Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[12/13, 6:15 PM] .: *MASHAHURI!*




_BISIMILLAHIR-RAHAMANIR-RAHIM_


*ARASHI*

Wannan littafin 'kirkiraran ne banyi don wani ko wata ba Wanda yaga yayi dai-dai da yanayin rayuwar shi to a rashin sani ne


*GARGADI*

Ban yarda wani ko wata ya yi amfani da wani 'bangare na jikin littafin nan nawa ba tare da izini ba a kiyaye!



*LITTAFIN NAN NA KUDI NE DUK ME BU'KATAR KARANTAWA SAI YA BIYA KUDIN KARATU #300 KACAL TA WANNAN ACCOUNT D'IN 0542382124 BINTA UMAR Gt bank.......KO KUMA KA NEMI NI TA WANNAN NUMBARS 08089965176_07084653262 INSHA ALLAH ZAN FAD'A MAKA YANDA ZAKA BIYA KUDIN KARATU, A KO DA YAUSHE INA MARABA DAKU MASOYA NA MASU SON RUBUTU NA NI CE DAI BINTA UMAR ABBALE😊*




*FREE PEGE*


*1*





Nutsastiyar yarinya ce take tafiya gefan titi tana sanye da kayan makaranta Wanda kana ganin su kasan na isilamiya ne yadin toyobo blue black Riga doguwa da dogon hijab har 'kasa kafarta cikin safa fara da takalmi plate baka ganin komai a jikinta sai 'kwayar idonta cikin nutsuwa take bin gefan titi domin isa gidan su dake cikin unguwar Shagari Qutears tafiya take a tsarge! Domin tasan kallon da jama'ar gari suke wa masu irin shigar su mussaman matasan unguwar su in suka zo shigewa har ihu! Suke musu suna fad'in"Allah a baki fir'auna a zuci! Sam basa tanka musu sanin da suka yi cewar yin hakan zubewar mutumci ne, to shiyasa take tafiya tana hard'ewa kasancewar a bokiyar tafiyar ta bata zo ba, anyi musu mutuwa a cikin gari sun tafi gaisuwa ita da 'yan gidan su. Aikuwa tana shigowa cikin layin su matansa da suke zaman kashe wando suka fara yi mata d'an kira! "Hi ke 'yar gidan Arrama Sarkin 'kauli Allah yace Annabi yace hahahahaha."! Suka 'karashe maganar tasu suna dariya cike da sha'kiyan ci.


Hanifa taji zuciyar ta na yi mata wani irin suya ta rasa me mahaifinta yayi wa jama'ar unguwar su suka d'auki karan tsana suka d'ora masa yaran su da manyan su, ko Dan ya kasance mutum mai tsoron Allah mai hana aikata 'barna kullum yana tunasar dasu abunda Allah da Annabi suka umarci bawa yayi, shine dalilin da yasa suka tsane shi, ita kad'ai take wannan zancan cikin zuciyar ta har ta isa gida.

Tun daga soron gidan nasu take jin saurin muryar mahaifin nata yana karatun al'kurani mai girma cikin 'kira'a mai da d'in saurare.


Cikin nutsuwa ta tu'be takalman ta a gefe guda ta zare safunan 'kafarta a hankali ta shige shi, cikin rumfar su ta shiga inda ta tadda mahaifiyar ta wacce suke kira da Ammi tana zaune kan kafet din dake shimfede a rumfar da farantin wake a cinyar ta tana gyarawa, cikin nutsuwa tace" Ammi sannu da gida."


A nutse mahaifiyar ta ta tace"Yawwa Hanifa kin dawo." Tana 'kokarin cire ni'kaf din fuskarta tace"Eh Ammi yau ni kad'ai naje makaranta na dawo gida ni kad'ai.! Cikin shagwab'a ta fad'i maganar.


A hankali Ammi tace"Mu bari Abbu ya kammala karatun alk'urani sai muyi maganar." Hanifa ta d'an zumb'ura 'karamin bakinta cikin shagwa'ba ta mi'ke d'akin dake cikin rumfar ta shige domin cire uniporm d'in jikin ta.






