Join Our WhatsApp Group

MASHAHURI Complete Hausa Novel Document by MASHAHURI


MASHAHURI

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 39901



MASHAHURI

Reading Time: 3 Hours

Added On: 21, Dec 2023

Author: Binta Umar Abbale ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : 08089965176, 07084653262

Book License : Free

Category: Romance 18+ Novels

File Size: 219.7 kb

File Type: txt

Views: 1744+

Download: 878+

Last download: 3 days ago

Description/Story: [12/13, 6:15 PM] .: *MASHAHURI!*




_BISIMILLAHIR-RAHAMANIR-RAHIM_


*ARASHI*

Wannan littafin 'kirkiraran ne banyi don wani ko wata ba Wanda yaga yayi dai-dai da yanayin rayuwar shi to a rashin sani ne


*GARGADI*

Ban yarda wani ko wata ya yi amfani da wani 'bangare na jikin littafin nan nawa ba tare da izini ba a kiyaye!



*LITTAFIN NAN NA KUDI NE DUK ME BU'KATAR KARANTAWA SAI YA BIYA KUDIN KARATU #300 KACAL TA WANNAN ACCOUNT D'IN 0542382124 BINTA UMAR Gt bank.......KO KUMA KA NEMI NI TA WANNAN NUMBARS 08089965176_07084653262 INSHA ALLAH ZAN FAD'A MAKA YANDA ZAKA BIYA KUDIN KARATU, A KO DA YAUSHE INA MARABA DAKU MASOYA NA MASU SON RUBUTU NA NI CE DAI BINTA UMAR ABBALE😊*




*FREE PEGE*


*1*





Nutsastiyar yarinya ce take tafiya gefan titi tana sanye da kayan makaranta Wanda kana ganin su kasan na isilamiya ne yadin toyobo blue black Riga doguwa da dogon hijab har 'kasa kafarta cikin safa fara da takalmi plate baka ganin komai a jikinta sai 'kwayar idonta cikin nutsuwa take bin gefan titi domin isa gidan su dake cikin unguwar Shagari Qutears tafiya take a tsarge! Domin tasan kallon da jama'ar gari suke wa masu irin shigar su mussaman matasan unguwar su in suka zo shigewa har ihu! Suke musu suna fad'in"Allah a baki fir'auna a zuci! Sam basa tanka musu sanin da suka yi cewar yin hakan zubewar mutumci ne, to shiyasa take tafiya tana hard'ewa kasancewar a bokiyar tafiyar ta bata zo ba, anyi musu mutuwa a cikin gari sun tafi gaisuwa ita da 'yan gidan su. Aikuwa tana shigowa cikin layin su matansa da suke zaman kashe wando suka fara yi mata d'an kira! "Hi ke 'yar gidan Arrama Sarkin 'kauli Allah yace Annabi yace hahahahaha."! Suka 'karashe maganar tasu suna dariya cike da sha'kiyan ci.


Hanifa taji zuciyar ta na yi mata wani irin suya ta rasa me mahaifinta yayi wa jama'ar unguwar su suka d'auki karan tsana suka d'ora masa yaran su da manyan su, ko Dan ya kasance mutum mai tsoron Allah mai hana aikata 'barna kullum yana tunasar dasu abunda Allah da Annabi suka umarci bawa yayi, shine dalilin da yasa suka tsane shi, ita kad'ai take wannan zancan cikin zuciyar ta har ta isa gida.

Tun daga soron gidan nasu take jin saurin muryar mahaifin nata yana karatun al'kurani mai girma cikin 'kira'a mai da d'in saurare.


Cikin nutsuwa ta tu'be takalman ta a gefe guda ta zare safunan 'kafarta a hankali ta shige shi, cikin rumfar su ta shiga inda ta tadda mahaifiyar ta wacce suke kira da Ammi tana zaune kan kafet din dake shimfede a rumfar da farantin wake a cinyar ta tana gyarawa, cikin nutsuwa tace" Ammi sannu da gida."


A nutse mahaifiyar ta ta tace"Yawwa Hanifa kin dawo." Tana 'kokarin cire ni'kaf din fuskarta tace"Eh Ammi yau ni kad'ai naje makaranta na dawo gida ni kad'ai.! Cikin shagwab'a ta fad'i maganar.


A hankali Ammi tace"Mu bari Abbu ya kammala karatun alk'urani sai muyi maganar." Hanifa ta d'an zumb'ura 'karamin bakinta cikin shagwa'ba ta mi'ke d'akin dake cikin rumfar ta shige domin cire uniporm d'in jikin ta.






