Join Our WhatsApp Group

SADAUKIN BURHAAN Complete Hausa Novel Document by SADAUKIN BURHAAN


SADAUKIN BURHAAN

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 52885



SADAUKIN BURHAAN

Reading Time: 4 Hours

Added On: 16, Nov 2023

Author: Jameela Jameey ƴar mutan Kankia ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : 08160508316, 07034464517

Book License : Paid

Category: Love Novels

File Size: 292.8 kb

File Type: txt

Views: 503+

Download: 262+

Last download: 2 hours ago

Description/Story: SADAUKI BURHAAN na JAMEEY YAR MUTAN KANKIA

*SADAUKIN BURHAAN*
_(Daukar Fansa_ _Cigaban Izzah ko Mulki )_
A Kingdom Story👑

*NA*
*JAMEELA JAMEEY*
_(Ya'r Mutan Kankia)_

*BISSIMILLAHIR RAHAMIRRAHIM*

_Godiya ta tabba ga Allah(SWT) daya sake aramana lokaci,inda muka sake haduwa a cikin wannan labarin mai_ _dinbin tausayi da ilmantarwa....Allah yahadamu da mafificin_ _alkhairin dake cikin_ _wannan littafi_

```Wannan labarin kirkirarran labari ne kamar yanda na fada maku abaya tun farkon labarin.....```

*Jinjina da tarin godiya ga masoyana naga addu'ar ku marar iyaka* *Allah yasaka maku da alkhairi,Allah yabar kauna ina tareda ku iya* *wuya so na hakika nike maku irin trillions din nan*

Sadaukin Burhaan na kudi ne akan Naira ɗari Ukku (300) domin karin bayani tuntubi wannan number👉🏻 08160508316 Acct detail 0777512438 Access Bank,Jamila Abubakar Bello.

_SHAFIN KYAUTA_

BABI NA ƊAYA

"Allah yaja da ran Sarauniyar Zairana kiranki ya riskeni."ya sadda kansa kasa yana sauraron yaji kiran da uwar gijiyar tashi tayi mashi.
wani irin wulakantaccen kallo ta watsa mashi da sauri Ado ya sake sunkuyar da kanshi kasa yana jin wani irin mummunar faduwar gaba baki daya jikin shi ya hau bari baisan sadda ya sake russanawa ba yafara neman afuwar ta.
shiru ne ya sake gauraye illahirin ɗakin kamar bakowa wajen kowa ya shuga taitayinsa.
cike da gadara gamida ta wata irin masifaffiyar izzah da takeji duk a lokacin,tafara magana cikin tarin miskilanci da nuna karfin ikon mulki....."sai yanzun kaga damar zuwa kirana."? "Allah ya yuci zuciyarki ba da gangan naki zuwa ba Mai Martaba ne ya tsayar da ni kiman aikin rai!"sake sadda kansa yayi kasa yanajin zuciyarsa kamar ta fado kasa."Dallah yiman shiru karka cikani da wadannan munanan maganganun naka masu saka mutun ciwon kai."Tuba nike uwar gijiyata kimin aikin rai."kallan sa ta kumayi a karo na biyu sannan ta cire kai gefe tace."labari ya sameni ance gobe zakuje Kasuwar Gobir siyan bayi ko."?
"Eh ranki shidade."Idan kunje ina so kaduba mani bayi guda biyu masu inganci da aminci ina bukatar mace daya namiji daya."
"Angama ranki shidade Allah yakara maki lafiya."karka kuskura ku kawo mani raggon bawa, muddin hakan takasance kashinka ya bushe idan kunne yaji......"
_Hmmm wani aikin sai gimbiya Zubaina....ko za'a dace da jajirtaccen_ _bawan da take bukata?_

"Allah yataimakeki bazaki sameni da sabama umarnin kiba zan jajirce inga na samu maki bawan da ya dace dake wannan hakkina ne a matsayina na masu kula da bayin wannan masarauta."ya rage naka zaka iya tafiya."Allah yakara girma ki huta lafiya."
Ga baki daya wajen kowa ya kama kanshi banda hidma na abinda sukeyi bakaramin canzawa Zubaina tayi ba sun rasa gane kanta bata ɗagawa kowa kafa cikin ZAIRANA labarin Zubaina ya karade ko ina kowa shakkunta yakeyi....tun gimbiya Amina na kwatantamata harta kyaleta ta saka mata ido saboda Mai martaba bai son ana takurata ya dauki son duniya ya daura mata kasancewar yanzun ita kadai yake yawan gani a cikin ya'yan sa......

_BURHAAN_
zuwa yanzun Masarautar Burhaan ta hargitse ta gama rikicewa ba abinda akeyi a cikin ta sai mulkin zalinci da kaskanci.