*MASHAHURI!!*
[12/13, 6:15 PM] .: *MASHAHURI!*




*Ga masu ba'katar cigaba da karanta wannan book d'in zasu biya kud'in karatu #300 kacal ta wannan account d'in.....0542382124 BINTA UMAR GT bank...... Ko kuma Ku same ni ta wannan numbars 08089965176_07084653262 Insha Allah sai in fad'a muku yanda za'ayi Ku biya*


*FREE PEGE*



*2*


Abbu sai da ya had'a izifi biyar sannan ya rufe al'kurani kana yayi addu'a kamar yanda ya saba ya mik'e a nutse yaje ya d'auki buta dake cike da ruwa a tsaya jikin window yana duba a suwakin sa. Alwala yake so ya d'aura ganin lokacin sallahr magriba ya gabato saura bai fi minti goma ba a yi kiran sallah.

Jin motsinsa jikin window d'in yasa Ammi mi'kewa da sauri ta futo tsagar gidan hannunta ri'ke da da a suwakin nasa tasan shi yake lalube jikin window din tace" Abbu ga asuwakin naka na d'auke maka d'azu Dana ga 'kwarika suna yawo a gurin."


"Masha Allah Halimatu Allah yayi miki albarka ina mutukar alfahari da kasancewar ki mata a gare ni ha'kika kina d'aya daga cikin matayen da manzon Allah (Slw) ya fad'a saboda duk suffofin ki sun nuna ke d'in mace ta gari ce."
Abbu ya fad'i maganar bayan ta 'karbi a suwakin hannunta fuskar sa cike da annuri.


A ko da yaushe kalmomin yabo da godiya ne suke futowa daga bakin mijinta zuwa gare ta. Baka ta ta'ba zama da Abbu na minti biyar bai fad'a maka Allah da annbi sunyi hani da aikata fajirci ba, tunda suka yi aure dashi basu ta'ba samun sa'bani ba a tsakanin su a ko da yaushe suna zaman lafiya da juna har Allah yasa suka haifi yara biyu kacal namiji d'aya mace d'aya Nasir shine babba sai Hanifa tsakaninsu akwai tazara sosai shekaru goma sha biyu ne a tsakinsu A halin yanzu Hafiz yana da shekaru ashirin da bakwai a duniya ita Hanifa Yanzu shekarun ta goma sha bakwai a duniya kuma har yanzu Ammi bata 'kara haihuwa ba ko b'atan wata bata 'kara yi ba tun bayan haihuwar Hanifa haka suke yin rayuwar su cikin ilimin addini da sanin ya kamata.


Kamar yanda ya saba bayan idar da sallahr isha'i yana zama 'kofar gidan shi yaja carbi kuma yana kallon yanayin yanda matasan unguwar suke yin rayuwar su, mutukar yaga abunda bai yi masa ba ko yaga ana 'kokarin a sa'bi Allah to babu shakka sai yayi magana akai, ta inda su kuma zasu fara yi masa dariya kamar yanda suka saba suna nuna shi da hannu cikin sha'kiyan ci. To yauma hakace ta kasance yana zaune kam daddumar shi wasu matasa uku suka 'karaso gurin da yake ko wanne da littafi na addini a hannunsa, kamar gaske suka mik'a masa hannu shima ya mi'ka masa nashi suka yi musabaha kamar yanda addini ya tada na, Abbu ya nuna musu gurin zama da hannunshi yana fadin "Masha Allah bisimillah Ku zauna mana." Zama suka yi kamar yanda ya umarce su, suna sinne kai domin sun San da sha'kiyan cin da suka zo gurin sa. Shi kuwa Abbu tufafin jikinsu yake kallo gami da yanda suka tara uban gashi a tsakiyar Kansu yayi wani irin tozo biyu daga cikin su ma har da d'an kunne a kunne su abun ya bashi mamaki sosai

Cikin nazarin su Abbu yace." Alhamdullahi ala kulli halin! Samari me yake tafe daku? Da alama kun zo d'aukar darasi ne."? D'aya daga cikin su yace." 'Kwarai kuwa Arrama munzo mu samu ilimin jima'i a gurun ka Wanda a hausance kuke kira da saduwa turawa kuma suke kiran abun da sexcual."


Abbu yaji wani irin nauyi da kunyar maganar ta rufe shi ko da wasa bai tsammaci wannan maganar ba daga gare su. Sunkuyar da kansa yayi yana nazari.