*MASHAHURI!!*
[12/13, 6:15 PM] .: *MASHAHURI!*




*Ga masu ba'katar cigaba da karanta wannan book d'in zasu biya kud'in karatu #300 kacal ta wannan account d'in.....0542382124 BINTA UMAR GT bank...... Ko kuma Ku same ni ta wannan numbars 08089965176_07084653262 Insha Allah sai in fad'a muku yanda za'ayi Ku biya*


*FREE PEGE*



*2*


Abbu sai da ya had'a izifi biyar sannan ya rufe al'kurani kana yayi addu'a kamar yanda ya saba ya mik'e a nutse yaje ya d'auki buta dake cike da ruwa a tsaya jikin window yana duba a suwakin sa. Alwala yake so ya d'aura ganin lokacin sallahr magriba ya gabato saura bai fi minti goma ba a yi kiran sallah.

Jin motsinsa jikin window d'in yasa Ammi mi'kewa da sauri ta futo tsagar gidan hannunta ri'ke da da a suwakin nasa tasan shi yake lalube jikin window din tace" Abbu ga asuwakin naka na d'auke maka d'azu Dana ga 'kwarika suna yawo a gurin."


"Masha Allah Halimatu Allah yayi miki albarka ina mutukar alfahari da kasancewar ki mata a gare ni ha'kika kina d'aya daga cikin matayen da manzon Allah (Slw) ya fad'a saboda duk suffofin ki sun nuna ke d'in mace ta gari ce."
Abbu ya fad'i maganar bayan ta 'karbi a suwakin hannunta fuskar sa cike da annuri.


A ko da yaushe kalmomin yabo da godiya ne suke futowa daga bakin mijinta zuwa gare ta. Baka ta ta'ba zama da Abbu na minti biyar bai fad'a maka Allah da annbi sunyi hani da aikata fajirci ba, tunda suka yi aure dashi basu ta'ba samun sa'bani ba a tsakanin su a ko da yaushe suna zaman lafiya da juna har Allah yasa suka haifi yara biyu kacal namiji d'aya mace d'aya Nasir shine babba sai Hanifa tsakaninsu akwai tazara sosai shekaru goma sha biyu ne a tsakinsu A halin yanzu Hafiz yana da shekaru ashirin da bakwai a duniya ita Hanifa Yanzu shekarun ta goma sha bakwai a duniya kuma har yanzu Ammi bata 'kara haihuwa ba ko b'atan wata bata 'kara yi ba tun bayan haihuwar Hanifa haka suke yin rayuwar su cikin ilimin addini da sanin ya kamata.


Kamar yanda ya saba bayan idar da sallahr isha'i yana zama 'kofar gidan shi yaja carbi kuma yana kallon yanayin yanda matasan unguwar suke yin rayuwar su, mutukar yaga abunda bai yi masa ba ko yaga ana 'kokarin a sa'bi Allah to babu shakka sai yayi magana akai, ta inda su kuma zasu fara yi masa dariya kamar yanda suka saba suna nuna shi da hannu cikin sha'kiyan ci. To yauma hakace ta kasance yana zaune kam daddumar shi wasu matasa uku suka 'karaso gurin da yake ko wanne da littafi na addini a hannunsa, kamar gaske suka mik'a masa hannu shima ya mi'ka masa nashi suka yi musabaha kamar yanda addini ya tada na, Abbu ya nuna musu gurin zama da hannunshi yana fadin "Masha Allah bisimillah Ku zauna mana." Zama suka yi kamar yanda ya umarce su, suna sinne kai domin sun San da sha'kiyan cin da suka zo gurin sa. Shi kuwa Abbu tufafin jikinsu yake kallo gami da yanda suka tara uban gashi a tsakiyar Kansu yayi wani irin tozo biyu daga cikin su ma har da d'an kunne a kunne su abun ya bashi mamaki sosai

Cikin nazarin su Abbu yace." Alhamdullahi ala kulli halin! Samari me yake tafe daku? Da alama kun zo d'aukar darasi ne."? D'aya daga cikin su yace." 'Kwarai kuwa Arrama munzo mu samu ilimin jima'i a gurun ka Wanda a hausance kuke kira da saduwa turawa kuma suke kiran abun da sexcual."


Abbu yaji wani irin nauyi da kunyar maganar ta rufe shi ko da wasa bai tsammaci wannan maganar ba daga gare su. Sunkuyar da kansa yayi yana nazari.


Wanda yayi maganar yace." Arrama! Munzo a shirye gamu da littafan mu muna 'bukatar d'aukar darussa kan harkar."