mutane cikinta basu da 'yanci ko kadan banda wulakanci ba abinda ake masu.....duk abinda bayin Masarautar zasuyi basuyin dai dai daga bugu sai aikin wahala ba sauki hatta masu mukamamma basuyin wani motsin kirki a cinin Masarautar.
gimbiya Saude ke ba baiwarta aikin gyaran lambu kasancewar bata son kowa na zuwa lambun ta idan ba wanda ta aminta da shi ba. wannan baiwar na cikin aiki tana rage ciyawun dake cikin lambun sai taga wasu irin manyan bakaken layu suna fidda hayaki....bakaramin tsorata tayiba har saida ta buga uban ihu mai razanarwa.
Da sauri gimbiya Saude ta shigo ta iske layun suna ta fidda hayyaki batasan sadda ta cakumi wuyan baiwar ba taita dukan ta kamar zata kasheta.
wani irin kuka ta fashe dashi mai cin rai tanaji tana gani aikinta ya gama lalacewa.....
Badan komai ba saboda ba'asan kowa ya gansu muddin sukai kwana bakwai a binne cikin ƙasa.Sarki Abduljalal zai mutu....
data gaji da dukan baiwar ta jata kasa ta hada ta da Barde,koda ta iske Barde baki daya baya cikin hankalin shi."ka hukunta man ita."batajira cewar shi ta baro mashi ita.
Kuka kawai takeyi ga tsoro da razana ya gama kamata.
Barde na tasowa yahau ta da duka kamar zai kashe ta ihu kawai takeyi cigaba da dukan ta yaci gaba dayi daga haka ya afka mata yai mata fyade saida yaimata kaca kaca sannan ya kyaleta jini ke zuba a kasanta haka yabarta a ya she kamar zata mutu numfashinta na fita sama sama ɗai ɗai kuma baifasa bugun baiwar nan ba ranar haka yaita haike mata cikin kankanin lokaci numfashin ta ya dauke baki daya.
______________
tunda galadima Hamza ya shigo fa'da yaketa kankanci da wukanta mutane gashi ya hana kowa magana saidai ido da suke bin shi dashi.
Sawa yayi a ka kira masa sarkin taska yana zuwa yakai gaisuwa cikin girmamawa dan shirune ya biyo baya sannan Hamza ya bukaci da Sarkin Taska da ya fiddo mashi kudi."akwai abubuwan da yaka mata ace anyima Masarautar nan"sadda kanshi kasa Sarkin Taska yayi yace."Allah yataimakeka kudin dake hannuna ba masu yawa bane."Mikake nufi."? "Allah yataimakeka ka aiko an karba kwanakin baya."wannan shike nuna zaka ha'inci fa'da ko? yau zaka dandana kudar ka kuma ya zama dole ka fiddoma talakawa kudaden su bana tantama kaine ka cinye dukiyar nan."ranka shidade walahi ko anini banci ba kaimin aikin rai."yiman shiru zakayi bayani ne."yanaji yana gani Hamza ya hana shi magana daga."aje a garkame mani shi gidan yari da sannu saina bankado duk wasu azzalumai maha'inta."yasa akai ram dashi akayi gidan yari dashi.
(Idan nine kadan kuka gani da sannu saina mayar da kowa cikinku abin tausayi a cikin Masarautar nan koda dan uwana ne Abdullahi ya zama wajibi kuyi biyayya ko kuna so ko bakya so da Hamza Muhammad kuke magana matsiyata daku!)

_Allah ya kyauta wannan wane kalar zalinci ne anya Masarautar Burhaan akwai Allah a cikin lamuranta_ 🤔

Haka kowa yakama gaban shi harta kai ga yanzun kowa na gudun zuwa fa'da gudun kar Hamza ya wulakanta mutun ko ya janyo wani sharrin yace kai kayi dan yaci mutuncin ka ko Abdullahi shima baicika son zaman fa'da ba saboda ya fahimci ba wanda Hamza bazai iya wulakantawa ba,baki daya Masarautar Burhaan tana kalkashin ikon sa.
************
Yau kimamin kwanan su Sadauki ukku suna tafiya kuma duk a kasa suke janshi idan sun tsaya to abinci zasuci suma sai sunci sun rage su yammashi ko ruwa diga mashi sukeyi a baki ya hade,baki daya yagama galabaita ko bacci aka kwanta shi baida arzikin ko mayafin dazai shimfida haka zai kwanta a kasa kamar marar galihu....basu suka isa Gobir ba sai wajen karfe biyun rana sadda suka isa Sadauki yagama galabaituwa da duka jikin shi duk sahun duka.
suna isa suka samu waje daban suka sa igiya suka daure kafar shi kamar wani rago,tunda aka shigo dashi mutane sukai ta ribibin shi kamar sunga nama kowa so yake ya siye shi bare yanda suka ganshi kyakkyawan gaske dashi cikin kankanin lokaci akafara cinikayyar shi sai fasama masu kai akeyi