Wanda yayi maganar yace." Arrama! Munzo a shirye gamu da littafan mu muna 'bukatar d'aukar darussa kan harkar."

Abbu ya d'ago kansa a nutse Yana so yaga fuskar yaron da yake masa wannan maganar me tsauri. Kasancewar gurin babu wadattacan haske yasa bai ga fuskarsa sosai ba, sai ya d'auki wayar shi dake aje gefe ya kunna torchlight d'in Yana haska su. Take ya gane yaron.... Bazai tab'a mance abunda ya faru tsakanin sa da yaron ba shekaru hud'u da suka wuce fuskar yaron baza ta ta'ba 'bace masa ba.


Gyaran murya yayi yace." Masha Allah na ainihin wato idan na fahimci abunda kuke nufi kuna so ki samu ilimi da zaku zauna da iyalan Ku lafiya shine abunda kuke nufi ko."?



Shi d'in ne dai ya 'kara magana a karo na uku yace." 'Kwarai kuwa Arrama muna so ka fed'e mana biri har bindinsa domin mun samu labari a gurin jama'ar gari cewa kana bada darasi iri-iri."


Abbu maganar tayi masa tsauri! Mutu'ka wato sharrin mutanan gari har ta kai sun fara yawo dashi a gari yana koyar da ilimin jima'i babu shi a tunanin sa suna so su 'bata masa suna ne tunda har ta kai tsagerun yara sun fara zuwa gabanshi suna yi masa maganar banza. Daurewa zuciyar sa yayi yace." Cikin ku waye zaiyi aure da har kuke so Ku San ilimin jima'i."


Shi d'in ne dai ya 'kara magana kamar d'azu a tsaye yace." Sanin waye zai yi aure a cikin mu bai dame ka ba Arrama mu dai kawai munzo nan domin ka warware mana komai akan harkar mu biya kud'in ka Ya shaik."! Ya k'arashe maganar sa cike da sha'kiyan ci

Abbu ya d'ago kansa a nutse yana kallonsa, shi d'in ma kallonsa yake da tsayyayun idanunsa na mashahuran 'yan duniya tsayayyun 'yayan gata Wanda suka samu d'aurin gindi a gurin iyayen su.








*MASHAHURI!*
[12/14, 9:40 PM] .: *MASHAHURI!*




*Ga masu ba'katar cigaba da karanta wannan book d'in zasu biya kud'in karatu #300 kacal ta wannan account d'in.....0542382124 BINTA UMAR GT bank...... Ko kuma Ku same ni ta wannan numbars 08089965176_07084653262 Insha Allah sai in fad'a muku yanda za'ayi Ku biya*






*FREE PEGE*


*3*



A nutse Abbu yace." Duk wanda yace muku ina koyar da ilimin jima'i to babu shakka yayi min 'karya alal ha'kika shi jima'i wani abu ne da Allah ya halasta shi a tsakanin mace da namiji anan gurin ina so in fahimtar dake cewar ina nufin miji da mata wanda aka d'aura musu aure da juna a gaban shaidu sannan shi namijin ya biya sadaki kamar yanda addini ya tana da, to babu shakka wannan mata ta zama mallakin sa ta bar hannun iyayen ta ta dawo nasa shike da iko da ita kuma a ko ina ne zai biyawa kansa 'bukata ta aure kamar yanda musulunci ya nuna mana, bayan wannan 'kofa da aka halasta mana ba a yadda mu bi wata kafar dake jikin matayen mu mu biya kan mu bu'kata ba, mutukar muka sa'bi Allah muka bi son zuciyar mu to babu shakka zamu shiga fushin ubangijin mu damu da zuri'ar mu, Wannan shine kawai abunda zan fad'a muku game da maganar da kuka zo min da ita."
Abbu ya 'karashe maganar tashi cikin nutsuwa da kamala.

Khalid ya zakud'a kafad'ar sa yana Sosa kansa cikin sha'kiyan ci yace." Ya sheik wannan tambihin naka bai samu guri ba domin kayi mana k'wange a cikinsa ka'ki ga fayyace mana karatu yanda ya kamata ta'be bakinsa yayi cikin izgili ya zura hannu cikin wandon jins din da yake jikin shi ya zaro kud'i dami ya zube gaban Abbu ya mi'ke tare da fad'in "Guys ku tashi muje ko."


