na aika masa da letter
cewa na dawo.
Na bude jakata na ciro turarena forever na fesa, sannan
na sabi gyalena na fita. Tun kafin na karaso na jiyo
kamshin turarensa.
Yana zaune saman motarsa kirar (Toyota camry), baka
wuluk, sanye yake da wando jean baki, rigarsa fara. Cikin
farin ciki na isa gabansa, nayi masa sallama ya dago da
kanshi daga wayar da ke hannunsa yana latsawa.
"Babyna". Sunan da yake kirana kenan. Na ce, Na'am".
Ya diro "Zo muje cikin mota." Na ce, "A'a mu zauna
can". Na nuna mishi dakalin kofar gidanmu.
Ya dan gyara tsaiwa, "Kin ce fa baki son Baba ya dinga
ganina da kananan kaya, kin san dai in muna can zai
ganni dole ko?"
Na dan yi jim ina nazari. Hakika Baba na fada cewa
Munnir ba dan mutunci ba ne, ya gane haka ne tun daga
suturar da yake sakawa.
Amma bana son shiga motarsa saboda ya cika son taba
jikina.. Ya katsemin tunani da cewa.
"Zo muje, na zo da muhimmiyar magana". Na ce masa,
"Nima ina da nawa muhimmin zancen". Baya ya bude ya
shiga, nima na shiga dayan gefen, sai dai ban rufe ba. Ya
ce "Rufo kofar mana". Na ce, "Ka barshi haka ma ya yi.
Ya kunna wutar motar, haske ya bayyana, ni da shi muka
kalli juna cikin ido. Nayi saurin janye nawa idanun, domin
wani abu da na ji yana bin jijiyoyin jikina.
Ya ce, "Ina sonki Hafsy, ban san irin son da nake miki
ba." Ya kama hannuna na kwace, tare da mai da su baya
na ce, "Don Allah Munnir ka daina son taba jikina,
haramunne fa". Ya ce, "Zamu fara ko? Haba Hafsy, ni ne
fa zan aure ki. Ko yaushe ina son in gwada miki so sai ki
yi ta ki, yaya ki ke yi tamkar wacce bata je makaranta
ba? Sai ka ce ba *yar boko ba? Ni fa kullum ina fada miki
ba zan auri mata muje kina min wani kunshe-kunshen jiki
ba.
Na bata rai, ya shafi kumatuna.
"Small beby, dan yi murmushi. Ba kya yin kyau in kin
daure fuska". Shikenan, ban san lokacin da murmushin
ya subuce min ba, matsalar ina mutuwar son Munnir. Ya
ce, "To fada min maganar kafin kiji tawa, don tawa in
kinji saikin bani goron albishir.
Na ce, "To ni dai dama ina son ne in ce maka ya dace
yanzun muyi aure, don wallahi da kyar Baba ya bari na
gama karatun nan. Sam shi ba ruwan shi da da boko, ka
dai sani". Ya ce, "Haba Baby, aure fa ki ka ce? Kin
manta alkawarin da muka yi ni da ke?"
Na ce, "Ban manta ba". Ya ce, "To ki kyale fadan Baba
kawai, ba nine ke biyan komai na karatunki ba? Come on
aje wannan topic din. Na shirya miki gagarumin party ne
saboda murnar gama karatunki, don haka yaushe zamu je
kasuwa musai kayan sawa?
Takaici ya cika ni, don haka ban tanka ba. Ya sake
matsowa in banyi magana ba nasan zai iya cewa zai
rungume ni. Da sauri na ce, "Duk lokacin da ka shirya".
Ya ce, "Gobe yayi? Dan ranar sati ne party din."
Na ce, "Um". Ya ce, "Wai ba ki murna ne angel dina?
Kada ki damu, kwanan nan za ki zana
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download SANADIN BOKO

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album