Cinikin sai ya koma gasa kowa bajintar sa yake nunawa ta fidda zunturutun kudi tashin farko mile saba'in aka taya Sadauki sukace albarka wani yace tamanin nan ma sukaki harda wanda yace mile dari amma sunce albarka basu taba kawo bawan dayakai darajar mile talatin ba tunda sukaga ana rububin sayen Sadauk sai suka kara daura guri akan shi kowa yaki yarda ya hakura da cinikin shi,suma sunki sallama shi har dare yayi anki karasa cinikin Sadauki aiko cikin kankanin lokaci wajen yayi tamkam da mutane kowa yana son yaga wanene wannan bawan mai farin jini har haka duk wanda yaga Sadauki sai yaji tausayin shi ya kama shi daganin shi ba ainahin bawa bane jikin shi kadai zaka kalla kasan yasaba da hutu,shiko sai binsu yake da ido kamar wani gele abu kamar wasa har wajen ya makare da mutane har ankai mile dari da hamsin amma sunki siyarwa......
kafin kace me sai aka fara sanar da isowar mutanen Zairana tunda Ado yayi ido hudu da Sadauki yaji ya bala'in shiga ranshi da ganin shi zaiyi juriya da yawa shima ya shiga fafatawa a cikin masu gasar cikiniki.....tashin farko mile dari biyu yasa Sadauki duk wanda ke wajen nan saida ya tsaya ya kalli Ado wani irin girman kai ya sake hawan mutanen da suka kawo Sadauki nan suka ce albarka Ado yasaka kallan Sadauki da kyau daga sama har kasa yai masa kallan tsaf."konawa akasai wannan bawan ba'a fadi ba ya hada komai kyawu da kwarjini ga tarin haiba duk ya hada."ya ayyana aransa bai musaba yace yasa shi mile dubu dari ukku da hamsin baki daya wajen nan aka hau ihu dan duk wanda ke wajen yakasa ja da Ado.....
koda suka ga kowa ya gaza sunsan bazasu kara samun sama da cinikin Ado ba, suka amince ya fiddo kudin su ya basu, suka kwance shi nan ya tambayi sunan shi dayake duk sun rude saboda sunga kudi suka ce sunan shi UMAR ba karamin dadi Ado yaji ba kama hannun Sadauki yayi yaje ya sai mashi abinci ya bashi,kamar tsohon mayunwaci haka Sadauki ke hannu baka hannu kwarya har kwarewa yake kai kace wani zai anshe mashi abincun sannan yaba shi ruwa ya sha.....
cikin yan mintoci har Sadauki yayi bacci shidai Ado yarasa dalilin dayasa Sadauki ya shiga cikin zuciyar shi a lokaci daya.
nan suka tashi ya ida siyan bayin su da mace guda daya da ya siyeta a mile saba'in sunanta Hafsat, suka samu waje suka kwanta shi da mutanan shi kowane bawa na kwance waje amma ya shigo da Sadauki cikin daki a shimfida daya suka kwanta kowa saida yai mamaki amma bata magantuwa sunyi tunanin kodan ya siyeshi da tsadane shiyasa yake bashi kulawa.
kowa bacci ya dauke shi tunda sukai asibar fari sukai sallah kowa ya hau dokin shi suko bayi suka daure su a jikin doki da igiya,koda wani babban bawa yazo daure Sadauki hanashi Ado yayi saida kowa yayi mamaki daura shi yayi agaban dokin shi duk da banisa sosai da Zairana a cikin yini daya suna iya isa take saida hassada ta shiga a tsakanin bawannan da Sadauki da haka suka cigaba ta tafiya zuwa MASARAUTAR ZAIRANA.....

Writer of👇🏻
•Nana Jawaheer
•Gimbiya Hakima
•A gidan Haya
•Sanadin Link
•Bayima 'yayane
•Barawo ne paid
•Sanadin Soyayyar minti
•Alqalami S1
•Bakin jinina ya jaman S2
•Qaddarata S3
•Haka Allah yaso S4
•Lokacine S5
•Daukar fansar budurcina paid
•Bani bace paid
•Bansan inda suke ba paid
•Buɗaɗɗiyar Soyayya paid
•Danginmu ne Sila paid
•Izzah ko Mulki
And
Know
•Sadaukin Burhaan paid


_Yar Mutan Kankia ce❣️_

Share saboda Allah🥰

*SADAUKIN BURHAAN*..
_(Daukar Fansa_ _Cigaban Izzah ko Mulki )_
A Kingdom Story👑

*NA*
*JAMEELA JAMEEY*
_(Ya'r Mutan Kankia)_

*BISSIMILLAHIR RAHAMIRRAHIM*

_SHAFIN KYAUTA_

BABI NA BIYU