Abbu ya bisu da kallo cikin mamaki! Ya mai da ganinsa kan kud'in da suke gaban shi, kamar Wanda Khalid din yayi masa d'aurin baki sam ya kasa yi musu magana suzo su d'auki kud'in su, babu abunda zaiyi da kud'in da suke bashi domin kwata-kwata bai yarda da tarbiyar yaran ba mussaman shi mai maganar cikin su. Ya san shi farin sani yaron da yayi masa abunda bazai ta'ba mantawa dashi ba.

Yana zaune a gurin yana tunanin yanda rayuwa ta duniya ta lalace da yanda 'yayan da aka haife su cikin musulunci gaba da baya amma suna kokarin mai da Kansu kafurai shi a ganinsa duk mutumin da ya bujerewa fad'ar Allah da manzon sa ta ya kafurta Kuma yazo duniya a banza zai koma a hofi shiyasa yake tsaye akan iyalinsa da su bi sinnar Annabi Muhammad (slw) yasan dai shiriya ta Allah ce duk tsantsenin sa da takatsantsan d'insa shima bai wuce Allah ya jarrabe shi ba, ala kullu halin dai yana addu'ar Allah ya tsallakar dashi da iyalinsa ga fad'awa ga halaka



Sai bayan ya gama sauraran tambihi daga malam Umar Sani fagge a tashar express redio sannan ya nad'e daddumar shi ya shiga gida, a lokacin suka matasan layin suka saki kid'a na wa'kokin Hausa iri-iri sai ihu! Suke yi kamar ba dare ba.


Abbu ya gyada kansa yana musu addu'a shiriya cikin zuciyar sa 'kofar gidan ya kulle yayi addu'a kana ya shiga cikin gidan yana haska torchlight din hannun sa.

Shiru Ammi da Hanifa sun yi bacci ya bude dakin shi ya shiga cikin nutsuwa yake yin komai Abbu kenan kamilin mutum mai ri'ko da addini da bin sinnar Annabi muhammadu (Slw)

*****

'Karfe bakwai na Safiya Hanifa ta gama shirin ta tana makaranta boko dake tana ajin 'karshe na kammala secondary school a nutse ta zauna kusa da mahaifiyar ta tana turo baki kamar yanda ta saba cikin shagwaba tace"Ammi ina kwana."


Ammi dake had'a mata abun karyawa tace"Lafiya lau Hanifa kin tashi lafiya."? Tace"Lafiya lau na tashi Ammi sai dai ke wayar Yayana." Ammi tayi murmushi tace"Yau zaki ganshi ya dawo ai yau juma'a." Cike da farin ciki Hanifa tace" Aikuwa wallahi na manta Allah ya dawo dashi lafiya." Ammi tace"Amin.


Bayan ta gama karyawa ta mi'ke da niyyar tafiya tana gyara ni'kaf din fuskarta tace"Ammi Abbu kuwa ya kammala azakar din da yake bamu gaisa ba kuma idan na tsaya zan makara." Ammi tace"Ai kuwa sai dai ki shige ki tafi domin Abbu bazai futo ba sai kusan sha biyu na rana lokacin zai shirya domin zuwa masallaci."


Hanifa tayi wa Ammi sallama ta futa tana gyara jakarta da take rataye a kafad'ar ta.


Gidan su Asalamiyya na gaba dasu kad'an Hanifa bata ta'ba tafiya ita kad'ai ba tare da ta biya mata ba Asalamiyya 'kawar Hanifa ce tun ta 'kuruciya halinsu yazo d'aya haka ma d'abiun su yazo d'aya bayan nan kuma Abbu ya yarda da tarbiyyar ta sannan mahaifin Asalamiyyar Abokin sa ne d'abi'un su sun zo d'aya shine yasa har ya aminta da 'kanwancen su Abbu yana sanya ido kan irin 'kawayen Hanifa sosai shiyasa itama take taka tsan_tsan bata fiye sakewa da jama'a ba