Abbu ya d'ago kansa a nutse Yana so yaga fuskar yaron da yake masa wannan maganar me tsauri. Kasancewar gurin babu wadattacan haske yasa bai ga fuskarsa sosai ba, sai ya d'auki wayar shi dake aje gefe ya kunna torchlight d'in Yana haska su. Take ya gane yaron.... Bazai tab'a mance abunda ya faru tsakanin sa da yaron ba shekaru hud'u da suka wuce fuskar yaron baza ta ta'ba 'bace masa ba.


Gyaran murya yayi yace." Masha Allah na ainihin wato idan na fahimci abunda kuke nufi kuna so ki samu ilimi da zaku zauna da iyalan Ku lafiya shine abunda kuke nufi ko."?



Shi d'in ne dai ya 'kara magana a karo na uku yace." 'Kwarai kuwa Arrama muna so ka fed'e mana biri har bindinsa domin mun samu labari a gurin jama'ar gari cewa kana bada darasi iri-iri."


Abbu maganar tayi masa tsauri! Mutu'ka wato sharrin mutanan gari har ta kai sun fara yawo dashi a gari yana koyar da ilimin jima'i babu shi a tunanin sa suna so su 'bata masa suna ne tunda har ta kai tsagerun yara sun fara zuwa gabanshi suna yi masa maganar banza. Daurewa zuciyar sa yayi yace." Cikin ku waye zaiyi aure da har kuke so Ku San ilimin jima'i."


Shi d'in ne dai ya 'kara magana kamar d'azu a tsaye yace." Sanin waye zai yi aure a cikin mu bai dame ka ba Arrama mu dai kawai munzo nan domin ka warware mana komai akan harkar mu biya kud'in ka Ya shaik."! Ya k'arashe maganar sa cike da sha'kiyan ci

Abbu ya d'ago kansa a nutse yana kallonsa, shi d'in ma kallonsa yake da tsayyayun idanunsa na mashahuran 'yan duniya tsayayyun 'yayan gata Wanda suka samu d'aurin gindi a gurin iyayen su.








*MASHAHURI!*
[12/14, 9:40 PM] .: *MASHAHURI!*




*Ga masu ba'katar cigaba da karanta wannan book d'in zasu biya kud'in karatu #300 kacal ta wannan account d'in.....0542382124 BINTA UMAR GT bank...... Ko kuma Ku same ni ta wannan numbars 08089965176_07084653262 Insha Allah sai in fad'a muku yanda za'ayi Ku biya*






*FREE PEGE*


*3*



A nutse Abbu yace." Duk wanda yace muku ina koyar da ilimin jima'i to babu shakka yayi min 'karya alal ha'kika shi jima'i wani abu ne da Allah ya halasta shi a tsakanin mace da namiji anan gurin ina so in fahimtar dake cewar ina nufin miji da mata wanda aka d'aura musu aure da juna a gaban shaidu sannan shi namijin ya biya sadaki kamar yanda addini ya tana da, to babu shakka wannan mata ta zama mallakin sa ta bar hannun iyayen ta ta dawo nasa shike da iko da ita kuma a ko ina ne zai biyawa kansa 'bukata ta aure kamar yanda musulunci ya nuna mana, bayan wannan 'kofa da aka halasta mana ba a yadda mu bi wata kafar dake jikin matayen mu mu biya kan mu bu'kata ba, mutukar muka sa'bi Allah muka bi son zuciyar mu to babu shakka zamu shiga fushin ubangijin mu damu da zuri'ar mu, Wannan shine kawai abunda zan fad'a muku game da maganar da kuka zo min da ita."
Abbu ya 'karashe maganar tashi cikin nutsuwa da kamala.

Khalid ya zakud'a kafad'ar sa yana Sosa kansa cikin sha'kiyan ci yace." Ya sheik wannan tambihin naka bai samu guri ba domin kayi mana k'wange a cikinsa ka'ki ga fayyace mana karatu yanda ya kamata ta'be bakinsa yayi cikin izgili ya zura hannu cikin wandon jins din da yake jikin shi ya zaro kud'i dami ya zube gaban Abbu ya mi'ke tare da fad'in "Guys ku tashi muje ko."


Abbu ya bisu da kallo cikin mamaki! Ya mai da ganinsa kan kud'in da suke gaban shi, kamar Wanda Khalid din yayi masa d'aurin baki sam ya kasa yi musu magana suzo su d'auki kud'in su, babu abunda zaiyi da kud'in da suke bashi domin kwata-kwata bai yarda da tarbiyar yaran ba mussaman shi mai maganar cikin su. Ya san shi farin sani yaron da yayi masa abunda bazai ta'ba mantawa dashi ba.