Sadaukin Burhaan na kudi ne akan Naira ɗari Ukku (300)Acct details 0777512438 Access bank,Jamila Abubakar Bello shedar biya ta wannan layin 08160508316



Sarki Abdulbasit Abdulkarim cikin turakarsa yarasa abinda ke masahi dadi abubuwa sun coshe mashi banda tunanin Burhaan ba abinda yakeyi yaji shiru daga bangaren su ba amo ba labari tunda akayi bikin su Asma'u....ba Mardiyyah bare yasa ran ganin ko Sadauki ne yazo kullun dasu yake kwana a cikin ransa yarasa me ke mashi dadi a rayuwar shi ta duniya hakan yasa Jakadiyarsa tayi masa kiran gimbiya Zainab bata jima ba ta iso ta zauna kallo daya tayima mijinta ta gane tsatsar damuwar da yake ciki,cikeda kulawa ta soma tam bayarsa abinda ke damunsa cikin tsatsar kulawa bai bata lokaci ba yaima iyalin nasa bayanin komai... itama cikin damuwar take jin shirun yai yawa."yakamata kaje da kanka kaji ko lafiya."tayi maganar a matukar raunane ɗan shiru yayi alamun mai nazari yace." ya dace nafara tura ɗan aike daga bisani zanje da kaina gaskia ina cikin damuwa marar misaltuwa."Allah yasa muji alkhairi."amin."
Abangaren Umm Aisha itama lamarin duniya duk ya tarar mata yaimata yawa ta rasa abinda ke mata dadi idan tayi magana sai mijinta yace ta cika san ya'ya bata da kara Mardiyyah tafita kawaici da sanin yaka mata tanaji tana gani saidai tasa ido amma kullun tana cikin damuwa da zulumi gashi ya hanata zuwa Burhaan yace saidai idan Asma'u ta haihu sannan zataje baki daya.
*******************
Basu suka isa Zairana ba sai wajen karfe biyar na yamma ba inda suka wuce sai sansanin bayi wani katon wajene Sarkin gida ya damka ma bayin da kanshi ya basu masauki amma ya ware Sadauki da Hafsat ba inda ya wuce dasu sai wajen Zubaina kasan cewar tana cikin daki nan ya tsaya dasu babban ɗaki.
Fadila tayibmashi iso zuwa wajen gimbiya Zubaina bayan kakar minti sha biyar ta fito cikin shigar alfarma bakaramin kyau tayi ba,a tsugun ne ta iske su,sai aikin kallon ɗakin Sadauki keyi,wajen ya kayatar dashi ainun.
kowa saida ya kawo gaisuwa wajen gimbiya Zubaina amma banda Sadauki daketa faman karewa dakin kallo.
Baki daya hankalin ta kacokam na kansa ta shagala da kallon irin kyau da tsarin hallittar da Allah yaima Sadauki...rabon da taga kyawu irin nashi bazata iya tunawa ba tajima bata ga kwakkyawan mutun kamar Sadauki ba,tafi karfin minti biyar tana aikin kallan sa har saida hadiman dake wajen suka gane kallar kallan begen da uwar gijiyar tasu take masa."tubarakallahu ahasanil kaliƙin lallai Allah ya gaza halittarsa yanda yaso."ta furta a zahiri tanaci gaba da baya kyawunsa a ranta hatta Ado saida ya kalli Zubaina saboda yasan halinta ba komai ne ke birge taba amma sai gashi tayi santin kyawun Umar....
koda yake dole a yab kalar hallittar shi saboda mutum ne cikakken mutun mai tarin cikar haiba da kyawun sura saida Ado yakara magana a karo na ukku sannan Zubaina ta dawo hayyacin ta.....
Kallansa tayi na sheke ta kauda kai ta basar dayake Sarauta jinintace take ta wayance ta fara masifa."Ado wannan wane irin sakaran bawane ka kawo mani."ranki shidade bawan nan yana da nagarta."shine bazai iya kawo gaisuwa a wajen uwar ɗakinsa ba bayan kowa ya kawo tashi gaisuwar uban wa yafi."?a gadarance tayi maganar tana kada kafa daya saman daya saidai har yanzun tana satar jallan Sadauki ta gefen ido kallan da ba kowa zai gane tanayi masa shi ba. tarin fargaba ya rufe Ado yafara ma Sadauki faɗa."bazaka gaishe da uwar gijiyar ka ba."dan kalan Ado yayi ya kauda kamsa batareda ya kalli inda gimbiya Zubaina taje ba ya gaisheta da muryar amo wadda ke karade zukatan maza du da yana cikin ganiyar sihiri hakan bai hana muryar Sadauki fitaba kamar ta da ba wanda dole sai mai sauraron...


Read / Download SADAUKIN BURHAAN

START READING

OR

DOWNLOAD TXT NOW
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album