Tun daga nesa ta hango cincirin don matasan samarin da suke ji da kansu a unguwar sun ke waye shi kamar ko da yaushe shi kuma yana tsakiyar su hannunsa ri'ke da 'katuwar some times tana ganin shi a unguwar amma bata san sunan shi ba ita dai haka kurrum yake burgeta duk ganin da zata yi masa da ni'kaf a fuskarta hakan baya hanata ta 'kare masa kallo sosai guy yake burgeta da irin dressing d'inshi kuma ta lura duk masu yi masa fadanci suna kwaikwayar sa ne da irin dressing din shi, gabanta ya cigaba da fad'uwa har ta iso kusa dasu, kanta a 'kasa tazo shiga cikin gidan su Asalamiyya taji Muryar d'aya daga cikinsu yana fad'in"Wannan munafukar yarinyar watarana sai mun yage ta Wallahi kullum jiki a rufe shegiya ko don tasan tana da kyau ne yasa take rufe jikinta oho."! Dariya suka saka d'ayan yace." Kai 'yar gidan Shaik ce fa."! A slow ya d'ago kanshi yana kallonta lokacin da ke 'kokarin shiga cikin gidan suka ci karo da Ya Abbakar yayan Asalamiyya ne ya futo yana wata irin tafiya irin ta manyan 'kwari yana ganinta ya gane ta ita kuma ta ja da baya da sauri cikin ladabi ta tsuguna har 'kasa ta gaishe shi." Abbakar ya shafa fuskarsa cike da jin dad'i ya amsa mata shi kam ladabin yarinyar yana burge shi babban abunda yake bashi haushi da ita yanda take rufe jikinta sai kace matar Liman. Yace." Hanifa yau ma sai dai ki tafi ke kad'ai don basu dawo ba amma dai mybe yau su dawo."

Jiki a sanyaye Hanifa ta juya tana fad'in to Ya Abbakar." Juyawar da zata yi suka had'a ido dashi, tayi saurin yin 'kasa da kanta a salu'be ta bar gurun. Shi kuma Abbakar ya 'karasa dabar tasu kamar yanda suka saba gaisuwar su yau ma haka suka yi suna dariyar sha'kiyan ci Salis yace." Kai d'an iska naga waccan me ni'kaf din ta gaishe ka har da tsuguna maka kai kuma sai was he baki kake hahahahaha." Ya k'arashe maganar yana dariyar shakiyanci.


Abbakar ya sosa kansa yana kallon hanyar da Hanifa ta wuce yace." Hanny kenan kasan nifa kamar 'kanwata take a gurina tunda 'kawar Asalamiyya ce shiyasa take bani girma."

A hankali ya d'ago kanshi yana kallon Abbakar din cikin yanayin maganar shi kamar ta mata yace." Kome baka girman da take sai mun tu'be ta mun ga abunda yake rufe kusan sau biyar kenan ina ganinta cikin wannan bakin abun sai na yaye ta Wallahi tun da yanzu na gano 'yar babban ma'kiyina ne."






_BintuUm@rAbb@le_



*MASHAHURI!*
[12/15, 10:04 AM] .: *MASHAHURI!*




*Ga masu ba'katar cigaba da karanta wannan book d'in zasu biya kud'in karatu #300 kacal ta wannan account d'in.....0542382124 BINTA UMAR GT bank...... Ko kuma Ku same ni ta wannan numbars 08089965176_07084653262 Insha Allah sai in fad'a muku yanda za'ayi Ku biya*

*Mutanan Nijar kuma idan suna bu'kata suma zasu tura katin waya orange ko Airtal ta wannan numbars 90899076_88137740 dala d'ari itace a madadin 'Dari uku na Najeria, MASHAHURI MAWA'KI ko da 'kud'in ka sai da rabon ka.!!!!!*





*FREE PEGE*



*4*



Abbakar ya kalleshi da jin abunda yake fad'a yasan halin Khalid bashi da kyau a ko wane fanni kuma baya yafiya komai girman mutum idan yayi masa abu sai ya rama gashi yaro ne duk a cikin su amma mugun tsoron sa suke ji Saboda yana da wani irin nasibi da kwarjini na jama'a duk inda ya ratsa sai ya tara mutane ko a makaranta ne haka zasu kewaye shi tun waya na waya ba kowa ne yake da ita ba shi ya mallaketa zai tara su suyi ta kalle kallen wa'kokin Hausa da turanci gami da kallan pictures din turawa masu bayyana tsaraici kai har da ma pictures din hausawa 'yayan musulci duk Khalid na dasu cikin wayar shi na irin 'yan matan da suke sonshi suke turo masa 'bangare-'bangare na jikinsu, shi kuma ya Tara abokan shi yayi ta nuna musu suna dariya in suka ga mai 'kananun nonowa su shek'e da dariya haka ma idan suka ga mai manya manyan nonowa da hifs nan ma kaji su suna dariya had'e da sakin ajiyar zuciya masu rauni kuwa a cikinsu sai kaji suna cewa"Wallahi saura kad'an na kawo haka dai zasu yi ta iskancin su na samarin masu tashan balaga.