Yana zaune a gurin yana tunanin yanda rayuwa ta duniya ta lalace da yanda 'yayan da aka haife su cikin musulunci gaba da baya amma suna kokarin mai da Kansu kafurai shi a ganinsa duk mutumin da ya bujerewa fad'ar Allah da manzon sa ta ya kafurta Kuma yazo duniya a banza zai koma a hofi shiyasa yake tsaye akan iyalinsa da su bi sinnar Annabi Muhammad (slw) yasan dai shiriya ta Allah ce duk tsantsenin sa da takatsantsan d'insa shima bai wuce Allah ya jarrabe shi ba, ala kullu halin dai yana addu'ar Allah ya tsallakar dashi da iyalinsa ga fad'awa ga halaka



Sai bayan ya gama sauraran tambihi daga malam Umar Sani fagge a tashar express redio sannan ya nad'e daddumar shi ya shiga gida, a lokacin suka matasan layin suka saki kid'a na wa'kokin Hausa iri-iri sai ihu! Suke yi kamar ba dare ba.


Abbu ya gyada kansa yana musu addu'a shiriya cikin zuciyar sa 'kofar gidan ya kulle yayi addu'a kana ya shiga cikin gidan yana haska torchlight din hannun sa.

Shiru Ammi da Hanifa sun yi bacci ya bude dakin shi ya shiga cikin nutsuwa yake yin komai Abbu kenan kamilin mutum mai ri'ko da addini da bin sinnar Annabi muhammadu (Slw)

*****

'Karfe bakwai na Safiya Hanifa ta gama shirin ta tana makaranta boko dake tana ajin 'karshe na kammala secondary school a nutse ta zauna kusa da mahaifiyar ta tana turo baki kamar yanda ta saba cikin shagwaba tace"Ammi ina kwana."


Ammi dake had'a mata abun karyawa tace"Lafiya lau Hanifa kin tashi lafiya."? Tace"Lafiya lau na tashi Ammi sai dai ke wayar Yayana." Ammi tayi murmushi tace"Yau zaki ganshi ya dawo ai yau juma'a." Cike da farin ciki Hanifa tace" Aikuwa wallahi na manta Allah ya dawo dashi lafiya." Ammi tace"Amin.


Bayan ta gama karyawa ta mi'ke da niyyar tafiya tana gyara ni'kaf din fuskarta tace"Ammi Abbu kuwa ya kammala azakar din da yake bamu gaisa ba kuma idan na tsaya zan makara." Ammi tace"Ai kuwa sai dai ki shige ki tafi domin Abbu bazai futo ba sai kusan sha biyu na rana lokacin zai shirya domin zuwa masallaci."


Hanifa tayi wa Ammi sallama ta futa tana gyara jakarta da take rataye a kafad'ar ta.


Gidan su Asalamiyya na gaba dasu kad'an Hanifa bata ta'ba tafiya ita kad'ai ba tare da ta biya mata ba Asalamiyya 'kawar Hanifa ce tun ta 'kuruciya halinsu yazo d'aya haka ma d'abiun su yazo d'aya bayan nan kuma Abbu ya yarda da tarbiyyar ta sannan mahaifin Asalamiyyar Abokin sa ne d'abi'un su sun zo d'aya shine yasa har ya aminta da 'kanwancen su Abbu yana sanya ido kan irin 'kawayen Hanifa sosai shiyasa itama take taka tsan_tsan bata fiye sakewa da jama'a ba

Tun daga nesa ta hango cincirin don matasan samarin da suke ji da kansu a unguwar sun ke waye shi kamar ko da yaushe shi kuma yana tsakiyar su hannunsa ri'ke da 'katuwar some times tana ganin shi a unguwar amma bata san sunan shi ba ita dai haka kurrum yake burgeta duk ganin da zata yi masa da ni'kaf a fuskarta hakan baya hanata ta 'kare masa kallo sosai guy yake burgeta da irin dressing d'inshi kuma ta lura duk masu yi masa fadanci suna kwaikwayar sa ne da irin dressing din shi, gabanta ya cigaba da fad'uwa har ta iso kusa dasu, kanta a 'kasa tazo shiga cikin gidan su Asalamiyya taji Muryar d'aya daga cikinsu yana fad'in"Wannan munafukar yarinyar watarana sai mun yage ta Wallahi kullum jiki a rufe shegiya ko don tasan tana da kyau ne yasa take rufe jikinta oho."! Dariya suka saka...


Read / Download MASHAHURI

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

1 Comments On MASHAHURI
avatar
oumara-wassai

4 months ago

Reply

39901

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album