Abbakar yace." Kar muyi haka dakai *Mashahuri* sau tari sunan da suke kiran sa dashi kenan ya cigaba da cewa "Jiya na samu labarin abunda kuka je kuka yiwa Shaik don Allah ku k'yale mutumin nan haka kuma babu ruwan Ku da 'yar sa don Allah."


Wani kallo ya watsawa Abbakar d'in cikin yanayin maganar sa a hankali yace." Kana wani tunani daban ina nawa tunanin, ni babu abunda zan yi mata tunda ba ita tayi min ba amma dai duk sanda na kara ganinta da jiki a rufe sai na tu'be naga abunda take 'boye wa ai bata fi sauran 'yan matan unguwa ba."


Su Salis suka sa dariya suna fad'in"Wallahi da kayi mana dai-dai Allah yasa ranar da zaka tu'be ta munanan mu sha kallo shegiya tasan tana da kayan aiki ne shiyasa take yawo cikin hijab, hahahahaha shima Shaik d'in abunda yake dubawa kenan shiyasa ya sa mata ido ai bai isa yayi wa Allah wayo ba." Suka 'karashe maganar tasu suna dariya had'e da tafawa Abbakar dai shiru yayi musu domin yasan sun fi 'karfinsa shima zai so yaga ranar da za'a tu'be Yarinyar yasan a ranar zai sha kallo.


Tunda taje makaranta ta kasa sakewa a aji da ta tuno kamanninsa sai gabanta ya yanke ya fad'i! Ya ilahi kanta ta sunkuyar kan daks tana addu'a cikin zuciyar ta ta rasa me yake damun zuciyar ta da guy, da batasan shi batasan daga inda yake zuwa gurin su Abbakar ba ta tabbata dai abokinsu ne kuma daga ni duk yafi su wadata ko ga yanayin sutturan da yake sawa da irin manya-manyan wayoyin da suke hannunsa tasan yaron d'an masu kudi ne, haka dai tayi ta addu'a kan Allah ya cire mata tunanin shi cikin zuciyarta har lokacin tashi yayi Hanifa bata fahimci komai ba ga kad'acin Asalamiyya ya dame ta suku-suku ta futo daga aji ta d'auki hanyar gidansu tana tafiya a tsarge kamar yanda ta saba.


Jama'a nata futowa daga gidajan su cikin shirin zuwa massalaci domin su sallahr juma'a ya wancin su da sabbin kaya da dadduma wasu da yaran su wasu na tafiya a 'kasa wasu kuwa kan abun hawan su, masu shaguna na rufewa suna tafiya massalaci duk domin samun lada gurin Allah.

A dai-dai wannan Lokacin ne su kuma suka saki kid'a ko cikin shagon Mabson kid'an da ya karad'e unguwar gabaki d'aya tun daga bakin titi mutan yakan iya jin 'kidan Muryar shi ce take tashi cikin sabuwar wa'kar shi mai taken *'Kwalelen ki!* sosai wa'kar tayi Dan banzan dad'i fiye da wa'kar shi ta farko da ya fara, ita wannan jiya ya shiga studio ya sake ta shine fa ya Tara abokan shi suna ji, kafin kace kwabo yaran da suke kokarin tafiya massalaci sun fara taruwa a 'kofar shagon suna le'kawa manyan ma daga cikinsu sun shagala da jin wa'kar azakar d'in da suke yi ma suka daina kawai suna tafiya suna sauraran wak'ar mai taken *Kwalelen ki!* Muryar Khalid akwai dad'i sosai wa'kar taja hankalin 'yan matan da suke cikin gidansu suna le'kowa waje wasu ma babu mayafai a
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On MASHAHURI
avatar
oumara-wassai

5 months ago

Reply

39901

Please Login or Register in order to submit comment